huxubobin jumu’ah - home - wrapa jihohin arewa maso yamma guda bakwai (jigawa, kaduna, kano,...

166
Huxubobin Jumu’ah Game Da Zamantakewar Aure A Shari’ar Musulunci Qungiyar Kare Haqqoqin Mata Da Tabbatar Da yi Musu Adalci Mai Laqabin (WRAPA) Nigeria Ce Ta Samar da wannan Littafi A Qarkashin Shirin Inganta Dokokin Zamantakewar Iyali A Musulunci (IFL) Talifin Goni Muhammad Sa’ad Ngamdu Shirin Tabbatar da Adalci ga Kowa (J4A) Ya Bada Tallafin Buga Waxannan Huxubobi da Aiwatar da Gwajinsu Maris 2016

Upload: tranthuan

Post on 11-Apr-2018

353 views

Category:

Documents


6 download

TRANSCRIPT

Huxubobin Jumu’ah Game Da Zamantakewar Aure A Shari’ar

Musulunci

Qungiyar Kare Haqqoqin Mata Da Tabbatar Da yi Musu Adalci

Mai Laqabin (WRAPA) Nigeria Ce Ta Samar da wannan Littafi

A Qarkashin Shirin Inganta Dokokin Zamantakewar Iyali A Musulunci (IFL)

Talifin

Goni Muhammad Sa’ad Ngamdu

Shirin Tabbatar da Adalci ga Kowa (J4A) Ya Bada Tallafin Buga Waxannan

Huxubobi da Aiwatar da Gwajinsu

Maris 2016

ii

©Women’s Rights Advancement and Protection Alternative (WRAPA)

Nigeria, 2016

All Rights Reserved

No part of this publication may be reproduced or transmitted in any form or by

any means electronic or mechanical, including photocopying, recording or any

information storage and retrieval system, without permission in writing from

the copyright owner.

ISBN: 978-978-54653-4-1

Ahmadu Bello University Press Limited, Zaria,

Kaduna State, Nigeria.

Tel.: 08065949711.

E-mail: [email protected];

[email protected]

Website: www.abupress.org

iii

Qumshiya

Muqaddima...................................................................................

Godiya...........................................................................................

Gabatarwa......................................................................................

Rayuwar Mace Qarqashin Inuwar Musulunci...............................

Aure Da Gina Rayuwar Iyali A Musulunci...................................

Aure Shine Tsarin Da Allah Ya Yarda Da Shi..............................

Waliyan Aure.................................................................................

Waxansu Daga Haqqoqin Miji Da Mata A Musulunci................

Yiwa Wacce Aka Saki Kyautar Jin Daxi Da Xaukar

Nauyin Matar Aure.....................................................................

Reno Da Sharuxan Da Suka Kevanta Da Shi................................

Haqqoqin Mace Akan Waliyyinta.................................................

Ni’imar Da Ke Cikin Aure............................................................

Haqqoqin ‘Ya’ya Akan Iyayensu..................................................

Maza Da Mata...............................................................................

Saki Shine Ke Rushe Gidajen Aure..............................................

Yawaitar Saki Ce Take Lalata Rayuwar Aure..............................

Waliccin Mahaifi Nau’i Biyu Ne Na Yin Dole Da Na Izini.........

Savani Tsakanin Ma’aurata Da Hukuncin Adalai.......................

Shar'anta Aika Masu Hukunci Biyu..............................................

Hukuncin Cutar Da Mace Da yin Saki Asanadiyyar Cutarwa......

Rabon Kwana Da Adalci Tsakanini Ma’aurata.............................

Kyautar Kwana Da Sayar Da Shi...................................................

Bin Iyaye........................................................................................

Aikin Mace Da Matsayinta A Musulunci......................................

iv

Muqaddima

Kalmar ijbari da Malaman fiqihu (Malikiyya) suka yi amfani da ita

wajen ayyana mahaifi da ikon da yake dashi na aurar da 'yarsa qarama

kan dole, ta jawo mabambantan fahimta tsakanin malumma. Wasu na

fahimtar ijbari na nufin tilastawa; inda wasu ke fahimtar akasin haka.

Bisa wannan da la’akari da Hadisai na Manzon Allah (SAW) Malamai

suka karawa juna sani cewa, wasu ba su goyi bayan auren dole ba,

wasu kuma na cewa mahaifi na da Ijbar kan 'yarsa.

Bincike da tuntubar al’umma da Kungiyar WRAPA ta gudanar

a jihohin arewa maso yamma guda bakwai (Jigawa, Kaduna, Kano,

Katsina, Kebbi, Sokoto, Zamfara) sun tabbatar da cewa iyaye na

fakewa da damar uba mahaifi ta Ijbari su tursasawa ’ya’yan su mata ta

hanyar aurar dasu ga duk wanda su iyayen suka ga dama. A lokuta da

dama; ba tare da la'akari da cewa shi aure wani muhimmin abu ne

wanda xorewarshi ko wargajewarshi al’amari ne da yake shafar

ma’auratan fiye da kowa ba. Da kuma fahimtar cewa illolin dake tare

da wargajewar shi abubuwa ne dake shafar iyayen da ma'aurata,

harma da al’umma baki daya.

A gefe guda kuma, masana da masu bincike da mahalarta

tarurruka sunyi savani. Wani vangaren na ingantar da Ijbari bisa

dogara da ra’ayin wasu Malaman mazahib; bugu da kari suna kafa

hujja da cewar wannan matsaya yayi dai dai da koyarwar Mazhabar

Malikiyya wadda ita ake bi a Najeriya. Wani bangare kuma na ganin

cewa Ijbari bashi da tushe a Qur'ani ko a Hadisan Manzo (S.A.W) sai

dai ra'ayin Magabata (Fuqaha'u).

A cikin wannan yanayi muna fata za'a faxaxa bincike da nufin

cimma matsaya akan wannan al'amari. Tare da fatar za’a lura da

waxannan abubuwa: Na xaya cewar Shariar Musulinci an gina ta akan

manufofi da suka haxa da nufin gusar da barna daga al’umma da

kuma kawo musu fa'ida (Maslaha). Na biyu amincewa da abinda ke

gudana a tsakanin al’umma a yayin da muka tsinchi kammu a yadda

xaukaka anfani da damar Ijbari sau da yawa kan zama ana kare

v

maslahar xaixai ku ne savanin akasarin al’umma; koda kuwa hakan

zai cutar da yarinyar da akayi wa aure bisa wannan damar. Kungiyar

WRAPA tana murna da ci gaba da tattaunawa da karfafa bincike mai

zurfi akan wannan maudu’i tare da fatan nan zuwa gaba masana zasu

kai ga matsaya mai kara karfafa hakkin ma’aurata a zaman aure a

musulunci.

Bisanin haka Kungiyar WRAPA na nuni ga bukatar samar da

matsaya ta gaugawa da la’akari da halin da ‘ya’ya mata suke fadawa.

Saboda haka mu lura yayin xaukan ko wane irin mataki, kasancewar

’ya’ya amanar Allah ce a hannun mu. Iyayen ’ya’ya, malamai,

shugabannin al’umma da hukumomin xabbaqa addinin Musulunci na

da haqqin ganin an bi duk wata hanya da zata samar da mafita da

maslaha a kan wannan al’amari. Mussamman saboda la’akari da

rayuwar yara mata waxanda kan tsinci kansu a halaye masu muni a

yayin da aka aurar dasu a karanchin shekaru ko aka tilasta aurar dasu

ga wanda basu so. Allahu a’alamu.

vi

Godiya

Godiya ta tabbata ga Allah mai rahama mai jinqai. tsira da aminci su

tabbata ga fiyayyen halitta da iyalan gidansa da sahabbansa da

waxanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwan ranar

sakamako.

Bayan haka, muna miqa godiya ta musamman da jinjina ga

asusun (Marc Arthur) wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa

tahanyar tallafi da taimako waxanda suka dace ga qungiyar cigaban

mata da kare haqqoqinsu, babu shakka wannan qungiya da haxin

gwiwar jihohin Arewa maso yamma guda bakwai sun cancanci yabo

da jinjina bisa ga gudunmawar da suka bayar don ganin aiwatar da

shirin nan na dokokin zamantakewar aure. Ba shakka wannan tallafi

ya haxa da xaukar nauyin samar da kayan aiki da qarfafa gwiwa

wanda hakan ba qaramar gudunmawa ya bayar ba wajen samun

cikakkiyar nasarar shirin ba, tsawon shekaru goma da suka wuce.

Haka nan wannan qungiya ta sami nasarar shirya taron

ilimantarwa a yankin Bwari a babban birnin Tarayyar Najeriya Abuja,

wannan taro an shafe tsawon kwanaki bakwai ana aiwatar da shi

(daga 2-9 ga watan Nuwamba 2014) tare da haxin gwiwar cibiyar

kare haqqoqin xan adam a musulunci mai taken“Ra’ayoyin qwararru da masana fiqihun zamantakewar iyali, don bunqasa hanyoyi da qudurce-qudurcen siyasa da suka shafi al-adun aure da saki’” kamar

yadda aka rairayo batutuwan da za’a tattauna akansu daga batutuwa

da aikace-aikace daban-daban na wannan qungiya tare da goyon

bayan Jihohin da aka ambata na Arewa maso yammacin Najeriya

guda bakwai wato Jigawa da Katsina da Kaduna da Kano da Kebbi da

Sokoto da kuma Zamfara. Haqiqa waxannan taruka sun sami

baquncin mahalarta masu xumbin yawa da suka haxa da malamai, da

wakilan cibiyoyin ilimi, da na shari’ah da malaman addinin musulunci

da hukumomin yaxa labarai.

Daga cikin sakamakon qarshe da mahalarta tarukan suka

amince akansu sun haxa da wajabcin samar da tsare-tsare da sababbin

vii

dabaru na bunqasa matakin ilimi na al’umma tare da wayar da kan

al’umma akan matsalolin da ke da mummunan tasiri ga haqqoqin

mata a qarqashi abubuwan da dokokin zamantakewar iyali suka qunsa

gwargwadon al’adun aure da kyakkyawar zamantakewa tsakanin iyali.

Kamar yadda an haxu akan cewa hanya guda xaya tilo ta aiwatar da

waxannan wasiyyoyi a aikace itace ta gabatar da su ta hanyar

huxubobi akan mimbari a masallatan Juma’ah.

Haka nan zavar mimbarin huxuba don isar da saqon da ke

qunshe cikin waxannan takardu yunquri ne da zai yi matuqar tasiri

wajen yaqar nau’oi daban-daban na ta’addanci da musgunawa da ake

yiwa mata da yara a cikin wannan al’umma ta mu kamar yadda

nazarce-nazarce na dokokin zamantakewa suka tabbatar. Ba shakka

yin hakan zai tabbatar da adalci ga kowa musamman ma waxanda

suke cikin barazanar musgunawa a waxannan jihohi na Arewa maso

gabas da muke magana akansu, kamar yadda kuma hakan zai qara

xaukaka martabar musulunci da musulmi a wannan qasa

viii

Gabatarwa

Da sunan Allah Mai rahama Mai Jinqai.

Dukkan godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin talikai, tsira da amincin

Allah su tabbata ga fiyayyen manzanni shugabanmu annabi

Muhammad da alayensa da sahabbansa da waxanda suka yi kira irin

kiransa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka: Haqiqa qungiyar kare haqqoqin mata da tabbatar da yi

musu Adalci (WRAPA) Najeriya ta yi namijin qoqari wajen kare

haqqoqin mata dai-dai da tanade-tanaden shari’ar musulunci na loqaci

mai tsawo wanda ya wuce shekaru goma. kamar yadda kuma bata yin

qasa a gwiwa wajen gayyato malamai da alqalai da malaman jami’o’i

don su haxu su tattauna akan al’amuran da suka shafi zamantakewar

iyali a mahangar Shari’ar Musulunci da nufin wayar da kan musulmi

akan haqqoqin mata. wannan qungiya ta shirya taruka wanda daga

cikinsu akwai wanda akayi a watan Agustar shekara ta 2009 da aka

gudanar a jihar Jigawa wanda mahalarta fiye da sittin da suka haxa da

malamai da alqalai da lauyoyi da malaman jami’ah suka halarta suka

kuma tattauna batutuwa kamar haka:

1. Ginshiqan walicci.

2. Mutuwar aure da abubuwa masu alaqa da shi.

3. Xaukar nauyin wacce aka saka da daxaxa mata.

3. Shayarwa bayan saki ko mutuwa.

5. Takardar registar aure a hukumance.

Ba shakka mahalarta sun tattauna waxannan batutuwa yadda ya

kamata, suka kuma kai ga matsaya wacce ta cancanci yabawa a

waxansu daga cikinsu, duk da cewa sun kaucewa magana akan

registar aure da hukunce-hukuncen damar da waliyyi ke da ita ta

auren dole.

A waxansu daga cikin irin waxannan taruka da aka yi na

tattaunawa waxansu sun nemi in rubuta littafi da harshen Hausa

ix

wanda zai yi qarin haske akan waxannan batutuwa da aka ambata

wanda kuma zai fayyacewa mutane irin abubuwan da suka shafi

rayuwarsu ta aure, kai da ma ta zamantakewa, ya kuma mayar da su

kan qa’idaojin addini da dokokinsa, ya kuma nuna musu hikimomin

da suke cikin zamantakewar iyali da hukunce-hukuncen su, wanda

hakan tasa na rubuta musu littafi mai taken “kundin zamantakewar iyali”. Haka nan a taron da mukayi a watan Satumba na shekarar

2015, mahalarta wannan taro sun amince da a rubuta huxubobi na

minbari da za su dace da abubuwan da littafin ya kunsa, a cewar su

lalle mai huxuba dai-dai yake da mai wa’azi wajen irin babbar

gudunmawa da tasirin da yake da shi matuqa a cikin al’ummarsa da

masu sauraronsa, da jama’arsa, kamar yadda yake kuma xan uwa ne

na mai bayar da tarbiyya da malami, wajen samun matsayi a zukatan

mutane gwargwadon kyautatawarsa da yin sa tsakani da Allah. Kamar

yadda a waxansu lokuta ma Allah kan bashi matsayi na musamman

wanda manyan mutane masu muqamin ba sa iya kaiwa ko kusa da shi.

Dukkan waxannan abubuwa sukan samo asali ne daga

kyakkyawan lafazi da ingantacciyar hanyar fa’idantarwa da qwarewa

wajen yin tasiri ga mutane ta hanyar siffantuwa dajin tsoron Allah da

yin abu tsakani da Allah tare da tsantsani. Bisa wannan ne na ga

dacewar in amsa wannan kira na samar da huxubobi da za su taimaka

wajen inganta al’amuran aure da qara samar da haxin kai tsakanin

ma’aurata, kamar yadda kuma na yi musu alqawarin cewa zan rubuta

wannan abu da aka nemi in rubuta, haka nan kuma waxansu daga

cikin mahalarta sun taimakeni ta hanyar aiko da waxansu ayoyi da

hadisai da zasu taimaka min wajen yin hakan, ina yi musu godiya

qwarai bisa wannan taimako.

Daga cikin waxannan bayin Allah akwai mai girma alqalin

kotun shari’ah a matakin farko dake jihar Jigawa mai girma Alqali

Bashir Birnin kudu, da ‘yar uwa malama Murjanatu Ibrahim daga

Katsina da sauransu. Ba shakka babban malamin nan mai suna Khairi

Sa’id yana faxa a mashahurin littafin nan nasa cewa“ba shakka mai huxuba a masallaci da mai wa’azin a taron jama’a sun fi tasiri a cikin zukatan jama’a fiye da duk wata kafa ta jan hankali ko ta hukuma ta

x

al’umma da jagorori da sojoji da jami’an tsaro. Domin sau da yawa jama’a kan ji tsoron waxannan da muka ambata, to amma fa ba sa son su. Shi kuwa mai huxuba a sanadiyyar nuna tausayinsa da kuvutarsa daga dukkan wani abin suka, ya kan iya samun damar tunvuke tushen sharri da ke dashe acikin zukatan masu aikata laifuka, ya kuma cusa musu jin tsoron Allah, da son gaskiya da amincewa da adalci da taimakon mutane a zukatansu. Ba shakka aikin mai huxuba shine gyara zukata, da farfaxo da kyawawan halaye a zukatan mutane, tare da inganta rayayyun zukata da tarbiya maxaukakiya don yin aiyuka tsarkakakku da aiki tuquru ba don kome ba saidon neman lada a wajen Allah Maxaukakin Sarki da manufar amfanar da mutane, don haka in anyi la’akari da wannan za’a ga cewa matuqar mai huxuba ya aiwatar da aikinsa akan doron abin da aka ambata fuskarsa za ta yi qwarjini, da annashuwa ya kuma kaishi ga wani matsayi maxaukai a wajen mutane.” Daga Khairi Sa’id

Wajen tattara waxannan huxubobi na yi amfani da littattafan

mazahabar Malikiyya irinsu“al-fiqhhul Maliki fi thaubihi al-jadid” na

Dakta Muhammad Bashir Shaqfah da littafin “Mudawwanatu al-fiqhi al-maliki wa adillatuhu” na Dakta As-sadiq Abdur-Rahman al-Firyani

daga cikin littattafan huxuba kuma akwai “al-mufid lil khuxaba, wa al-murshidin” na Imam Nasir Adam da“mausu’atu a immati al-haramain ash-Sharifain” wanda Khairi Sa’id ya tattara da sauransu.

Muna roqon Allah Maxaukain Sarki ya sanya wannan aiki ya zama

tsarkakakke don neman yardarsa, ya kuma zamo mai amfani ga

musulmai baki xaya, haqiqa shi mai iko ne akan haka, madalla da

wanda muka dogara da shi kuma madalla da wanda muke fatan ya

bamu nasara.

Goni Muhammad Sa’ad Ngamdu.

xi

1

1

Rayuwar Mace Qarqashin Inuwar Musulunci

Da sunan Allah Mai rahama Mai jinqai.

Godiya ta tabbata ga Allah wanda yayi mace da namiji daga xigon

maniyyi a lokacin da aka tofa shi cikin mahaifa, ya kuma fifita

sashinsu wajen halitta.”Kuma namiji bai zamo kamar mace ba”. (Al-

Imran: 36). Ina qara yi masa godiya bisa ni’imominsa waxanda ba za

a iya qididdige su ba. Ina shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai

Allah, shi kaxai yake bashi da abokin tarayya, sunaye kyawawa nasa

ne, da siffofi maxaukaka, ina kuma shedawa lalle shugabanmu

Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne wanda shine abin

yarda, ma’abocin ceto babba, da daraja mafi girma. Allah yayi daxin

tsira a gare shi da alayensa da sahabbansa ma’abota falala da kaifin

hankali, Allah yayi daxin aminci a gareshi aminci mai yawa.

Bayan haka, “ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne.

(Nisa’i:1).

Ya ku musulmai! ya kamata ku sani cewa an xauki lokaci mai

matuqar tsawo. Kuma an shafe dubunnan shekaru mace tana zaune

cikin wani irin yanayi mara daxi kafin zuwan addinin Musulunci, ba

shakka, mace ta kasance abar wasa da ita a hannun azzalumai tana

fuskantar nau’oi daban-daban na azaba da tozartawa, kamar yadda ta

sha fama da qasqanci da wulaqanci, a kwana a tashi a kullum ba abin

da take qara fuskanta sai zalunci da rashin kwanciyar hankali, tsawon

2

waxannan lokuta, haka nan aka kasa samun koda mutum xaya

shiryayyeda zai ji tausayinta ko dai a matsayin ta na uwa, ko ‘ya ko

matar aure, musamman ma wacce mijinta ya mutu da marainiya a

cikinsu ko ma kowacce mai rauni.

Mace ta kasance acikin al’ummomin Girkawa ana sayen ta, a

kuma sayar a kasuwanni kamar yadda ake sayar da dabbobi da bayi,

kai har ta kai ga cewa ma suna yi mata laqabi da najasa daga aikin

shexan dukkan wannan fa yana faruwa a yankin gabashin Turai.

Dangane kuwa da yammacin Turai an samu cewa har wani taro aka

gudanar a shekara ta 756 Miladiyya don lalubo ko ana iya sa mace

cikin jinsin bil-adama? to koma dai menene ita ba komai bace in

banda mai yin hidima ga namiji, sannan kuma a wancen lokacin ne

aka fitar da wani qudiri da shugabannin addini suka rattabawa hannu a

qasashen Turai cewa haramun ne ga mace ta karanta littafi mai tsarki

a domin kasancewarta ummul-aba’isin duk wani bala’i da jinsin bil-

adama ke fama dashi a wannan duniya a rayuwarsu.

Haqiqa wannan mataki nasu na qasqantar da mace har ta kai an

sami waxansu daga cikinsu da su ke iqirarin cewa lalle mace sharri ce

da ya zamo tilas ayi amfani da shi, kuma wani bala’i ne da zukata

suka shaqu da shi, kuma masifa ce wacce ba ta yadda za a iya guje

mata, kamar yadda ake ganinta holoqo hadarin kaka da kuma ciwon

da ba ya jin magani.

Su kuwa al’ummomin qasar Sin a zamanin dasun kasance

acikinsu idan mijin mace ya mutu sai itama a qone ta domin cigaba da

rayuwarta bashi da wani amfani, a rashin tausayi irin na su da halayya

irin ta dabbobi masu matuqar mugunta. A zamanin Jahiliyya kuwa

mace ta kasance a yankin tsibirin larabawa a na binne ta a rairayi tun

tana yarinya qarama, kamar yadda duk wanda aka yi masa bushara da

cewa matarsa ta haifi ‘ya mace sai ya rinqa tsanar fitowa jama’a su

ganshi saboda munin abin da aka yi masa bushara da shi, ba shakka

wannan wauta da girma take, baya ga kafircewa kyautar Allah, don in

ba domin haka ba mene ne na murtuke fuska da hautsinewarta da

zama cikin xaure fuska? ba don kome ba sai don abokiyar rayuwarsa

ta haifi mace, Allah Maxaukakin Sarki yana cewa “kuma idan aka

3

yiwa xayansu bushara da mace sai fuskarsa ta wuni baqa qirin, alhali kuwa yana mai cike da baqin ciki yana voyewa daga mutane domin munin abinda aka yi masa bushara da shi. Shin zai riqe shi ne akan wulaqanci, ko ko zai turbuxe shi a cikin turvaya? To abin da suke hukuntawa ya munana” (Nahl: 58-59). To hakanan dai mace ta shafe

loqaci mai tsawo tana rayuwa mara xaxi qarqashin hukunci na

zalunci mai muni da kama karya da ta zamo ruwan dare, yadda ake

amfani da mace kamar wata na’ura da ake amfani da ita ba tare da

tausayawa ba ko kaxan. Mace tana cikin irin wannan yanayi na baqin

ciki ne kwatsam sai hasken musulunci ya keto, hasken rahamarsa da

addininsa ya mamaye ko ina, duniya ta fahimci irin laifukan da ta

tafka dangane da mace.

Mace a mahangar musulunci ba ta gaza a kasancewarta warin

namiji ba (shi kuma na ta warin) domin kuwa annabi tsira da amincin

Allah su tabbata a gareshi yace: “mata tsagi ne na maza”1 to a wannan

loqaci aka wayi gari duniya ta amince za ta bawa mace waxansu daga

cikin haqqoqinta.

Ba ta yadda za ayi mace ta sami dukkan haqqoqinta cikakku

har sai in ta yi rayuwa a qarqashin inuwar addinin Musulunci. Domin

kuwa duk wani tanadi ko tsari da za'ayi wa rayuwar mace Musulma

abune mai iyaka da karancin falala. Wasu dokoki da haqqoqin da

qasashen Turai na wannan zamani waxanda ba ruwansu da addinin

Musulunci suka tsara ba nata bane. Domin kuwa addinin musulunci

shine ya shar'antawa mace haqqoqinta cikakku yayi bayaninsu dalla-

dalla; haqqoqin da take da su da nauyin da ya hau kanta. Ya tabbatar

mata da alkhairai masu yawa da abubuwa na kamala.

Musulunci ya lullube rayuwarta mai rauni da nau’i daban daban

na karamci da girmamawa. Ya kuma yiwa mutuncinta tanade-tanade

na kare shi da kulawa da shi a wani irin yanayi da bata tava

1 Ahmad da Abu Dawud da Bukhari

4

mafarkinsa ba kafin zuwan hasken Musulunci, ballantana kuma tayi

kwaxayin samunsa ko ta wacce irin hanya.

Don haka ya ke 'yar uwa musulma, abin nema gareki shine ki

tsare kanki a duk halin da zaki samu kanki a ciki. Haka kuma su

waxanda suka xauki nauyin sauke haqqoqinki ke mace musulma

lallai ne suyi adalci a fili da boye.

Haka nan addinin musulunci cikin hikimarsa ya kevance mace

da waxansu aiyuka da suka dace da ita don bayar da gudunmawarta

wajen gina al’umma bisa la’akari da siffofinta na musamman. Ya

ware mata waxansu ayyuka da ba mai iya aiwatar da su sai ita; da

suka haxa da xaukar ciki da haihuwa da shayarwa da tarbiyyar yara da

hidimar iyali da basu kulawa da wasu sauran ayyuka da suka dace da

irin yanayinta na musamman. A dukkan irin waxannan aiyuka da

mace za ta yi a ciki da wajen gida za ta yi sune cikin sutura da kulawa

da karewa da tsare mutunci da kykkyawan xabi’a da kyawawan

xabi’u na bil adama.

Ba shakka waxannan aiyuka na da matuqar muhimmanci

wanda bai gazana waxanda maza suke yi a fagage daban-daban ba.

Shugaban mawaqa (Ahmad Shauqi) Yana cewa:

“Ku reni ‘ya’yanku mata bisa kyawawan xabi’u, don

hakan babbar garkuwa ce a garesu daga masu

wulaqantasu, uwa makarantace in har ka bata horo, to ka

bada horo ga al’umma ingantacciya, uwa dausayi ce

matuqar an kula da ba shi ruwa sai yayi ta yin yabanya

matuqa”.

Haka nan manzon Allah tsira da amincin Allah su qara tabbata gare

shi yana cewa: “duk wanda yake da ‘ya’ya uku mata sai ya rene su, ya tausaya musu, ya xauki nauyinsu Aljannah ta tabbata gareshi1” sai aka

1 Bukhari aadab al-mufrad daibn Majah

5

ce ‘ya manzon Allah koda guda biyune? Sai yace: “koda guda biyu ne”.

6

Huxuba Ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah wanda yake alqalanci da hukuncin

gaskiya, kuma shine mafiyin dukkan wani mai hikima, ya yi hukunci

na adalci ya kuma yi umurni da shi, ya kuma haramtawa kansa

zalunci, ya haramta shi ga bayinsa, kuma shine mafi tausayin masu

tausayi, ina shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah wanda

shine Ubangijin na farko da na qarshe, ina kuma shedawa

shugabanmu annabi Muhammad bawansa ne kuma manzonsa, kuma

shine wanda ya fifita akan duk halittunsa, tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi da alayensa tsarkaka da sahabbansa masu iklasi da

duk wanda ya bi tafarkinsa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:

Ya ku mutane; ina yiwa kai na da ku wasiyya da jin

tsoron Allah ina kuma tunatar da ku cewa ba shakka

musulunci yayi umarni da girmama mata a matsayinsu na

iyaye ko ‘ya’ya ko matan aure, kamar yadda yayi umarni

da girmama su a loqacin da suka kasance ‘yan uwan

mahaifa maza ko mata, haka nan ya qarfafa tausaya musu

a loqacin da mazajensu suka rasu da loqacin da su ka

zamo marayu. Mace a mahangar musulunci itace mai

renon mazaje kuma tushen kowanne gwarzon namiji,

kuma ita ce uwa ga kowanne babban mutum kamar

yadda take makaranta da take yaye kowanne jagora abin

koyi. Don haka idan ta gyaru to gaba xayan al’umma ta

gyaru haka nan in ta karkace daga hanya to kowanne

tubali na ginin al’umma zai yi rauni, daga qarshe gininta

ya rushe. Don haka duk wani mai karamci zai karramata

kuma ba mai wulaqanta haqqinta sai wulaqantacce,

kamar yadda ba shakka tana iya yin galaba akan duk

wani mai girma, ita kuwa ba mai yin galaba a kanta sai

mai mummunan hali, kamar yadda ma’aikin Allah tsira

7

da amincin Allah su tabbata a gare shi yake cewa: “ina yi

muku wasiyya da kyautatawa mata bisa alheri, don

haqiqa ita mace an halicce ta ne daga qashin haqarqari

karkatacce, kuma mafi karkacewa a qashin haqarqari

shine samansa, idan kayi qoqarin miqar dashi sai ka

karyashi in kuma ka barshi ba zai gushe ba yana karkace

ba”1. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “kuma Allah

ya sanya muku matan aure daga kawunanku, kuma ya

sanya muku daga matan aurenku xiya da jikoki, kuma ya

azurtaku daga abubuwa masu daxi, shin fa, da qarya suke

yin imani, kuma da ni‘imar Allah suke kafirta? (Nahl:

72). Wannan shine tubali na farko da musulunci ya xora

harsashin ginin karrama mace da ‘yanto ta daga

waxancan tsare-tsare na kama-karya waxanda ta shafe

lokaci mai tsawo tana rayuwa a qarqashinsu, ya kuma

ceto rayuwarta daga waccan guguwa da ka iya mayar da

rayuwarta ta zama mara amfani. Kuma manzon Allah

tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa:

“lalle Allah ya haramta muku savawa iyaye mata da

binne ‘ya’ya mata kuma mafi alherin cikinku shine mafi

alheri ga iyalansa kuma nine mafi alherinku ga iyalina”2

yaku “yan uwa” waxannan misalai hujjoji ne da ke

tabbatar da cewa mace tana da matuqar qima da matsayi

a musulunci, kamar yadda duk wani abu da ta aikata za ta

sami kyakkyawan sakamakonsa, haka nan duk abinda ta

aikata za ta xauki nauyin alhakinsa.

Allah Maxaukakin Sarki Yana cewa: “kuma wani rai baya yin tsirfa face domin kansa, kuma mai xaukar nauyi baya xaukar nauyin wani, sa’annan ya baku labari ga abin da kuka kasance a cikinsa kuna savawa juna” (An-Nam1 :64). Kamar yadda kuma yake cewa:

1 Bukhari ya ruwaito

2 An hadu akansa

8

Kuma su matan suna da kamar abinda yake akansu yadda

aka sani kuma maza suna da wata daraja akansu, (Baqara

228).

Kuma ba shakka wannan daraja da aka ambata ba zata tava bawa

namiji damar tauye wani haqqi na mace koda daidai da qwayar

tsakiya ne ba ko yayi watsi da martabarta, abin da ake nufi da darajar

shine tsayuwa da zai yi wajen sauke nauyin da ke kansa da kuma

jagoranci da aka bashi bisa abin da Allah cikin hikimarsa ya sanyawa

maza na qarfin jiki da na hali da kaifin hankali waxanda bai sanya su

ga mace ba.

Kamar yadda Allah Maxaukain Sarki yake cewa:

Maza masu tsayuwa ne akan mata, saboda abinda Allah ya fifita sashensu da shi akan sashe, kuma saboda abinda suka ciyar daga dukiyoyinsu” (Nisa’i: 34) don haka in

har mace tana son daidaito tsakanin ta da namiji to ba

laifi Allah ya share mata hanyar yin hakan bisa abinda ya

dace da ita wato yin aiyuka na qwarai, saboda faxin

Allah Maxaukakin Sarki: “saboda haka Ubangiji ya

karva musu da cewa “Lalle ne ni ba zan tozartar da aikin wani mai aiki ba daga gareku, namiji ko kuwa mace sashenku daga sashe” (al-Imran: 195), haka nan kuma

yana cewa: “wanda ya aikata aiki na qwarai daga namiji ko mace alhali yana mumini, to haqiqa muna rayar da shi rayuwa mai daxi. Kuma haqiqa muna saka musu ladansu da mafi kyawun abinda suka kasance suna aikatawa.

(Nahl: 97).

Hakanan duk wanda ya cewa mace za ta iya yin dai-dai da namiji a

kowanne fage na rayuwa, to ba shakka ya yaudare ta, ya kuma gajiyar

da ita, saboda faxin Allah Maxaukakin Sarki:

Halittar Allah da ya halicci mutane a kanta, babu

musanyawa ga halittar Allah. wannan shine addini

9

madaidaici, kuma amma mafi yawan mutane basu sani

ba” (Rum: 30) yana kuma cewa: “hanyar Allah wacce ta

shuxe daga gabanin wannan, kuma ba zaka sami

musanya ba ga hanyar Allah (Fath: 23).

Ya Allah kada ka bar wani zunubi namu a wanna wuri da muke face

ka gafartashi, haka nan wani baqin ciki face ka yaye mana shi, haka

nan wanda ya yi nesa da iyalinsa face ka mayar da shi, haka nan mara

lafiya face ka warkar da shi, haka nan mai bashi face ka hore masa

abin biya, haka nan wanda yake cikin wata damuwa face ka fitar

dashi, hakan duk wata buqata daga cikin buqatu na duniya da lahira

wacce a cikinta akwai masalaharmu ka kuma yarda da ita face ka biya

mana ita, ka sauqaqeta ya Ubangijin talikai.

Yaku bayin Allah! “Haqiqa Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’a, yana yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90) ku tuna Allah sai ya tuna ku, ku kuma yi masa

godiya bisa ga ni’imominsa sai ya qara muku.1

1 Daga littafin Al-mufid lii khutaba’ wal murshidin, na Imam Muhammad Nasir Adam

10

2

Aure Da Gina Rayuwar Iyali A Musulunci.

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya halalta aure, ya haramta lalata,

wanda ya sanya mala’iku su zamo ma’abota fukafukai biyu-biyu da

uku-uku da huxu-huxu, wanda Allah yake cewa: “ku auri abinda yayi muku daxi daga mata, biyu-biyu da uku-uku da huxu-huxu. (an Nisa’:

3).

Godiya ta tabbata ga wanda ya halicci ma’aurata biyu namiji da

mace daga xigon maniyyi a loqacin da yake shiga cikin mahaifa, ina

shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, wanda yake shi

kaxai ne mai samarwa, bai Haifa ba, ba’a haife shi ba, kuma babu

xaya da ya kasance tamka a gareshi, kuma ina shedawa cewa

Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, ma’abocin kyawawan

halaye, tsira da amincin Allah su qara tabbata ga qololuwar abin koyi

na qwarai kuma babban tsani na kaiwa ga Allah, shugabanmu

Muhammad fiyayyen waxanda suka aura suka aurar ya kuma ba aure

cikakken haqqoqinsa a bayyane da voye wanda ke cewa:

To amma ni na kan yi azumi in kuma sha in kuma

kwanta in yi barci, ina kuma aurar mata, kuma duk

wanda ya kaucewa tafarkin Sunnah ta to baya tare da ni”1

da alayensa tsarkaka da sahabbansa shiryayyu da duk

wanda ya bi tafarkinsu bisa kyautatawa har zuwa ranar

sakamako, “yinin da mutane ke tashi zuwa ga Ubangijin

halitta (Muxaffifin: 6).

1 Bukhar da Ahmad

11

Bayan haka:

ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya

halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi

ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza

da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon

juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya

kasance akanku Mai tsaro ne. (an-Nisa’i: 1) “ya ku

waxanda suka yi imani ku bi Allah da taqawa, kuma ku

faxi magana madaidaiciya. Ya kyautata muku ayyukan

ku, kuma ya gafarta muku zunubanku. Kuma wanda yayi

xa’a ga Allah da manzonsa to lalle ya rabauta babban

rabo mai girma (Ahzab 70-71).

Lalle mu mun gitta amana ga sammai da qassai da

duwatsu, sai suka qi xaukarta kuma suka ji tsoro daga

gareta, kuma mutum ya xauketa, lalle shi (mutum) ya

kasance mai yawan zalunci, kuma mai yawan jahilci

(Ahzab: 72).

Haka nanAllah bai nufi cewa xan Adam zai yi rayuwa kamar sauran

dabbobi da sauran ‘yan uwansa a halitta na halittu daban-daban ba,

wato ya zamo sha’awararsa a sake take ba tare da an yi mata wani

linzami ba, ta yadda mu’amala tsakanin mace da namiji za ta wayi

gari sakaka ba abin da yake saita ta. A maimakon haka sai ya sanya

wani tsari wanda zai dace da xan adam na auratayya wanda shine zai

kare masa darajarsa, ya tsare masa mutuncinsa da karamcinsa ya

kuma yi masa sakamako akan hakan.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana

cewa: “hakama acikin saduwar da xayan ku zai yi da matarsa akwai ladan sadaka” sai su ka ce: “ya manzon Allah shin xayan mu ya biya buqatarsa, sannan kuma ya kasance ya na da lada? Sai yace: shin kuna ganin cewa da ya sanya ta cikin haramun zai kasance yana da zunubi?

12

To hakama idan ya sanya ta cikin halal zai kasance ya na da lada1”,

wato sai ya sanya haxuwar namiji da mace haxuwa ce mai karamci da

aka gina ta akan yardarsu ta kuma zamo haxuwa ce ta cuxe-ni-in cuxe

ka bayan kowannensu ya bayyana yardarsa a fili, sannan kuma da

shedawa cewa kowanne daga cikinsu ya zamo wani sashe ne na xan

uwansa, wanda da hakane ya xora sha’awa bisa amintacciyar hanya

ya kuma kare dangantaka daga vacewa, ya kuma ba mace kariya daga

zamowa wata gona ta biyan buqatar kowanne shashasha. Don haka sai

ya sanya wani tubali mai qarfi na ginin zamantakewar iyali wacce aka

kewaye ta qauna irin ta uwa da son mahaifi ta yadda zamantakewar za

ta haifar da wani tsiro mai kyau, tare da samar da zuri’a abar ala-san-

barka. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Kuma Allah ya sanya muku matan aure daga kawunanku,

kuma ya sanya muku daga matan auren ku xiya da jikoki

kuma ya azurta ku da abubuwa masu daxi, shin fa da

qarya suke yin imani, kuma da ni‘imar Allah suke

kafirta? (Nahl: 72)

Kamar yadda matsayin mace bai tsaya ga kasancewarta abokiyar

zaman namiji a duniya kaxai ba, a maimakon haka itace za ta samar

masa natsuwa da kwanciyar hankali, baya ga babban nauyi da ke

wuyan mace, wanda ya fara tun daga haihuwa har zuwa ga duk wani

abu da bai wuce ikonta na xabi’a da na halitta ba. Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa:

Kuma akwai daga ayoyinsa ya halalta muku matan aure

daga kanku domin ku natsu zuwa gareta, kuma ya sanya

soyayya da rahama a tsakaninku. lalle ne daga cikin

wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani” (Rum:

21). Haqiqa aure yana kare ma’abocinsa daga munanan

halaye da sha’awa ke iya jawowa, ya kuma bashi dama

1 Muslim da Ahmad suka ruwaito

13

tayin rayuwa iri biyu, mai qarewa da dauwamammiya (ta

hanyar barin zuri’a). Domin idan ba don aure ba da ba’a

sami wanzuwar jinsin xan-adam a doron bayan qasa ba.

don haka shi aure shi ne abin da ke da dawwamar da

ambato ya kuma xaukaka darajar wanda ya yi shi.

Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi

yace: “idan mutum yayi aure to ya cika rabin addininsa

don haka sai yaji tsoron Allah a sauran rabin”.1 “duk

wanda ke da wadatar da zai yi aure bai yi ba, baya tare da

ni”2 “duniya wani xan jin daxi ne, mafi alherin jin

daxinta it ace mace ta gari”3 kamar yadda kuma manzon

Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yake

cewa: “yaku taron matasa duk wanda yake da ikon

xaukar nauyin aure a cikinku to yayi aure domin ya fi

komai kawo runtse ido (daga kallon haram) ya fi komai

tsare farji (daga zina) wanda kuma ba zai iya ba to ya

lazimci azumi domin shi garkuwa ne a gareshi”4 ya kuma

ce: “ku auri matan da kuke qauna kuma masu haihuwa

domin al’umma ta, tafi sauran al’ummomi yawa a ranar

alqiyama5.

Haka nan yana da matuqar muhimmanci musan cewa mace rabin

tsagin namiji ce domin ya zo a wata ruwaya: “mata tsagi xaya ne na maza” Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

“Kuma su matan suna da kamar abin da yake akansu yadda aka sani kuma maza suna da wata daraja akansu” (Baqara: 228) bisa wannan

ne ya wajaba akan kowanne namiji ya san cewa, tsayawa tsayin daka

wajen ganin ya sauke nauyin amanar mace da ke wuyansa abu ne da

1 Baihaqi da Alhakim

2 Tabarani ya ruwaito

3 Ibn Majah da Tabarani

4 ABu Dawud da Ibn Majah

5 A hmad da Abu Dawud da Bukhari

14

ya zama wajibi gwargwadon ikonsa, wannan kuwa ya samo asali ne

kasancewar ita mace tana da yanayi na musamman da ya kevantu da

ita, kuma mace ba kamar namiji ta ke ba a halittar ta da xabi’unta, don

bincike ya nuna hatta qwayoyin halittar qwaqwalwarta an yi ta ne da

xabi’ar riqe abin da aka aika mata, ita kuwa ta namiji dawo da shi

take yi, wannan yazo dai-dai da faxin Allah Maxaukakin Sarki:

idan basu zama maza biyu ba, to namiji guda da mata

biyu, daga waxanda kuka yarda da su daga shedu”

(Baqara: 282), hakan yana daga cikin al’adar mata su

kafircewa kyautatawa wanda hakan ya na daga cikin

tauyayar addininsu da hankalinsu Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa: “kuma kuyi zamantakewa da su ta

alheri. sannan idan kun qisu, to akwai tsammanin kuqi

wani abu Allah ya sanya wani alheri mai yawa a cikinsa”

(Nisa: 19), haka nan a dunqule kuma Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa: “kuma kada ku manta da falalla a

tsakaninku, lalle ne Allah ga abin da ku ke aikatawa shi

mai gani ne. (Baqara 23).

Ya ku‘yan uwa na musulmi! Haqiqa mata masu taimakawa ne da aka

damqa a hannunku, kun karve su da amanar Allah ku ka halalta

farjinsu da kalmar Allah da amincewar iyayensu don haka kuji tsoron

Allah a cikin al’amarinsu. manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gareshi yana cewa:

Ka da wani mumini ya quntatawa wata mumina, in har

ya tsani wani hali nata zai yarda da wani na daban1.

Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

1 Imam Ahmad

15

Maza masu tsayuwa ne akan mata saboda abin da Allah

ya fifita sashensu da shi akan sashe, kuma saboda abin

da suka ciyar daga dukiyoyinsu. To salihan mata masu

xa’a ne masu tsarewa ga gaibi saboda abin da Allah ya

tsare. kuma waxanda kuke tsoron bijirewarsu to ku yi

musu gargaxi kuma ku qaurace musu a cikin wuraren

kwanciya, kuma ku doke su. sannan kuma idan sun yi

muku xa’a, to kada ku nemi wata hanya a kansu..”

(Nisa’i: 35). Haka nan yana da muhimanci mu ambata

cewa, lalle rayuwar zamantakewar aure ta sava kacokan

da sauran nau’oi na zamantakewa waxanda ba ita ba,

waxanda ka iya haxa tsakanin mace da namiji, kamar

yadda zamantakewar aure ta fita daban da kowacce a

shari’ar musulunci kasancewarta rayuwa ce ta

dundundun har zuwa rasuwar xaya daga cikin ma’aurata

ko kuma in rabuwa ta zo a rabu cikin kyautatawa, don

haka ba alaqa ce ta xan wani loqaci ba, kamar yadda take

alaqa ce da komai na ta yake a bayyane babu yaudara ko

ha’inci cikinta, kuma rayuwa ce ta gwargwadon iko da

babu takurawa ko gazawa a cikinta. Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa: “sai mawadaci ya ciyar daga wadatarsa

kuma wanda ake quntata masa arziqinsa to sai ya ciyar

daga abinda Allah ya bashi. Allah zai sanya sauqi a

bayan tsanani (Xalak: 7), haka nan rayuwar aure rayuwa

ce da ke tafiya bisa qa’idar nan ta “ba cutaba cutarwa”1

kamar yadda manzon Allah tsira da amincin Allah

sutabbata gare shi ya kasance yana yin umarni da haka a

cikin hadisansa.

Ba shakka aure ibada ce zalla, ciyarwa a cikinsa kuma sadaka ce,

kamar yadda matar aure ba baiwa ba ce, ba mai hidima ba ce, haka

nan rayuwar aure ba zamantakewa ce kawai ta abota ko sabo da juna

1 Muslim da Shafi’i da Ibn Majah

16

ba. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “kuma kada kuyi gurin abinda Allah ya fifita sashenku da shi akan sashe, maza suna da rabo daga abin da suka tsirfanta, kuma mata suna da rabo daga abin da suka tsirfanta. Ku roqi Allah daga falalarsa. Lalle ne Allah ya kasance ga dukkan kome masani. (Nisa’i: 32).

Kuma yadda ya zama tilas kada maza su manta da cewa an

halicce ta ne daga qashin haqarqari, kuma mafi karkacewa a qashin

haqarqari shine samansa, duk irin qoqarin da za kayi don miqar dashi

ba zai miqe ba sai dai ka karyashi kamar yadda babu mai karya shi sai

mugu. don haka kyautata musu yafi munana musu, kuma manzon

Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa:

An cusawa zukata xabi’ar qaunar wanda ya kyautata

musu da qin wanda ya munana musu”1 haka nan wani

mawaqi yana cewa:

Kyautatawa mutane in har kana son bautar da zukatansu,

don sau da dama kyautatawa kan bautar da xan-adam

Tsira da amincin Allah su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammad

da alayensa da sahabbansa kayi xaxin tsira mai yawa a gareshi.

1 Abu alfaraj al asfihani, hilyat al awliya’

17

Huxubata Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya sanya halittar mutum daga ruwa,

ya kuma sanya masa dangantaka da surukantaka haqiqa Ubangijin ku

ya kasance mai cikakken iko, ina shedawa babu abin bautawa da

gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya, madalla da

mai shiryawa da mai ba da nasara, ina sheda cewa shugabanmu annabi

Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne kuma ya kasance ga

muminai mai tausayi ne mai jinqai, tsira da aminci su tabbata ga

wanda aka aiko ga mutane gaba xayansu a matsayin mai bushara da

mai gargaxi, shugaban mu Muhammad shugaban waxanda suka yi

jihadi don xaukaka addinin Allah jihadi mafi girma, da alayensa masu

tsarki masu albarka da sahabbansa masu jihadi waxanda suka haifawa

musulunci masu kira da shiryawa, da waxanda suka suka biyo

bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako, ranar da dukiya da

‘ya’ya ba za suyi amfani ba, sai wanda ya zowa Allah da zuciya

kuvutacciya. “Ya Ubangijinmu! Ka bamu sanyin idanu daga

matanmu, da zuriyarmu kuma ka sanya mu shugabanni gamasu

taqawa.”

Bayan haka, “ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (an-

Nisa’i:1)

Ba shakka miji da mata sune ginshiqin zamantakewar iyali ta

gari, kamar yadda nauyin kulawa da iyali yana wuyansu haka nan

alhakin tabbatar da nagarta da kuvutarta daga kowacce barazana ita

ma tana wuyansu. Kuma mace ta gari a qarqashin koyarwar

musulunci itace tushen kowanne hali na kamala, mai tarbiyyar mazaje

da jarumai don haka in har tasowarta ta kasance ta qwarai, mai

xaukakar matsayi mai girman muqami domin kasancewarta

18

masana’antar mazaje. kamar yadda ake cewa duk loqacin da ka ga

jarumi namiji to ba shakka akwai mace a gefensa.

Uwa makaranta ce idan aka kula da ita, an kula da

al’umma mai qwarin tushe

Haka nan idan xabi’unta suka tavarvare halayenta suka karkace to

xaukacin al’umma sai ta wargaje, al’umma ta lalace, zamantakewar

iyali ta tavarvare, ruxani ya mamaye tsarin zamantakewar al‘umma,

fitina ta watsu ko’ina. Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata

a gare shi yana cewa: “ban bar wata fitina a baya na mafi cutarwa ga maza kamar mata ba”1

Kamar yadda aure shine mataki na farko na xaukar nauyin jagoranci

da shugabanci kamar yadda manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi yake cewa: “kowannenku mai kiwo ne kuma abin tausatawa akan abinda ake bashi kiwon”2

don haka Allah maxauakakin

sarki yake cewa:

Ya ku waxanda su ka yi imani, ku karewa kanku da

iyalinku wata wuta makamashinta mutane da duwatsu ne,

akanta akwai waxansu mala’iku masu kauri, masu qarfi.

Ba su savawa Allah ga abin da ya umurce su, kuma suna

aikata abin da ake umurninsu.” (Tahrim: 6). Kuma abu

mafi muhimmanci wanda addinin musulunci ya kula da

shi ga masu riqo da shi bayan imani da Allah da

kyakyawar niyya shine yiwa kai garkuwa domin kuwa

shi kansa imanin da Allah da manzanninsa yiwa kai

garkuwa ne daga halaka ta har abada.

1 An hadu akansa

2 An ruwaito shi a muwatta an kuma hadu akansa

19

Haka nan yiwa kai garkuwa ya game komai na rayuwa, kamar yadda

ya qunshi bin dukkan umarni da nisantar faxawa cikin abubuwan da

Allah Maxaukakin Sarki ya hana.

Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Ka cewa muminai maza su runtse daga ganinsu, kuma su

tsare farjojinsu. Wannan shine mafi tsarki a gare su. Lalle

ne Allah mai qididdigewa ne ga abin da suke

sana’antawa. Kuma ka cewa muminai mata su runtse

daga ganninsu, kuma su tsare farjojinsu, kuma kada su

bayyana qawarsu face abin da ya bayyana daga gare ta…

(Nur: 30-31).

Haka nan Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Kuma ku tabbata a cikin gidajenku, kuma kada ku yi fitar

gaye-gaye irin fitar gaye-gaye ta jahiliyyar fako. Kuma

ku tsaida salla, kuma ku bayar da zakka, ku yi xa’a ga

Allah da manzonsa (Ahzab: 33).

Kamar yadda akwai ayoyin alqur’ani masu yawa da hadisan manzon

Allah tsira da amincin Allah sutabbata a gare shi da suke yin nuni da

kamewar maza da mata gaba xayansu, haka nan ya zama tilas su haxa

gwiwa wajen tarbiyyar abin da Allah ya azurta su da shi na ‘ya’ya

maza da mata tarbiyya ta musulunci, kamar yadda ya zama wajibi

akan kowannensu ya taimaki xayan wajen bayar da gudummawarsa

da sauke nauyin da ke kansa na nauyin kula da iyali.

A koda yaushe manzon Allah tsira da amincin Allah ya tabbata

a gare shi yana magana ne da masu ingantaccen hankali. Don Allah

xan uwa bani labarin kana ganin akwai wanda zai amince a ce wanda

yake qarqashinsa ya tozarta ko da kuwa mai yi masa hidima ne ko

kuma dabbarsa? Ballantana kuma a ce ‘yarsa. Don haka manzon Allah

tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “ku yi aure kuma ku

20

hayayyafa don lalle ni zan fi sauran al’ummomi yawan jama’a a ranar alqiyama”1 domin mu san cewa lalle mu iyaye maza da mata tilas ne

mu sauke nauyin abin da musulunci ya wajabtawa kowanne daga

cikinmu wanda idan ba muyi hakan ba to mun ci amana. Allah

Maxaukakin Sarki yace:

Ya ku waxanda suka yi imani! kada ku yaudari Allah da

manzonsa, kuma ku yaudari amanoninku, alhali kuwa

kuna sane. (Anfal: 27) Haka nan kuma yana cewa;

Ka ce lalle masu hasara sune, waxanda su kayi hasarar

rayukansu da iyalansu, a ranar qiyama. To waccan fa

itace asara bayyananna (Zumar: 15)

Wani mawaqi yana cewa:

Maraya ba shine, wanda iyayensa su ka yi bankwana da

baqin cikin rayuwa suka barshi a wulaqance ba. Lalle

maraya shine wanda zaka iske yana da ballagazar uwa

ko uba wanda bashi da loqacin kula da shi.

Ya Ubangiji ka da ka bar wani zunubi namu a wannan guri ba tare da

ka gafartashi ba, haka nan duk wata damuwa face ka yaye ta, haka nan

mai bashi face ka bashi abin biya, haka nan kada ka bar wata buqata

tamu wacce a cikinta akwai yardarka mu kuma muna da maslaha a

cikinta face ka biya mana ita ka kuma sauqaqe ta ya Ubangijin

halittu.

Yaku bayin Allah! “Haqiqa Allah yana yin umarni da

adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana

hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’a, yana

yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90)

1 Abdur Razzaq as-san’ani

21

3

Aure Shine Tsarin Da Allah Ya Yarda Da Shi.

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya halalta aure ya haramta zina, ya

kuma sharxantawa musulmi aure a matsayin hanyar mu’amala

tsakanin namiji da mace, ya kuma sanya aure ya zamo xaya daga

cikin sunnonin Allah a halittunsa da tsarinsa. ya kuma sanya shi gama

gari ta yadda ba wani jinsi da zai kauce daga gare shi a xaukacin

halittun da suka haxa da ta bil-adama da dabbobi da duniyar tsirrai,

Allah mafi xaukaka mai faxa yana cewa: “kuma daga komai mun halitta nau’i biyu wata qila zaku yi tunani” (Dhari’at: 49) Kamar

yadda shine wanda ya sanya aure ya zamo tsarin da Allah ya zava don

hayayyafa da yaxuwa da xorewar rayuwa, bayan ya yiwa kowanne

daga cikin ma’aurata tanadin gudunmawar da zai bayar wajen cimma

manufar auren, Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Yaku mutane lalle mu mun halicce ku daga namiji da

mace, kuma muka sanya ku da ga qabiloli, domin kusan

juna. lalle mafificin daraja a wurin Allah, (shine) wanda

shine mafificinku a taqawa. Lalle ne Allah Masani ne

Mai qididdigewa” (Hujrat: 13) a wani wurin kuma yana

cewa: “ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa,

wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga

gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu

yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda

kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle

ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (Nisa’i:1)

Ina kuma shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai

yake bashi da abokin tarayya kuma ina shedawa Muhammad bawansa

22

ne kuma manzonsa ne tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi

wanda yake cewa:

Yaku taron matasa duk wanda zai iya xaukar xawainiya a

cikinku to yayi aure domin shine mafi bayarda kariya ga

runtse ido mafi bayar da garkuwa ga farji, wanda kuwa

ba zai iya ba to ya lazimci azumi domin shi garkuwa ne

gareshi” Imam Ahmad da abu Dawud suka ruwaito.

Wanda kuma yace:

Idan bawa yayi aure to rabin addininsa ya cika sai yaji

tsoron Allah a sauran rabin” Baihaqi da Hakim suka

ruwaito. Shine kuma yace: “duk wanda ke da wadatar yin

aure bai yi ba to baya tare da ni1

Allah yayi daxin tsira a gare shi da alayensa da sahabbansa, da

waxanda suka biyo bayansu da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka,

Ya ku mutane! Ku sani cewa Allah bai yi nufin barin xan adam yayi

rayuwa irinta sauran nau’oin halittu ta hanyar barin sha’awarsa

sauqaqaqqiya ba tare da linzami ba ta yadda mu’amala tsakanin mace

da namiji za ta zamo cikin hayaniya ba. A maimakon haka sai ya

sanya masa tsarin da ya dace da shugabanci da aka xora masa. Haka

nan ya sanya haxuwar namiji da mace haxuwa ce ta karamci da aka

gina ta bisa yardarsu da yardar waliyyansu, aka kuma xora ta akan

nema da amincewa a matsayin alamomi guda biyu na amincewa tare

da shedawar shedu akan cewa kowannensu ya zama halal ga abokin

zamansa.

To da hakane kuma musulunci ya sanyawa sha’awa tafarki

amintacce ya kuma tsare zuri’a daga vacewa, ya kare mace daga

1 tabarani

23

kasancewarta abar kwaxayin kowanne mavarnaci, ya kuma sanya

tubalin zamantakewar iyali a kewaye da xabi’ar qauna ta uwa, wacce

tausayin uba ya bata kulawa ta yadda za ta samar da shuka mai

yabanya da matuqar ban sha’awa. Ba shakka irin wannan tsari shine

Allah ya yarda da shi ya kuma xora musulunci akansa ya kuma rushe

duk wani tsari da ya savawa wannan. Haka kuma aure shine hanya

mafi kyau ta haihuwar ‘ya’ya da yawaita zuri’a da xorewar rayuwa da

ba zuciya kariya da kulawa matuqa. Haka nan, aure ibada ne don haka

ya zama wajibi ga duk wanda zai yi aure ya koye shi kamar yadda

yake koyar sauran nauo’i na ibada. Babban malamin wannanal’umma

wato Abdullah bin abbas Allah ya yarda da shi yana cewa: “ibadar mai yawan ibada ba ta cika har sai yayi aure”1

Yaku bayin Allah! haqiqa neman izinin aure na daga cikin

matakan farko na aure, domin kuwa Allah ya shar’anta shi kafin qulla

alaqar aure, domin kowanne daga cikin ma’aurata ya san abokin

zamansa na nan gaba, haka nan ya sami damar fuskantar auren bisa

ilimi da basira. Haka nan sharaxi ne ga mace ta kasance ta kuvuta

daga dukkan abubuwan da za su sa shari’a ta hana aurensa da ita a

wannan loqaci. Ya kuma kasance babu wanda ya rigashi ta hanyar

neman aure wandashari’a ta amince da shi, kamar yadda aka haramta

neman auren mai yiwa waninsa idda, ba banbanci tsakanin iddar

mutuwa da saki, haka nan ba banbanci tsakanin saki mai kome da

marar kome. Kamar yadda babu laifi ayi jirwaye mai kamar wanka

wato ya halalta ayi jirwaye da bayar da kyauta ga mai idda idan har

sakin ba mai kome ba ne.

Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

kuma babu laifi akan ku a cikin abin da kuka gitta da shi

daga neman auren mata ko kuwa kuka voye a cikin

zukatanku Allah ya san cewa lalle ne ku za ku ambata

musu (shi). kuma amma kada ku yiwa juna alqawari da

shi a voye, face dai ku faxi magana sananniya. kuma

1 Musnad Abi Shaibah

24

kada ku qulla niyyar xaurin aure sai littafin (idda) ya kai

ga ajalinsa. kuma ku sani cewa lalle ne, Allah yana sanin

abin da ke cikin zukatanku, saboda haka ku ji tsoronsa.

kuma ku sani cewa Allah mai gafara ne mai haquri.

(Baqara: 235).

Ya ku bayin Allah ku sani cewa, Allah cikin hikimarsa yayi izini ga

mai neman aure ya kalli wacce yake neman aurenta, domin auren ya

zama an yi shi ta fuskar da za’a sami cikakkiyar nutsuwa da

amincewa.

An karvo daga Mughira xan Shu’ubah cewa ya nemi auren

wata mata, sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare

shi yace da shi: “ko ka kallle ta? Sai yace: a’a, sai yace ka kalle ta domin yin hakan zai qara cusa shaquwa a tsakaninku” An-Nisa’i da

Tirmidhi da Ibn Majah suka ruwaito ya kuma ce hadisi ne mai kyau.

Haka nan an karvo daga Jabir xan Abdullah Allah ya yarda da

shi yace: manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi

yace: “idan xayanku zai nemi auren wata mace to in har ya sami ikon ya kalli abinda zai ja hankalinsa to ya aikata hakan”1

.

Abin da aka halalta a gani daga wacce ake neman aurenta

shine fuska da tafukan hannu kawai, ana kallon fuska ne don sanin

haske da kyau, tafukan hannu kuwa don sanin laushin jiki da

kaushinsa. Kuma baya halalta ga mai neman aure ya nufi jin xaxi da

kallon wacce yake neman aurenta in har kuwa yayi hakan to ya aikata

zunubi.

Kamar yadda ya halalta mai neman aure ya wakiltawani ko

namiji ko mace ya dubo masa fuskar wacce zai aura da tafukanta,

haka nan kuma ya halalta wacce aka wakilta mace ta ga abin da ya

wuce fuska da tafukan hannu. A cikin hadisin anas manzon Allah tsira

da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya aika ummu salma ta gano

1 Almustadrak

25

masa wata baiwa sai yace: “ki shinshina kumatunta ki kuma dubo dugaduganta”1

.

Haka nan ya zama wajibi ga mai neman auren idan ya nemi

auren mace amma ba ta burgeshi ba ya kame bakinsa, kada ya faxi

wani abu daga cikin abubuwan da za su cutar da ita in an ambace su

domin tana iya yiwuwa abin da bai burgeshi ba, ya burge waninsa.

Haka nan wannan hukuncin baya tsaya ne kawai ga namiji ba, ita ma

mace zata duba mai neman aurenta domin kuwa ita ma akwai abin da

zai iya burgeta na sa kamar yadda shi ma yake da wanda zai burgeshi

na ta.

Kamar yadda kevancewa da wacce ake neman aurenta bai

halalta ba, domin zata cigaba da kasancewa haramun ga mai neman

aurenta har sai an xaura musu aure, domin kuwa ba za’a iya

amincewa kevancewarsu ba, gudun suna iya aukawa cikin abin da

Allah ya hana. Sai dai idan akwai muharrami ana iya kevewa da ita

don ba ta yadda za ayi a sami savon Allah a loqacin da yake nan. An

karvo daga Jabir Allah ya yarda da shi, manzon Allah tsira da amincin

Allah su tabbata a gare shi yace: “duk wanda yayi imani da Allah da ranar qarshe to kada ya sake ya kevance da wata mace ba tare da muharraminta ba, in ko har yayi hakan shexan ne zai zamo na ukunsu”2

. An kuma karvo daga Abdullah xan Umar Allah ya yarda da

shi yace: manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare shi

yace: “duniya jin xaxi ce kuma mafi alherin jin xaxin ta mace ta gari”

Muslim ne ya ruwaito, an kuma karvo wani hadisi daga gare shi

“duniya jin xaxi ce, kuma daga cikin mafi alherin jin xaxinta macen da za ta taimaki mijinta dangane da lahira” Zain ya ambace shi.

An kuma karvo daga Abu Umamatu Allah ya yarda da shi, daga

annanbi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “mumini ba zai amfana da wani abu ba bayan jin tsoron Allah Maxaukakin Sarki da wani abu mafi alheri a gare shi kamar mace ta gari ba, wacce idan

1 Albaihaqi da Ahmad da Hakim

2 Imam Ahmad da Bukhari

26

baya nan sai ta riqe masa amanar kanta da dukiyarsa” Ibn Majah ya

ruwaito.

Ina rokon Allah ya yi mana albarka ni da ku, ya kuma amfane

ni ya amfane ku da fahimtar alqur’ani mai girama, ya kuma amfane

mu gaba xaya da abin da ke cikinsa na ayoyi da ambato na hikima

27

Huxuba Ta Biyu:

Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa muna yaba masa muna

neman gafararsa, muna neman taimakonsa, muna tuba a gareshi, muna

dogara da shi, muna kuma neman tsarin Allah daga sharrin

kawunanmu, da miyagun aiyukanmu, muna kuma shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah kuma Muhammad bawansa ne kuma

manzonsa, ya riqe amana, yayi nasiha ga al’umma, kuma yace: “mafi alheri a cikinku shine mafi alheri a wurin iyalansa kuma ni ne mafi alherin ku ga iyalina” Allah yayi xaxin tsira a gare shi da aminci mai

yawa.

Bayan haka:

Ya ku mutane ina yiwa kaina wasiyya da ku da jin tsoron Allah

a mu’amalarmu ga matanmu da iyalanmu haka nan a wajen

mu’amalarmu da sauran hulxoxinmu da su, a matsayinmu na bil-

adama. Ku sani ya zama wajibi a kanmu mu ciyar da su mu tufatar da

su, kamar yadda aka sani a shari’ance Allah Maxaukakin Sarki yana

cewa:

Kuma ciyar da su da tufatar da su yana kan wanda aka

haifar masa da alheri, ba a qallafawa rai face iyawarsa.

Ba’a cutar da uwa game da xanta, kuma ba’a cutar da

uba game da xansa, kuma akan magaji akwai misalin

wancan. to idan su kayi nufin yaye akan yardatayya daga

garesu, da shawartar juna, to babu laifi akansu. kuma

idan kun yi nufin bayar da xiyanku shayarwa to babu

laifi akanku, idan kun miqa abin da ku ka zo da shi bisa

al’ada, kuma ku bi Allah da taqawa, kuma ku sani cewa

lalle Allah daga abin da kuke aikatawa shi mai gani ne.

(Baqara: 233).

28

A wani wurin kuma Allah Maxaukakin Sarki yace:

Ku zaunar da su daga inda kuka zauna da gwargwadon

samunku, kuma kada ku cuce su domin ku quntata a

kansu kuma idan sun kasance ma’abota ciki ku ciyar da

su har su haife cikinsu. sannnan idan sun shayar da mama

saboda ku sai ku ba su tsadodinsu. kuma ku yi shawara a

tsakaninku bisa abin da aka sani. kuma idan kun nuna

talauci yo wata mace zata shayar da mama saboda shi

(mijin) (Xalaq: 6).

Ya ku bayin Allah lalle yaqi da zuciya da horar da ita akan kulawa

jajircewa wajen sauke nauyi da haqqoqin iyali da haquri da

halayensu, da jurewa cutarwarsu, da qoqarin gyara su, da shiryar da

su bisa hanyar addini, da qoqarin neman halal dominsu, da tarbiyyar

da kowanne mutum zai ba ‘ya’yansa duk abubuwa ne da suka zamo

tilas a kawunanku! Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a

gare shi yana cewa:

Rana xaya ta shugaba mai adalci tafi daraja wurin Allah

fiye da shekaru saba’in1.

Don haka wahalhalun kula da iyali da ‘ya’ya dai-dai suke da na jihadi

don xaukaka kalmar Allah Maxaukakin Sarki, saboda haka ne Bishir

yake cewa:

Ahmad bin Hambal ya fini abubuwa guda uku: yana

neman halal don kansa da kuma don waninsa” kuma

manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata gare shi

yace: “abinda mutum zai ciyar da iyalinsa da shi sadaka

ne2

1 Tabarani

2 Musnad Shihab al qada’i

29

Kuma haqiqa akan bawa mutum lada bisa lomar da yakai bakin

matarsa.

Ina roqon Allah ya yi mana albarka, ni da ku baki xaya wajen

fahimtar Alqur’ani mai girma ya kuma amfane mu ni da ku da abin da

yake cikinsa na ayoyi da Ambato mai hikima, ya kuma karva mana ni

da ku domin shi mai ji ne kuma masani. Ina roqon Allah ya gafarta

min, ya gafarta muku.

Ku yi salati da salllama ga shugabanmu annabi Muhammad,

wanda shine mafi alherinmu ga iyalinsa, da alayensa da sahabbansa

masu yin aiki da ikhlasi, da waxanda suka biyosu da kyautatawa har

zuwa ranar sakamako. Ya Allah ka yarda da shugabanmu Abubakar

da Umar da Usman da Ali da sauran sahabbai baki xaya.Ya Allah

kada ka bar wani zunubi namu a wannan wuri da muke face ka

gafartashi, haka nan wani baqin ciki face ka yaye mana shi, haka nan

mara lafiya face ka warkar da shi, haka nan mai bashi face ka hore

masa abin biya, haka nan wanda yake cikin wata damuwa face ka

fitar dashi, hakan nan duk wata buqata daga cikin buqatu na duniya da

lahira wacce a cikinta akwai masalaharmu kuma akwai yardaka face

ka biya mana ita, ka sauqaqeta, ya Ubangijin talikai.

Ya ku bayin Allah! “Haqiqa Allah yana yin umarni da

adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana

hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’a, yana

yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90)

Ku tuna Allah sai ya tuna ku, ku kuma yi masa godiya bisa ga

ni’imominsa sai ya qara muku, lalle ambaton Allah shine mafi girma.

30

4

Waxansu Daga Haqqoqin Miji Da Mata A Musulunci

Saki da riqo da abin kirki ko saki da kyautatawa.

Godiya ta tabbata ga wanda ya sanya aure a shari’ah yarjejiniya ce

tsakanin namiji da mace, wanda ta hanyarsa ne ya halaltawa kowanne

xaya daga cikinsu ya ji daxi da xayan, kamar yadda kuma ya

bayyanawa kowanne daga cikinsu abin da yake da shi na haqqoqi da

waxanda aka xora masa na wajibin al’umma wanda kuma manufarsa

ita ce tsare jinsin bil adama.

Haka nan ya shar’anta saki idan cigaba da rayuwar aure ta

gagara bisa waxansu dalilai.

Allah Maxaukakin Sarki yace:

Ya kai annabi idan kun saki mata sai, sai ku sake su ga

iddarsu, kuma ku qididdige iddar. Kuma ku bi Allah

Ubangijin ku da taqawa. Kada ku fitar da su daga

gidajensu kuma kada su fita face suna zuwa da wata

alfasha bayyananna, kuma waxancan iyakokin Allah ne,

kuma wanda ya qetare iyakokin Allah to lalle ya zalunci

kansa. Baka sani ba xammanin Allah zai fitar da wani

al’amari a bayan haka. Sannan idan sun isa ajalinsu (na

idda) sai ku riqe su da abin da aka sani ko ku rabu da su

da abin da aka sani (Talaq 1-2)

Ina kuma shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaxai

yake ba shi da abokin tarayya, mulki da godiya duk nasa ne, kuma

makoma zuwa gare shi take. Ina kuma shedawa lalle shugabanmu

31

Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, wanda shine ya

xabi’antu da mafi kyawun halaye wanda kuma shine yake cewa:

A cikin abubuwan da Allah ya halalta babu wanda ya fi

yin fushi da shi kamar saki”1 wato duk da cewa an

ambace shi da halal amma abin qi ne wanda ba ya so,

wanda hakan kaxai ta isa ta sa a nisance shi.

Bayan haka, yaku mutane haqiqa ina yi muku wasiyya da ni kaina da

jin tsoron Allah. “Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (an-Nisa’i:1)

Ya ku ‘yan uwa na maza da mata ku sani cewa Allah

Maxaukakin Sarki ya shar’anta saki don tausayawa da tausasawa ga

kowanne daga cikin ma’aurata, ta yadda aka ba su dama su warware

abin da suka qulla a tsakaninsu bisa yarda da amincewarsu, da nufin

samun kwanciyar hankali a cikinsa, to amma a maimakon hakan sai

ya jawo musu wahalhalu da rashin kwanciyar hankali ko takura da

rashin samun damar sauke nauyin da Allah ya xora musu. Kamar

yadda ake iya cewa saki maslaha ce ta miji domin kuwa shi aka bawa

wuqa da nama in har ya fahimci cewa matarsa tana da wani abin suka

ko dai na halitta ko na hali, wanda hakan zai jawo mutum ya yi

tambaya da cewa to yaya al’amarin zai kasance in kuma shi mijin ne

yake da wannan tawaya? Ko kuma a lokacin da matar da tsani zama

da shi saboda muninsa na halitta ko na xabi’a? Amsar wannan

tambaya itace, ba shakka Allah Maxaukakin Sarki ya bawa mace ita

ma haqqin neman a warware aurenta da mijinta (khul’i) ta yadda za ta

fanshi kanta ta hanyar ba mijin wani abu don mayar masa da abin da

ya kashe mata don ya sawwaqe mata. Allah maxaukakiin sarki yana

cewa: “idan kun ( danginsu) ji tsoron ba za su tsayar da iyakokin

1 Abu Dawud da Hakim da Baihaki

32

Allah ba, to babu laifi akansu a cikin abin da ta yi fansa da shi” (Baqara: 229)

Haka nan ya zo a cikin hadisi ingantacce cewa matar Thabit

xan Qais tace da manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a

gare shi “miji na ba na zarginsa ta vangaren halayyarsa ko addininsa sai ni ba na son kafirci bayan musulunci” a wata riwayar kuma “ni dai ba zan iya zama da shi ba ” sai manzon Allah tsira da amincin Allah

su tabbata a gare shi yace: “ shin ko za ki iya mayar masa da gonarsa?” sai tace qwarai kuwa. Sai manzon Allah tsira da amincin

Allah su tabbata a gare shi yace: “karvi gonar ka kuma sake ta”

Bukhari ya ruwaito shi. Daga wannan bayani da ya gabata za mu

fahimci cewa saki abu da Allah Maxaukakin Sarki ya shar’anta a

lokacin da ake ganin cewa ba ta yadda za’a yi a sami haxin kai

tsakanin ma’aurata, aka kuma sami matsananciyar buqata yin hakan to

sai miji ya aiwatar da shi bayan an xau tsawon lokaci na haquri tare

da tunanin abin da zai iya biyo bayan sakin, tare da jimamin aiwatar

da shi a lokacin da dalilan da za su jawo yin sakin suka qi gushewa.

Haka nan Allah Maxaukakin Sarki ba ya shar’anta saki ba ne don

mutane su yi amfani da shi ta mummunr hanya, ko su xauke shi a

matsayin abin rantsuwa a wuraren kasuwancin mutane da sauran

abubuwa na savani da ke faruwa a tsakaninsu, domin kuwa ya zo a

hadisi ingantacce “duk wanda zai yi rantsuwa to ya rantse da Allah1” wannan na nuna cewa yin amfani da saki wajen rantsuwa haramun ne,

kamar yadda ake iya ladabtar da wanda ya aikata hakan. Sannan Allah

Maxaukakin Sarki ya sanya saki ya zamo sau biyu waxanda in har aka

sake samun saki bayansu to babu sauran halaccin kome sai bayan ta yi

wani auren mijin ya tare da ita. To da wannan ne aka yiwa mutane

linzami musamman a lokutan da zukatansu suka harzuqa ko kuma

suka fusata, kamar yadda aka siffanta a cikin bayanin sharuxxan saki

na sunna wanda shi kaxai ne shari’a ta amince da shi, wato saki

wanda yayi dai-dai da sunnah savanin na bidi’a wanda ko dai ya

kasance haramun ko makruhi. Saki na Sunnah shine wanda – in har

1 Ahmad da Imam Bukhari da Muslim

33

akwai buqatar yin hakan – mutum zai saki matarsa saki xaya a lokacin

da take da tsarkin jinin hailar da bai sadu da ita bayansa ba, bai kuma

qara wani sakin akansa ba har zuwa lokacin da za ta kammala idda.

Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “Ya kai annabi idan kun saki mata sai, sai ku sake su ga iddarsu, kuma ku qididdige iddar. Kuma ku bi Allah Ubangijin ku da taqawa. Kada ku fitar da su daga gidajensu kuma kada su fita face suna zuwa da wata alfasha bayyananna, kuma waxancan iyakokin Allah ne, kuma wanda ya qetare iyakokin Allah to lalle ya zalunci kansa. Baka sani ba xammanin Allah zai fitar da wani al’amari a bayan haka. Sannan idan sun isa ajalinsu (na idda) sai ku riqe su da abin da aka sani ko ku rabu da su da abin da aka sani…”

(Talaq 1-2)

Ba shakka wannan aya na nuna cewa sakin da aka bayar da izini

a yi shi shine saki xaya wanda bayan aukuwarsa za’a sami damar

kome a cikin idda. saboda da faxin Allah Maxaukain Sarki: “Kada ku fitar da su daga gidajensu kuma kada su fita face suna zuwa da wata alfasha bayyananna, kuma waxancan iyakokin Allah ne, kuma wanda ya qetare iyakokin Allah to lalle ya zalunci kansa. Baka sani ba xammanin Allah zai fitar da wani al’amari a bayan haka. sannan idan sun isa ajalinsu (na idda) sai ku riqe su da abin da aka sani ko ku rabu da su da abin da aka sani…” (Talaq 2).

Haka nan waxannan ayoyi na yin nuni da cewa, saki wanda

shari’ah ta amince da shi shine wanda aka yi shi a lokacin da mace

take cikin tsarki domin kuwa Allah Maxaukakin Sarki cewa ya yi “ ku sake su ga iddarsu” abin da ake nufi ga iddarsu shine a lokacin da

suke tunkarar iddarsu. Kamar yadda aka hana yin saki cikin jinin haila

domin kuwa hakan zai tsawaitawa mace iddarta ya kuma cutar da ita.

Haka nan kuma an hana miji ya saki matarsa a cikin tsarkin da ya sadu

da ita a cikinsa, domin idan ya yi hakan zai jefa ta cikin shakkun cewa

tana da ciki ko ba ta da shi a sanadiyyar waccan saduwa da ya yi da

ita, ta kuma rasa gane wacce irin idda za ta yi shin ta mai ciki ce da za

ta qarshe da zarar ta haihu ko kuwa ta mai lissafin jini ce?.

Dukkan nau’oin sakin na bidi’ah makaruhi ne banda sakin mace

tana cikin jinin haila wanda shi haramun ne, da shi da wanda aka yi

34

saki fiye da xaya a lokaci guda da wanda aka yi shi a cikin tsarkin da

aka sadu da mace a cikinsa.

Ya ku musulumai! Haqiqa Allah ya yi muku umarni da ku

girmama mata. Haka nan kuma zavavven Allah tsira da amincin Allah

su tabbata a gare shi yana cewa “inayi muku wasiyya da ku riqe mata da kyautatawa donin mace an halicce ta ne daga qashin haqarqari karkatacce, kuma mafi karkacewa daga cikin qashin haqarqari shine na samansu, in ka yi qoqarin miqar da shi sai ka karya shi, in kuma ka barshi a haka ba zai gushe yana kantare ba” Bukhari ya ruwaito shi.

Allah Maxaukain Sarki Yana cewa: “kuma Allah ya sanya muku matan aure daga kawunanku, kuma ya sanya muku daga matan aurenku xiya da jikoki, kuma ya azurta ku da abubuwa daxaxa. Shin fa da qarya suke yin imani, kuma da ni’imar Allah su, suke kafirta? (Nahl: 72)

Ya Allah kada ka bar wani zunubi namu a wanna wuri da muke

face ka gafartashi, haka nan wani baqinciki face ka yaye mana shi,

haka nan wanda ya bar iyalinsa face ka mayar da shi, haka nan mara

lafiya face ka warkar da shi, haka nan mai bashi face ka hore masa

abin biya, haka nan wanda yake cikin wata damuwa face ka fitar

dashi, haka nan duk wata buqata daga cikin buqatu na duniya da

lahira wacce a cikinta akwai maslahar mu face ka biya mana ita, ka

sauqaqeta ya Ubangijin talikai. Yaku bayin Allah! “haqiqa Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin ku kuna tunawa” Nahl: 90). Ku tuna Allah sai ya

tuna ku, kuma ku yi masa godiya bisa ga ni’imominsa sai ya qara

muku.

35

Huxuba ta biyu

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya bayyanawa bayinsa na gari

hanya mafi dacewa, ya horar da su bisa ladubba mafifita, ya kuma

yiwa waxanda ya so dace da yin aure dominsa, shine Ma’abocin

sunaye da siffofi mxaukaka. Ina shedawa babu abin bautawa da

gaskiya sai Allah kuma ina shedawa cewa Annabi Muhammad

bawansa ne kuma manzonsa ne wanda shine mai cewa:

Abubuwa guda uku yinsu da wasa da gaske ne kuma yinsu da gaske; gaske ne, aure da saki da kome”1

wannan

kuma shine abin da ma’abota ilimi suke aiki da shi. Ya

ku bayin Allah! ku sani cewa, kome shine maida auren

mace wacce aka saki da mijinta zai yi a cikin iddarta ba

tare da sake sabon aure ko waliyyi ko sadaki ba. Haka

nan haqqin da miji yake da shi na yin kome baya faxuwa

daga kansa ko kuwa shine da kansa ya sarayar da shi,

domin haqqi ne da Allah ya xamfara shi da saki ya kuma

damqa shi a hannun miji don haka babu wanda yake da

ikon yin wurgi da shi, sannan kuma Allah ya sanya kome

ne don bayar da damar a yi gyara a kuma magance

matsaloli da qarin samun damar gwada yiwuwar a zauna

tare. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “kuma mazajen aurensu sune mafiya haqqi ga mayar da su a cikin wancan, idan sun yi nufin gyarawa. Kuma su matan suna da kamar abin da ke kansu, yadda aka sani. Kuma maza suna da wata daraja akansu (su matan). Kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima” (Baqara: 228). Kamar yadda

kuma an halalta kome matuqar tana cikin idda ko da

kuwa xaya daga cikin ma’auratan yana cikin haramin

aikin hajji ko umra haka nan ko da xayansu bashi da

lafiya irin rashin lafiyar da ka iya yin barazana ga

1 Abu Dawud da Tirmidhi suka ruwaito

36

rayuwarsa. Waxannan abubuwa sune banbance banbance

da ke tsakanin aure da kome, shi kome ba sabon xaurin

aure ba ne, a madadin haka kome jaddada aure ne wanda

da ma tun can farko akwai shi.

Kome yana faruwa ta xaya daga cikin waxannan hanyoyin, ko dai

miji yace: “na dawo da matata qarqashin aure na” ko ta hanyar amfani

da wani lafazi da ke nuna yinsa ko da kuwa mijn bai yi niyya ba ya

faxi hakan ne ta hanyar wasa. Domin kuwa manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi ya bayyana cewa kome da wasa

dai-dai yake da yinsa da gaske kamar yadda ya gabata. Waxannan

abubuwa dukkansu suna faruwa ne in an yi la’akari da hukunci na

zahiri, dangane kuwa da ainihin abin da ke cikin zuciyar xan adam shi

da Allah kowanne aiki yana buqatar niyya, in kuwa aka rasa ta to aiki

ya vaci kamar yadda ita kuma niyya ita kaxai ba ta wadatarwa har sai

an haxa ta da aiki wato furtawa ba.

Abu na biyu shine, miji ya cigaba da ma’amala ta aure da

matarsa da niyyar kome wanda kuma yin hakan yakan tabbata ne a

lokacin da ya sadu da ita ko ya shafa ta ko ya sumbance ta. Ya ku

bayin Allah! Ku yiwa annabin rahama salati domin lalle Allah

Maxaukakin Sarki ya yi muku umarni da yin haka a inda yake cewa:

“Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi. Ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56).

Ya Allah, ka yi tsira da aminci ga shugabanmuAnnabi

Muhammad, da alayensu da sahabbansa baki xaya, ya Allah ka qara

yarda da shugabanninmu, Abubakar da Umar da Usman da Ali da

sauran sahabbai baki xaya. “Lalle Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90). Ina roqon Allah ya yi mana albarka, ni da ku baki xaya

wajen fahimtar Alqur’ani mai girma ya kuma amfane mu ni da ku da

abin da yake cikinsa na ayoyi da Ambato mai hikima, ya kuma karva

37

mana ni da ku domin shi mai ji ne kuma masani. Ina roqon Allah ya

gafarta min, ya gafarta muku.

38

5

Waliyyan Aure

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya shar’anta hukunce hukunce ya

kuma rarrabe tsakanin halal da haram, ya yi umarni da aikata

nagartattun aiyuka ya kuma yi hani ga aikata munana, ya kuma

girmama ma’abota hankali da tunani ta hanyar shiriyarsu bisa

musulunci. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Kuma akwai daga ayoyinsa ya halitta muku matan aure

daga kanku domin ku natsu zuwa gareta, kuma ya sanya

soyayya da rahama a tsakaninku. lalle ne daga cikin

wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani (Rum:

21).

Haka nan muna yiwa Allah Maxaukakin Sarki godiya bisa ga abin da

ya shar’anta ya kuma sunnanta na aure. Ina shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya,

wanda shine ya haramta alfasha ta sarari da ta voye, kuma muna

shedawa shugabanmu Annabi Muhammad bawansa ne kuma

manzonsa ne wanda shine yake cewa:

“Ba aure sai da waliyyi” yana kuma cewa: “duk matar da

ta yi aure ba tare da iznin waliyyinta ba aurenta vatacce

ne1 ya Allah ka yi daxin tsira a agare shi da alayensa da

sahabbansa.

Bayan haka, ya ku mutane! lalle walicci ga mace a lokacin da za ta yi

aure na xaya daga cikin alamomin girmamata da martaba ta, domin

1 Abu Dawud da Tirmidhi

39

kuwa Allah Maxaukakin Sarki ya sanya mata wanda zai tsaya mata ya

kuma kare ta ya kuma tsare mata haqqoqinta tun a wurin xaurin aure,

domin kuwa da ace za ta xauki nauyin abubuwa ita da kanta da sai

kunya ta jawo ta sarayar da haqqoqinta da yawa, na wannan vangare

da ya shafi kayan da ya kamata a yi mata yayin xaurin aure. A xaya

vangaren kuwa wanda shine mafi mahimmanci wanda shine al’amarin

zavar miji mai addini, wanda ya dace wanda zai kwantar mata da

hankali, mai hanakali wanda zai ba ta haqqoqinta, a kowanne daga

cikin waxannan vangarorin waliyyi ya fi ta canacanta domin kuwa a

mafi yawancin lokuta ya fi ta gogayya, kamar yadda zai fi ta hangen

nesa da fahimtar haqiqanin al’amura. Kamar yadda an sa sharaxin

cewa duk wanda zai yiwa mace walicci to ya kasance namiji. Manzon

Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “mace ba ta aurar da mace, haka nan mace ba ta aurar da kanta, mazinaciya itace ta ke aurar da kanta”1

haka nan kuma tilas ne ya kasance baligi mai

hankali kuma ‘yantacce. Don haka walicci yaro baya inganta haka nan

wanda aka tilastawa ko mahaukaci ko bugagge ko kwarkwar. Kamar

yadda an sharxanta cewa ya zamo musulmi don haka waliccin kafiri

ba ya inganta ga ‘yar sa ko ‘yar uwarsa musulma, kamar yadda

waliyyi tilas ne ya kasance baya cikin haramin aikin hajji ko umra,

domin ya zo a hadisi ingantacce “wanda ya yi haramar hajji ko umra ba zai aura ba kuma ba zai aurar ba”2 Idan muka ce Alwali sharaxi ne wajen xaurin aure, to waye ya

cancanta a fara gabatarwa?

Wanda yafi dacewa da ya zamo Alwalin mace shine; mafi kusanci a

gareta ta vangaren mahaifinta, saboda haka Uba yafi cancanta akan

kaka, shi kuma kaka yafi cancanta akan ‘yan uwanta, ‘yan uwa

shaqiqai sunfi ‘yan uwa ta wurin uba cancanta, ‘yan uwa na uba kuma

sunfi Baffanu cancanta, wasu malamai sunce kawunai suma sunfi

baffanu cancanta. 1 Subulussalam juz’I na uku shafi 127 da sunan ibn majah

2 Muwatta malik, Abu Dawud da Muslim

40

Amma anyi savani kan waliccin xa, shin zai zamo waliyin

mahaifiyarshi ko a’a? Imam Shafi’i yace xa bashi da haqqin walicci

akan mahaifiyarshi; domin ba’a dangantashi gareta, ana danganta xa

ne ga mahaifinshi, amma sauran malaman fiqihu sunce yanada haqqin

waliccin mahaifiyarshi, har ma wasu sun gabatar dashi akan Uba.

Waliyyi ya kasu kashi biyu; wato wanda ke da haqqin yin dole da

wanda ba shi haqqin yin dole, waliyyi mai haqqin yin dole shine

wanda ke da damar aurar da ‘ya mace wacce take hannunsa ba tare da

izininta ba, ko da kuwa ga makaho ne, kuma ko da sadaki qasa da na

tsararrakinta, matuqar dai bai tabbata cewa ya yi hakan ne don ya

cutar da ita ba, alal misali ya aurar da ita ga fasiqi ko mai cutar albaras

ko kuturu ko mahaukaci ko dandaqaqqe. A waxannan halaye da aka

ambata ba shi da ikon yin dole saboda abin da ya zo a cikin hadisi:

“ba cutaba cutarwa” waliyyi mai haqqin yin dole ya haxa da mahaifi,

ko wanda ya yi wasiyya ya riqe ‘yarsa ko wanda mutumin da aka

barwa wasiyya ya yi wasiyyar ya kula da ita. Mahaifi yana da ‘yancin

yiwa ‘yarsa auren dole ko da kuwa ba’a sami amincewarta ba in ta

kasance budurwa ko qarama. Ya zo a cikin hadisi daga annabi tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “bazawara ta fi cancanta (ta yi zavi) da kanta fiye da na waliyyinta, ita kuwa budurwa sai a nemi izininta, kuma alamar izinin na ta shine shirunta” 1. wannan hadisi na

nuna cewa, hukuncin budurwa ya banabanta da na bazawara, a lokacin

da bazawa ta fi canacanta da ta zavawa kanta miji ita kuwa budurwa

za’a nemi izininta ne don a ji ko ta amince a ranta, don da ace duk

hukuncinsu iri xaya ne da hadisin bai banbanta su da cewa bazawar ta

fi cancanta da kanta ita kuwa budurwa sai a nemi izininta ba.

Damar da mahaifi yake da ita ta tilastawa ‘yarsa al’amari ne da

aka kafawa waxansu sharuxa, na farko daga cikinsu shine kasancewar

mahaifin bai yanke hukunci cewa yaba ‘yarsa ‘yancin tasarrufi cikin

al’amuranta ba, a misali yace da ita: na hukunta cewa kin kai

hankalin da za ki iya yiwa kanki zavi ko na damqa damar yin zavi a

hannunki. Sannan kuma ya zama tilas ta kasance budurwa ce da ba ta

1 muslim

41

tava yin aure ba, domin in ta tava aure ta xan daxe a gidan mijin

kamar abin da ya kai shekara xaya, to ikon da yake da shi na yi mata

dole ya faxi. Haka nan idan mijin da ya zava mata bai dace da ita ba,

saboda kasancewarsa fasiqi ko yana da wata nakasa to ya zama dole a

ba ta zavi, haka kuma idan yana da wata cuta bayyananniya to uba ba

shi da ikon yi mata dole kasancewar cutuwa abu ne da aka hana auka

mata a kowanne irin yanayi.

Haka nan kuma wanda mahaifi ya yiwa wasiyya da kula da

‘yarsa yana da haqqi irin na mahaifi wajen yiwa ‘yar da aka bar masa

dole a cikin al’amuran da shi kansa mahaifin yake da ‘yanci a cikinsu

to amma da sharaxin sai mahaifin ya amince masa da ya yi dole ko dai

a bayyane ko kuma a dunqule. Dangane da bazawara kuwa wanda aka

yiwa wasiyya yana da hukunci iri xaya ne da na mahaifi ba zai aurar

da it aba har sai ya nemi izininta da yardarta.

Ya yan uwa! Akwai wata masifa da ta vullo a wannan yanki

namu na qasar Hausa ta yadda za ka iske cewa kowanne waliyyi yana

auren dole, kai ciki ma har da makusanta waxanda ba waliyyai bane,

kai a waxansu lokuta ma zaka iske har da mata waxanda sun xauki

kansu a matsayin suna da haqqin yin dole, irin waxannan za ka iske

suna yiwa mace auren dole ne ta hanyar wakilta wani namiji. Ba

shakka, yin hakan abu da yake haramun bai halalta ba. Kuma haqiqa

yin hakan zalunci ne babba kuma wuce gona da iri ne wajen sauke

nauyin da Allah ya xora muku na ‘ya’yanku kuma ka da mu manta

kowanne mutum za’a yi masa hisabi bisa amanar kansa da ta

‘ya’yansa maza da mata da ‘yan aikinsa da ‘yan uwansa da ma dukkan

waxanda suke qarqashin kulawarsa. “Haqiqa kowannenku mai kiwo ne kuma abin tambaya ne dangane da abin da aka ba shi kiwo”.

““dukiyoyinku da xiyanku fitina xai ne. kuma Allah a wurinsa akwai wani sakamako mai giram: ( Taghabun: 15)

Huxuba Ta Biyu

42

Godiya ta tabbata ga Allah a kowanne yanayi, muna kuma neman

tsarinsa daga halaye irin na vatattu, kuma muna roqonsa afuwa da

lafiya da dawwamammiyar kuvuta daga dukkan sharri a dukiyoyinmu

da iyalanmu, muna kuma neman tsarinsa daga fitinar rayuwa da ta

mutuwa da fitinar Dujjal la’ananne da bijirewar mata daga biyayyar

mazajensu.

Muna godewa Allah Maxaukakin Sarki mai girma da xaukaka

bisa ni’imominsa muna fatan Allah ya tsare mana su daga gushewa.

Kuma muna shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi

kaxai yake ba shi da abokin tarayya wanda shine masanin sirri da abin

da yake bayyane, kuma shine wanda halitta da umurni duka suke

hannunsa. Kuma muna shedawa Muhammad bawansa ne kuma

manzonsa ne wanda Allah ya qarfafa da nasara da mu’ujizozi da

alayensa da sahabbansa Allah ya yi daxin tsira a gare su.

Ina roqon Allah ya yi min albarka ni da ku wajen fahimtar

Alqur’ani mai girma ya kuma amfane mu ni da ku da abin da ke

cikinsa na ayoyi da ambato mai hikima, ya kuma karva mana ni da ku

domin shi mai ji ne kuma masani. Allah ya gafarta min ya gafarta

muku. “Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, Ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56) tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi da alayensa da sahabbansa ka yi daxin tsira a gare

su.

Lalle Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa

ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin

qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin

ku kuna tunawa (Nahl: 90). Ina roqon Allah ya gafarta

min ya gafarta muku.

43

6

Yiwa Wacce Aka Saki Kyautar Jin Daxi Da Xaukar Nauyin

Matar Aure.

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya halitta muku mata daga

kawunanku ya kuma sanya qauna a tsakaninku. Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa:

kuma akwai daga ayoyinSa Ya halitta muku matan aure

daga kanku, domin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya

sanya soyayya da rahama a tsakaninku. Lalle a cikin

wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani (Rum:

21)

Ina shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma

Muhammad bawansa kuma manzonsa, wanda yake shine ma’abocin

halaye masu girma, tsira da amincin Allah su tabbata a agre shi da

alayensa da sahabbansa, salati mai yawa.

Bayan haka:

Yaku bayin Allah! lalle Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya

halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi

ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza

da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon

juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya

kasance akanku Mai tsaro ne. (An-Nisa’i:1)

44

Abdullahi xan Umar yana cewa: “duk matar da aka saki tana da haqqi ayi mata kyautar da zata ji xaxi in banda wacce aka saki ba tare da an yanka mata sadaki ba, ba’a kuma kwanta da ita ba”

Daukar nauyin mace:

An karvo daga manzon Allah dangane da matanmu mai ya kamata mu

yi musu me kuma za mu bari? Sai yace “ka zowa gonarka yadda kake so, kuma ciyar da ita matuqar ka ci, ka tufatar da ita idan kayi tufa kada ka muzanta siffarta kar kuma kayi duka” silsilatul ahadith

assahihah.

Ya ku bayin Allah! Lalle ciyarwa wajibi ce akan duk wani miji da

matarsa take yin iddar da za’a iya yin kome domin kuwa matar da

take cikin iddar kome kafin ta kammala hukuncinta iri xaya da na

matar aure a komai in banda saduwa. Haka nan kuma ya zama tilas a

xauki nauyin mai idda matuqar tana da ciki a wannan hukunci babu

banbanci tsakanin iddar saki marar kome da wacce take yin iddar

mutuwa. Haka nan kuma wacce take zaman istibra’i na wani aure

vatacce saboda abin da ya zo a dunqule cikin faxar Allah Maxaukakin

Sarki: “kuma ma’abota cikunna ajalinsu, (shine) cewa su haifi cikinansu” (Talaq: 5). Haka nan an ware wacce aka yi li’ani da ita

wacce ita ba ta da haqqin kulawa kasancewar mijin ya kore cikin nata

ta hanyar li’ani. Kulawa ba ta wajaba ga mace marar ciki wacce take

iddar sakin da ba kome, saboda hadisin Fatimah ‘yar Qais a lokacin da

ta kawo qarar qarancin abin xaukar nauyinta da mijinta ya aiko mata,

sai manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace da

ita “baki da haqqin kulawa”1 da kuma abin da za’a iya fahimta daga

faxar Allah Maxaukakin Sarki “ku zaunar da su daga inda kuka zauna daga gwargwadon samunku. Kuma kada ku cuce su domin ku quntata a kansu. Kuma idan sun kasance ma’abota ciki sai ku ciyar da su har su haife cikinsu” (Talaq: 6) ba shakka wannan ayar ta yi umarni da a

zaunar da waxanda aka saki, umarni na gaba xaya, sannan aka yi

1 Sunan Abi Dawud da Muslim

45

umarni da kulawa da masu ciki kaxai, don haka sai ya bayyana daga

abin da za a iya fahimta daga ayar cewa wacce ba mai ciki ba ta da

haqqin kulawa a iddar saki marar kome. Kamar yadda babu haqqin

kulawa ga mai iddar mutuwa saboda ita kulawa ana bayar da ita ne a

sanadiyyar jin daxi da ita ne wanda ya gushe daga yin mutuwa kamar

yadda zamantakewa ta qare. “kuma kace, “ ku yi aiki saannan Allah zai ga aikinku, da manzonsa da muminai, kuma za a mayar da ku zuwa ga masanin voye da bayyane, sannan ya ba ku labari da abin da kuka kasance kuna aikatawa” (Taubah: 105).

Ya ku bayin Allah! lalle kulawa da mace ya qunshi ciyarwa, da

tufatarwa da wurin kwana da sauransu, haka nan kulawar miji da

matarsa ta kasance wajibi ne saboda tsare kanta da take yi ta kula da

maslaharsa ta kula masa da gidansa da ‘yayansa’ a madadinsa, to

kamar yadda aka xora mata nauyin sauke wannan wajibi to shima sai

aka tilasta masa ya sauke wani nauyin nata na wajibi wato shine samar

da kulawa don ta sami damar sauke nauyin da aka xora mata da zarar

an xaura aure wanda kuma ake fatan ta tsayu da ita ta fuska mai kyau,

ba shakka matarka ce take sanya zuciyarka ta huta daga tunanin

tsaftace gida da kula da shi ta xauke maka nauyin girki da shara da

shimfixa da wanke kwanuka da samar da abubuwan jin daxin rayuwa

sannan kuma ta biya maka buqatar saduwa wanda ba don haka ba da

ba ta yadda za a yi mutum ya rayu a gidansa shi kaxai.

Abu Sulaiman ad-darani yana cewa:

Hidimar mace ta gari ba ta tsaya gare ka a al’amuran

duniya kaxai ba dominkuwa ta kan samar maka da

kwanciyar hankali fuskantar aiyukan lahira, wato ta

hanyar kula masa da gida da biyan buqatar sha’awa.

Yaku bayin Allah! daga abin da muka ambata za a fahimci cewa abin

da ake nufi da xaukar nauyi shine samar da buqatu na tilas waxanda

suka zama tilas ga rayuwar xan adam ta yadda ba za ta buqaci wani

abu a wurin wani na daban ba. waxannan buqatu na tilas na rayuwar

xan adam sune: abinci, tufafi da mazauni. dangane da abinci shine

46

wanda rayuwa ba ta yiwuwa sai da shi kamar yadda shine abin da zai

gina masa jikinsa yakuma tsare rayuwar da aka saki cikin jikin.

Su kuwa tufafi suna bayar da kariya ne ga jiki. Shi kuwa gida

shine inda xan adam zai kwana ya huta ya kuma sami tsaro daga

abubuwan da ka iya cutar da shi. Kulawa ta wajibi ba ta wuce

waxannan abubuwa uku da sauran hidimomi da ke xamfare da su,

haka nan kuma ta haxa da duk wani abu da mace za ta iya cutuwa da

barinsa. Da kuma sauran abubuwa da za a bayyana anan gaba. Ya ku

bayyin Allah bari mu yi bayani akan kowanne xayan daga cikin

waxancan abubuwa da muka lissafa. Na farko shine abinci, abincin da

ya zama wajibi miji ya ciyar da matarsa shine wanda zai iya

gwargwadon ikonsa da wadatarsa da kuma wadatar matar da

matsayinta, da yanayin gari da al’adu da zamantakewa da yanayin

rayuwarsu ta fuskar kasancewa mazauna birni ne su ko na qauye, da

yanayin tafiya ko zaman gida da farashin kayan abincin a lokacin da

ciyarwar ta wajaba wato yanayin araha da na tsada, waxannan

abubuwa kuwa za mu ga cewa dukkansu suna da alaqa da al’ada,

kamar yadda ya zama tilas akan miji ya samar da dukkan abin da ya

zama tilas wajen yin abinci bisa al’ada, kamar yadda akan qarawa mai

shayarwa da sauran abubuwan da za ta qara samun qarfi wajen

shayarwa don ya tallafa mata wajen shayar da xan nata.

Abinda ake nufi da al’ada itace al’adar garinta don haka ya

zama tilas a yi la’akari da halinsu su biyun. Babu banbancin

kasancewarsu sun yi dai-dai da juna a wadata abun ne da yake

bayyane to amma a loqacin da suka sava to ya zama dole a yi amfani

da yanayin tsaka-tsaki na yanayin guda biyu kasancewar kulawar

talaka ba ta kai yawan mawadaciya ba kamar yadda Wannan shine

abin da ake dogaro da shi a mazhaba.

Kulawa a gurinmu ba abu ne da za a iyakance shi ba, kamar

yadda ba yanayin mijin kaxai za a kula da shi ba savanin waxanda

suke faxin hakan, ba shakka za a yi la’akari da yanayin ma’auratan

biyu ne ta yadda za a yanke mata abin da zai wadace ta gwargwadon

abin da akan gani nan matsayinta, da matsayin mijin nata na wadata

da qunci saboda faxin Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “kuma

47

ciyar da su da tufatar da su yana akan wanda aka haifar masa da alheri” .(Baqara 233). Wanda hakan yana nuna kula da yanayinsu

gaba xayansu. Da kuma faxar manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gareshi, ga matar abu Sufyan “ki xauki abin da zai ishe ki da ‘ya’yanki da abin da aka sani”1

Bukahari ya ruwaito shi. sai annnabi

tsira da amincin Allah su tabbbata a gare shi ya xora ta akan abin da

zai ishe ta ba tare da yayi mata iyaka ba, haka nan ita ma kulawa ana

bayar da ita ne gwargwadon abin da zai ishe ta da abin da aka sani.

haka nan ya zama wajini ya wadatar da ita da abin da aka sani.

Ya ku bayin Allah! abu na biyu shine tufatarwa wadda wacce

aka iyakance ta da aqalla sau biyu a shekara xaya loqacin sanyi da

abin da ke biye na loqacin bazara, na biyu kuma loqacin zafi da abin

da ke biye da shi a loqacin damina, kowanne loqaci akwai abin da ya

dace da shi matuqar dai loqutan sun banbanta da juna, in kuwa ansami

cewa loqutan basu da banbanci da juna to xaya ma ta wadatar a

tsawon shekara. Haka nan wasu sunce a kowanne loqacin sanyi da na

zafi za a yi tufafi in har irin tufafin da ake yiwa kowanne loqaci ya

sava da juna ne kawai a shekararsu, wato in har aka sami cewa

shekara ta farko zai wadatar a shekara ta biyu da ta uku, kamar yadda

ya yi a shekara ta farko ko kusa da haka, to za a iya wadatuwa da ita

har zuwa lokacin dsa za ta lalace. wannan hukuncin ya haxa da

lulluvi da mayafi da abin shimfixa da kayan sanyi da zanen lulluva na

lokutan sanyi da na zafi.

Haka nanan lissafa tufatarwa gwargwadon shi kansa kyallen da

nau’insa wajen yawa da qaranci gwargwadon halin mijin da halin

matar da matsayin kowannensu a al’adance. Mafi qarancin sutura

itace wacce za ta suturce jiki da kai ta kuma bayar da kariya daga zafi

da sanyi.

Ku faxaka ya ku ‘yan uwa! Ku yi salati da sallama ga mafi

alherin halittar Allah, Annabi Muhammad kamar yadda Allah da

kansa ya yi masa umarni da yi masa salati da sallama inda yace:

1 Bukhari

48

“Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, Ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56). ya Allah ka yi tsira da aminci a

gare shi da alayensa da sahabbansa kayi aminci garesu mai yawa.

49

Huxuba ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah Mai girma wanda shine girman ikonsa ya

buwaya, alherin sa da kyautatawarsa suke dawwamammu, wanda

shine ya umarci mace da yin lullubi da lazimtar ladubba waxanda

akansu aka gina ginshiqin kowanne gida. Muna shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya,

muna kuma shedawa Muhammad bawansa ne kuma manzonsa wanda

shine yake cewa “Akwai dinarin da zaka kashewa kanka, da wanda za ka kashewa iyalanka, wanda za ka kashewa iyalanka shine ya fi girman lada. " tsira da aminci su tabbata a gare shi da iyalansa da

sahabbansa.

Ya ku bayin Allah! Abu na uku na xawainiyyar iyali shine

wurin kwana, wato ya samar wa matarsa wurin zama wanda ya dace

da ita, ko dai ta hanyar mallaka ko haya ko aro. Haka nan yanayin

mazaunin zai kasance ne wanda ya dace da matsayi da siffa da

darajarta, kamar yadda al’amarin yake wajen ciyarwa gwargwadon

halin miji za ayi la'akari da shi.

Haka nan mace mai girma ma’abociyar matsayi tana da haqqin

kada a zaunar da ita a gidan da za ta zauna tare da ‘yan uwan miji,

waxanda suka haxa har da iyaye, don yin hakan na iya cutar da ita in

an yi la’akari da yanayin da ta taso a ciki, kamar yadda hakan zata iya

kai su ga yi mata shishshigi cikin al’amuranta. To amma idan aka

sharxantawa mace zama da ‘yan uwan miji da makusantansa waxanda

babu aure a tsakanin su da shi, to ba ta da ikon kin amincewa da zama

tare da ‘yan uwa miji a gida xaya sai dai in ta sharxanta hakan ko an

sami wani abu na cuta, idan kuwa ta sharxanta cin gashin kanta daga

yan uwansa ta hanyar rashin zama tare da su a gida xaya tun a wurin

xaurin aure to tana da 'yancin yin hakan.

Hakan nan ko da bata sharxanta hakan ba to amma sai aka

sami cutarta ta hanyar zamanta da su, wato kamar ganin sirrinta ko

sauran al’amuran da ba za ta so a gani ba, ko ma dai suka cutar da ita

50

da wani abin na daban, kamar yawan faxa tsakaninta da su, to tana da

'yancin kin amincewa don kada ta cutu da hakan.

Haka nan xaya daga cikin ma’aurata ba shi da yancin qin

amincewa da zama tare da, 'ya'yan wata ko wani mijin matuqar dai

babu wani mai kula da su na daban, kuma ya/ta san da haka tun kafin

a xaura auren, to ba shi da 'yancin korarsu daga gidansa, amma idan

bai san da hakan kafin daura aure ba, to yana da yancin qin amincewa

ya zauna da su.

Hakan nan wajibi ne akan miji ya xauki xawainiyar nemowa

matarsa magani, wanda hakan ya haxa da samo mata likita, biyan

kuxin magani da abubuwa makamantan haka, a wurin da yawa daga

cikin malamai. Haka nan ya zama wajibi akansa ya biya mai karvar

haihuwar da take karvar haihuwar matarsa, ko da kuwa bayan ya sake

ta ne, hakan nan saye- sayen kayan da ake bayarwa na haihuwa suma

sun wajaba akansa waxanda suka haxa da abinci da abin sha da

alawoyi.

Hakan nan kulawa da kwalliyar mace wacce idan an barta za ta

cutu ta hanyar rashin lafiya ko sukurkucewa, ba tare da banbanci

tsakanin ta yau da kullum da wacce ba ta yau da kullum ba, waxannan

sun haxa da kwalli, da qunshi, da saura, da man da za ta shafa a

jikinta.

Kyautar jin daxi itace duk wani abu da miji zai ba matarsa qari

akan sadaki, don ya rage mata jin raxaxin rabuwar da aka yi da ita, ta

hanyar sakinta, a nan babu banbanci tsakanin wacce aka yi mata saki

mai kome da wacce aka yiwa saki mara kome, kamar yadda kuma

wacce aka saki saki mara kome za a ba ta ne da zarar sakin ya auku,

ita kuwa wacce aka saki saki mai kome za a jira ne har sai ta kammala

iddarta kasancewar ita za ta cigaba da kasancewa a matsayin matar

aure ne har zuwa lokacin da iddarta za ta qare, domin kafin wannan

lokaci tana cikin jiran kome ne ba ta fara jin raxaxin sakin ba tukunna.

Kamar yadda kuma koda wacce aka saki ta mutu ne za a ba

magadanta waccan kyauta ta daxaxawa. Hukuncin kyautar daxaxawa

ga wacce aka saki mustahabbi ne, su kuwa shafi’iyya sun tafi akan

51

cewa wajibi ce kuma dalilan waxanda suke ganin wajibince sun fi

karfi. Allah Maxaukakin Sarki Yana cewa:

kuma waxanda aka saki suna da daxaxawa gwargwadon

hali, wajabci akan masu taqawa (Baqara: 241).

A wani wurin kuma yana cewa:

kuma babu laifi akanku idan kun saki mata, matuqar ba ku

shafe su ba, kuma ba ku yanke musu sadaki ba, ku ba su kyautar

daxaxawa, akan mawadaci gwargwadonsa, kuma akan maquntaci

gwargwadonsa domin daxaxawa da alheri, wajibine akan masu

kyautatawa” (Baqara: 236) haka nan Allah yana cewa: “ya kai annabi

ka cewa matanka, idan kuna nufin rayuwar duniya da qawarta, to ku

zo in yi muku kyautar bankwana in sake ku saki mai kyau” (Ahzab:

28). Haka nan kuma Allah Maxaukakin Sarki yace: “ya ku waxanda

suka yi imani idan kun auri muminai mata, saannan kuka sake su

gabanin ku shafe su, to ba ku da wata idda da za ku lissafa akansu,

kuma ku yi musu kyautar jin daxi, kuma ku sake su saki mai kyau

(Ahzab: 49).

Ya bayin Allah ku ji tsoron Allah, ku kiyaye haqqoqin

matanku, ku yi tsayin daka wajen sauke su, kamar yadda ya kamata,

tare da kiyaye ladubban yin hakan, da kiyaye manufofinsu ba shakka

yin hakan na da lada mai yawa, kamar yadda hakan na qara havaka

alkhairi, da soyayya, tare da qara danqon qauna da tausayi.

Ya Ubangiji ka bamu sanyin idanu daga matanmu da

zuriyarmu, kuma ka sanya mu shugabanni ga masu taqawa. ya Allah

ka karvi tuban masu tuba, ka gafartawa masu zunubi, ka biya bashin

waxanda ake bi bashi, ka warkar da marasa lafiyarmu, da sauran

marasa lafiya musulmai, ya Allah ka gafartawa matattunmu ka gafarta

musu zunubansu, ka karemu ya Ubangijin talikai “Haqiqa Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’a, yana yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90). ina wannan Magana

52

tawa ina nemawa kaina da ku gafarar Allah mai girma, tare da sauran

musulmi daga kowanne zunubi, ina roqonsa ya gafarta musu, domin

shine mai yawan gafara mai yawan rahama.

53

7

Reno Da Sharuxan Da Suka Kevanta Da Shi

Godiya ta tabbata ga Allah, tsira da amincin Allah su tabbata ga

Manzon Allah, bayan haka, godiya ta tabbata ga Allah, muna gode

masa muna kuma neman gafararsa, muna neman tsarin Allah daga

sharrin kawunanmu, da munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya

shiryar babu mai vatar dashi, wanda kuma ya vatar babu mai shiryar

da shi. Kuma ina shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah,

kuma ina shedawa Shugabanmu Annabi Muhammadu bawan Allah ne

kuma manzonsa ne, ya isar da saqo ya sauke nauyin amfana, ya yiwa

al’umma nasiha ya yi jihadi wajen xaukaka addinin Allah matuqar

jihadi ya barmu akan hanya mai haske wacce hasken darenta dai-dai

yake da na ranarta, ba wanda zai kauce daga tafarkinta sai hallakakke.

Allah ya yi daxin tsira da albarka bisa alayensa da sahabbansa da

mabiyansa da wanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar

sakamako.

Bayan haka:

Allah Maxaukakin Sarki yace: “ya ku waxanda suka yi imani!

Kubi Allah da taqawa akan haqqin binsa da taqawa kuma kada ku

mutu face kuna masu sallamawa’’ (A’li-imran: 102). Haka nan Allah

Maxaukakin Sarki yana cewa:

kuma masu haihuwa (sakakku) suna shayar da abin

haifuwarsu shekara biyu cikakku ga wanda ya yi nufin ya

cika shayarwa. Kuma ciyar da su da tufatar da su yana

kan wanda aka haifar masa da alheri. Ba a kallafawa rai

face iyawarsa. Ba a cutar da uwa game da xanta, kuma ba

a cutar da uba game da xansa, kuma akan magaji akwai

misalin wancan. To idan suka yi nufin yaye, akan

54

yardatayya daga gare su da shawartar juna, to babu laifi

akansu. Kuma idan kun yi nufin ku bayar da xiyanku

shayarwa, to babu laifi akanku, idan kun miqa abin da ku

ka zo da shi bisa al’ada. Kuma ku bi Allah da taqawa.

Kuma ku sani cewa lalle ne Allah, ga abin da ku ke

aikatawa, Mai gani ne (Baqara: 233)

Ya ku mutane! ina yi muku wasiyya da kaina da tsoron Allah, kuma

ku sani cewa, reno shine ba wa yaro kulawa ta fuskar samar masa

makwanci da abincinsa da tufafinsa da tsaftar jikinsa da wurin

kwanansa. Hukuncin reno kuma wajibi ne, domin yin watsi da shi

tozartarwa ce ga yaro da hallaka shi, kamar yadda reno xaya ne daka

cikin abubuwan da Allah ya kimsa a cikin xabi’ar kowanne xan adam,

don haka za ka iske cewa ba ya kevanta ne kaxai da tsarin shari’ar

musulunci ba. Kamar yadda reno yana zama wajibi ne akan kowanne

xaya daga cikin uwa da uba kasancewarsa haqqine na tarayya

tsakanin wacce ta ke renon da wanda ake renon dukkansu suna da

haqqin a ciyar da su a tufatar da su, kamar yadda kuma wanda ake

renon yake da haqqin a dinga zuwa ana ganinsa, a na sa ido akan

yanayin da yake ciki da duba shi da ladabtar da shi, da ilmantar da shi.

Haka nan reno haqqi ne da ke kan shaqiqai mata muharramai,

sannan shaqiqai maza. Ga masu reno kamar haka:

Na farko Uwa domin itace ta fi kowa tausaya masa, kamar yadda an bada

labarin cewa wani mutum da ya saki matarsa, ya kuma yi nufin qwace

xansa daga wurinta sai ta zo wajen manzon Allah tsira da amincin

Allah su tabbata a gare shi tace;

ya Manzon Allah wannnan xana ne wanda cikina ya

kasance shine mazubinsa, kuma mamana shine abin

shansa, kamar yadda cinyata itace wajen hutawarsa, to

gashi mahaifinsa ya sake ni yana kuma son ya qwace min

shi’’ sai Manzon Allah tsira da amicin Allah su tabbata a

55

gare shi yace; “ke ki ka fi kowa haqqin riqe shi matuqar

ba kiyi aureba (Aunul ma’abud)

Sannan kuma abu Dawud da Tirmidhi sun fitar da hadisi daga Ali

Allah ya yarda da shi yace: Zaid dan Haritha ya fita ya nufi Makkah

ya dawo shi da ‘yar Hamza, sai Ja'afar yace: ni zan karveta don ni na

fi haqqin in riqe ta domin ‘yar baffana ce, sannan kuma akwai ‘yar

uwar mahaifiyarta matata, to ga shi kuma ‘yar uwar uwa tana da

hukunci irin na uwane. Shi kuma Ali sai yace: Ni na fi cancanta da

riqe ta don ‘yar baffana ce ga kuma matata ‘yar manzon Allah wacce

tafi kowa cancanta da ta riqe ta. Sai Zaid yace ni na fi cancanta da

renon ta, don ni na fita na nemota na shafe tafiya mai tsawo. Sai ya

ambaci hadisin nan da yake cewa:

Dangane da yarinya kuma na yi hukunci da a bayar da ita

ga Ja'afar ta yadda za ta kasance da yar’uwar

mahaifiyarta domin yar’uwar uwa a matsayin uwa take”

a wata riwayar kuma yace: “Lalle ‘yar uwar uwa, uwa

ce’.

Haka nan reno ya kan kasance ga mata da maza ne kamar kamar

yadda haqqin reno ya ke babu banbanci tsakanin musulmi da kafiri,

da bawa da ‘yantacce matuqar dai duk sharuxansa sun cika garesu,

wannan kuwa ya samo asaline kasancewar reno nauyi ne na

shugabanci da jagoranci don haka ba wanda ya cancanta ya yi shi sai

wanda ya siffantu da siffofi irin waxanda za su tabbatar da

cancantarsa, da cewa zai bawa yaron kariya ya kuma iya tsayawa da

abubuwan da yaron yake buqata to amma asalin waxanda aka sani da

reno sune mata, domin sune suka fi tausayi da jinqai suka fi sanin

hanyoyin tarbiyar qananan yara, sannan kuma sai ya koma hannun

maza kasancewar su ne suka fi ikon bayar da kariya, da kula wa, da

tsayuwa da abubuwan da yaron ke da bukata, to amma kowanne daga

cikin sn yana da sharuxa

56

Hakan nan an shimfixa waxansu sharuxa na tabbatar da haqqin

reno kafin mutum ya cancanci aiwatar da shi a kuma bashi ikon yinsa.

Daga cikin waxannan sharuxa akwai waxanda suka shafi wanda za’a

yiwa reno namiji da kuma waxanda suka shafi mace mai reno sannan

akwai waxanda suke yin tarayya a tsakaninsu:

2. Hankali Ba’a bayar da reno ga mahaukci, ba banbanci tsakanin mahaukacin da

ya haukace gaba xaya da wanda ya kanyi hauka na wani lokaci ya

warke wani lokaci, kamar yadda ba’a bayar da reno ga mai

rangwamen hankali ko kwar-kwar.

3. Ikon tsayawa da shi Wato ikon tsayawa da al’amuran wanda ake reno, don haka ba a bayar

da reno a hannu mai rauni da tsoho, da makaho, da bebe, da kurma, da

gurgu, da sauran ire-iren su maza ne ko mata duk waxannan ba’a basu

reno sai dai idan akwan waxanda za su yi musu renon, domin su

kansu suna da buqatar wanda zai tsaya da al’amuransu ballantana ace

za su xauki nauyin wani. To amma Hanafiyya suna da wata Magana

dangane da renon makaho da suka ce: “Dangane da renon sa indai har yana da ikon bayar da kariya to za’a iya bashi in kuwa ba hakan ba to ba za’a bashi ba” wannan kuma shine ra’ayin Mazhabin Shafi’iyya

3. Shiriya Shiriya xaya ce daga cikin siffofin cancanta, wacce ta haxa da balaga,

da ikon iya kulawa da xawainiya don sau da yawa za ka iske mutum

ya balaga to amma ba shiryayye bane to sai ya zama duk da balagarsa

wawa ne mai al’mubazzaranci ba zai iya kulawa da dukiya ba, sannan

kuma tana iya yiwuwa a sami wanda yake shiryayye amma bai balaga

ba, wannan abune da yake faruwa a kowanne lokaci na rayuwar

mutune.

Don haka sai Malikiyya suka sharxanta shiriya da wannan

ma’anar ta biyu wato suka xauka cewa mai renon ya kasance

shiryayye ne wajen kulawa da dukiya ko da kuwa ba baligi bane,

57

kasancewar daga cikin abubuwan da reno ya qunsa akwai tsare

dukiya, da iya hulxa ta kuxi ta hanya mai kyau don haka bisa wannan

ba’abawa wawa ko al-mubazzari reno don kada ya lalata dukiyar

wanda ake reno.

Addussuqi yace: In har ya tabbata yaro yana iya kulawa

da dukiya to an tabbatar da cewa zai iya renon waninsa,

ta yadda zai kasance shi wancan yaro mai reno shida mai

renonsa suna qarqashin kulawar mai renon yaron na

farko abin nufi sai renon babban ya kasance ta fuskar

rayuwar wanda ake renon shi kuma na yaron ta fuskar

dukiyarsa

1. Kuvuta daga cututtukan da ake iya xauka:

Wannan ya haxa da duk wata cuta da ake jin tsoron yaron zai

kamu da ita koda kuwa shi kansa yaron yana da irinta wannan

ya haxa da kuturta da sauran dangoginta na cututtuka masu

yaxuwa waxanda wani yake iya xauka a sanadiyar cakuxuwa

ko wanda za’a iya cutuwa ta hanyar hakan waxannan sun haxa

da qarzuwa da kirci da kuturta, to amma idan cutar mai sauqi ce

to ba za ta cutar ta fannin cancantar reno ba, wannan ya qunshi

kowacce cuta dake iya yaxuwa ko cutarwa da likitoci za su iya

ganowa a kowannane lokaci a kowacce qasa tana iya shiga

cikin jerin cututtuka da muka ambata.

2. Amana: abin da ake nufi a nan shine mai renon ya

kasance wanda ake iya amincewa da shi ne ta fuskar addinin

wanda ake reno da xabi’unsa da tarbiyyarsa, don haka ba’a

bayar da reno ga wanda ake jin tsoron zai iya gurvata addinin

wanda ake reno ko xabi’unsa ko tarbiyyarsa don haka ba’a

bayar da reno ga fasiqi ko fasiqa waxanda suka haxa da

mashaya giya ko wanda ya shahara da zina ko nau’oin wasanni

da aka haramta kasancewar irin waxannan na iya shagala da

fasiqancinsu da wasanninsu su bar waxanda aka ba reno su

58

tozarta. Haka nan mai reno namiji da mace duk xaya suke ta

fuskar amana

Ibn Abdul Bar yace:

Sabo da haka malamai ba sa ganin dacewar renon fajira

3. Samun muhalli: an sharxanta cewa tilas ne mahallin

mai renon ya kasance killatacce ne ta yadda za a amincewa

wanda ake renon ba zai wulaqanta ba, ko waxansu abubuwa ba

za su same shi ba, kamar shigowar fasiqai gidan ko su yi

mu’amala da yara, kamar gidan ya kasance yana qarshen gari

ne ba shi da tsaro kowa na iya shiga da daddare, haka nan ana

jiyewa ‘ya mace tsoron lalacewa a lokacin da ta kai munzalin za

a iya saduwa da ita. Hakan nan yaro na miji shima akan jiye

masa tsoron hakan.

Don haka za mu fahimci cewa manufar samun mahalli ita ce a

samu abubuwa guda uku: kare rai, da kare dukiya da kuma kare

mutunci daga gurvata.

4. Rashin kakkausan hali: Haka nan an sharxanta cewa

kada a sami kakkausan hali na mai reno ga wanda zai

raina don haka duk wanda aka san cewa yana da qarancin

tausayi da mugunta ko dai tun asali haka halinsa yake ko

kuma a sanadiyyar gabar dake tsakaninsa da mahaifan

wanda zai raina to in dai aka tabbatar da hakan sai a

gabatar da waninsa.

Dangane kuwa da haqqokin da ake yin tarayya akansu a dunqule

Iman Malik yana cewa dangane da mai reno mace:

Idan mace ba ta kasance a wuri killatacce ba, ko kuma ba

amintacciya ce ba, ko mara lafiya, komai rauni, ko

tsohuwa, to ba za a bata reno ba ‘yantacciya ce ita ko

baiwa

59

Albaji yace: “dalilin da yasa aka ce hakan shine; shi dai reno an sharxanta shi ne don tausayawa yaro, don haka idan har za ta gaza wajen tsayuwa da hakan ko bata da tausayi haqiqa zamansa a wurinta tozarta ce a gare shi” kuma waxannan abubuwa da aka faxa dangane

da mai reno mace an sharxanta su ga mai reno namiji. Ya ku bayin!

Allah “Haqiqa Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’a, yana yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90). Ku ambaci Allah zai ambace ku, kuma ku yi masa godiya

bisa ni’imarsa sai ya qara muku, kuma haqiqa ambaton Allah shine

mafi girma kuma Allah yana sane da abin da kuka kasance kuna

aikatawa.

60

Huduba ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah wanda shine abin nufi da buqata, tsira da

aminci dawamammu su tabbata ga annabin Allah, kuma manzonsa

kuma shugabanmu Annabi Muhammad, tsira wanda yake

dauwamamme da dauwamar mulkin Allah kuma ina shedawa babu

abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin

tarayya kuma ina shedawa Muhammad bawansa ne kuma manzonsa

ne Allah yayi daxin tsira a gare shi da alayensa da sahabbansa da duk

wanda yayi aiki da shiriyar sa har zuwa ranar sakamako.Ya ‘yan uwa

cikin imani kuji tsoron Allah haqiqanin jin tsoronsa .

Ba shakka Ahmad ya ruwaito hadisi shi da Hakim ya kuma

inganta shi daga Abu Ayyub al Ansari Khalid xan Yazid Al-ansari

Allah ya yarda da shi annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare

shi yace: “duk wanda ya raba tsakanin yaro da mahaifiyarsa Allah zai raba shi da masoyansa a ranar alqiyama”.

Reno haqqi ne na yaro da yake da shi akan mahaifansa, kuma

xaya daga cikin abubuwa da suka zamo wajibi a kansu matukar dai

akwai alaqar aure a sakaninsu kuma suna zaune tare, to idan kuwa

suka rabu da juna to a wannan lokaci sai a kula da maslahar yaron da

za a rena. dangane kuwa da waxanda suka tafi a kan cewa haqqi ne na

uwa to sun dogara ne da faxar manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi "ke ki ka fi cancanta da riqe shi matukar ba ki yi aure ba” sannan kuma kasancewar za ta cutu a lokacin da aka raba ta

da yaron nata alhali kuwa Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “Ba a cutar da uwa game da xanta” (Bakara: 233). Dangane kuwa da

waxanda suke ganin cewa haqqi ne na yaro sun yi la'akari ne da kare

rayuwar yaron, da kula da shi da maslaharsa ba tare an waiwayi

maslahar mahaifiyarsa ba, wanda a dalilin haka ne ma za ka ga cewa

ana karve shi daga hannunta a lokacin da ta yi aure koda kuwa za ta

cutu a sanadiyyar yin hakan. Haka nan kuma idan mahaifinsa ya yi

tafiya irin tafiyar da za a zauna a can. Kamar yadda akan tilasta mata

61

reno matuqar ba wanda zai yi renon yaron sai ita wanda dukkan

waxannan abubuwa an yi sune don kulawa da yaron.

Haka nan bai kamata al’amarin reno yaci karo dana walicci ba

don haka a lokacin da yaro ya kasance qarqashin renon mahaifiyarsa,

hakan ba zai hana ya rinqa zuwa wurin mahaifinsa yana ilmantar da

shi ya koya masa ladabi, ya kuma damqa shi a hannun wanda zai

koya masa Alkurani da karatu da sana’a ko yadda za a gudanar da

rayuwa ba, wannan ya biyo bayan kasancewar waxannan abubuwa

dukkansu abubuwane da ake samun su daga mahaifi, don haka

mahaifi ya fi cancanta da ya riqe yaro a lokacin da yake buqatar

koyarwa, duk da cewa hakan ba zai hana renonsa ba. Haka nan xaukar

nauyin yaron da za a rena wanda yake talaka ne da nemo masa wanda

ya fi cancanta da renon sa, duk yana kan mahaifinsa mawadaci wanda

shine zai xauki nauyin abin da zai ci, ya sha, da kuma suturar da zai

sa, da sabulun wanka, da duk abin da zai buqata na wanki da sauran

kayan amfani. Kuma abin da za a yi la’akari da shi a dukkan

waxannan abubuwa ita ce al’ada, da wadatar mahaifin ko talaucinsa,

da kuma irin abubuwan da suka dace da sauran yara da ake reno masu

matsayi irin na sa.

Haka nan tilas ne akan mahaifi ko wanda ake yiwa wasiyya ya

xaukewa wacce aka bawa reno abinda za ta xauki nauyin yaron da

suturarsa, da dukkan abubuwa da aka ambata, kamar yadda alkali na

iya rubuta cewa: "wane ya bawa wance kaza da kaza don a yiwa yaronsa kuxin abinci, da yi masa hidima, da kuxin hayar gidansa’’ Kamar yadda kuma haqqi ne na mahaifiya ta ga ‘ya’yanta qanana

kowacce rana sau xaya, idan ba a wurinta suke ba, ta kuma ga

‘ya’yanta manya kowanne sati sau xaya. Khalil a cikin Mukhtasar xinsa yana cewa: “An hukunta haka ga yara qanana sau xaya a kullum, su kuwa manya kowacce ranar Jumuah”

Allah ya yi muku albarka ga fahimtar Alkurani mai girma ya

kuma amfane ku da abin da ke cikinsa na ayoyi da ambato mai

hikima, kuma muna roqon Allah ya tserar da ni da ku daga azaba mai

raxaxi, ya kuma shigar da ni, ya shigar da ku gidan ni’ima ya kuma

amsa muku domin shi Mai jine Masani.

62

Haqiqa Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa

ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin

da aka qi da rarrabe jama’a, yana yi muku gargaxi

tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90).

Ku miqe zuwa ga sallah, Allah ya yi muku rahama.

63

8

Haqqoqin Mace Akan Waliyyinta

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya yi umurni da aiyuka nagari da

sada zumunta ya yi mana hani ga savawa iyaye ya kuma sanya haqqin

musulmi akan xan uwansa musulmi ya kasance mafi qarfin haqqoqi,

haka nan kuma ya sanyawa mace haqqi akan waliyanta na su aurar da

ita ga wanda ya dace da ita, ta kuma amince da shi. Kuma muna

shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah wanda shi kaxai

yake bashi da abokin tarayya kuma wanda yake shine ya yi halitta,

kuma dukkan wanda ba shi ba abin halitta ne, muna kuma shedawa

shugabanmu Annabi Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne,

wanda shine mai gaskiya abin gaskatawa ya Allah ka yi daxin tsira da

aminci a gare shi da alayensa da sahabbansa waxanda suka sauke

haqqoqi, da waxanda suka biyo su da kyautatawa cikin waxanda suka

gabata da kuma waxanda suka yi saura.

Ya ku mutane! Ku ji tsoron Allah ku kuma godewa ni’imar da

Allah ya yi muku ta ‘ya’ya a matsayin jarrabawa ko dai su zame muku

abin farin ciki duniya da lahira, ko su zame muku asara da abin

nadama, da wahala duniya da lahira. Kuma lalle yana xaya daga cikin

hanyoyi na godewa ni’imar Allah a cikinsu, ku tsaya da abin da Allah

ya wajabta akan ku na renon su da ladabtar da su bisa mafi kyawun

halaye, ku kuma aurar da su ta hanyar da Allah da Manzonsa suka yi

muku umarni, don haka ya zamo tillas mahaifi ya ji ra’ayin mace ya

sami yardarta kafin ya aurar da ita.

Ya ku bayin Allah! Haqiqa haqqin iyali da jibintar al’amuransu

abu ne da ya tabbata da ayoyi da hadisai, Manzan Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi yana cewa:

64

lalle wanda ya fi kowa imani daga cikin muminai shine

wanda ya fi kyawawan halaye ya kuma fi su tausasawa

ga iyalinsa1.

Don haka ya zama tilas ga dukkan mai hankali ya yi aiki da

shiryarwar manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi

yace dangane da tausayawa mace ko dai a matsayinta na matar aure

ko ‘ya ko ‘yar uwa. Idan ta kasance matarsa to ya kamata ya sani

cewa tana da haqqoqi akansa haka ma idan ta kasance uwa to tana da

haqqoqi, kuma yana daga ciki haqqoqin da ‘yarsa ke da su akansa

akwai gujewa aurar da ita ga wanda ba taso ko ga wanda bai dace da

ita ba.

An karvo daga Khansa’u ‘yar Khidam Al-ansari cewa:

mahaifinta ya aurar da ita a lokacin tana bazawara sai ta ji ba ta son

hakan, sai ta je wajen Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata

a gare shi sai ya warware auren nata (Fathul bari). An karvo kuma

daga Ibn Abbas Allah ya yarda da shi yana cewa: “wata yarinya ta zo wajen Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ta ambata masa cewa mahaifinta ya aurar da ita alhali ba ta so, sai Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya ba ta zavi”

Iman Ahmad da Abu Dawud suka ruwaito.

An karvo daga Abdullahi xan Buraidata shi kuma ya karvo

daga mahaiafinsa yace: “wata budurwa ta zo wajen Manzon Allah tsira da aminci su tabbata a gare shi tace: lalle mahaifina ya aurar dani ga xan xan uwansa don ya xaukaka matsayinsa, yace: sai Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya sanya al’amarinta a hannunta sai ta ce na zartar da abin da mahaifina ya yi dama na yi nufi ne nasanar da mata cewa iyaye maza ba su da haqqi na tilastawa ‘ya’yansu mata. Ibn Majaha ya ruwaito shi kuma maruwaitansa

ingantattu ne.

Ya ku ‘yan uwa! Lalle bayan abin da ake ji a zuciya dangane

da ‘ya’ya da abin da Allah ya sanya a cikin zukatan iyaye na qauna da

1 Imam Ahmad da Tirmidhi

65

tausayi da jinqai da tausayi ga ‘ya’yansu ba za su bari mahaifi ya

aurar da yarsa ga wanda ba ta so ba. Don ba shakka, zukatan iyaye an

cusa musu qaunar ‘ya’yansu an kuma dasa musu tausayi da son bayar

da kulawa gare su, da tausaya musu, da bayar da mahinmanci ga

al’amuransu. Don haka duk wanda ya rasa wannan xabi’a ta tausayi

ya aurar da ‘yarsa ga wanda bai dace ba, ko ga wanda ba ta so batare

da wata maslaha ba, to ba shakka ya siffantu da mugunta ya bi son

zuciya. Kamar yadda xaukar irin wannan mataki baya rasa haifar da

mumman sakamako na fanxarewar yarinyar da aka yiwa auren dole ya

janyo ta gudu daga cikin gidan mijinta ta faxa cikin halaye na qazanta

da bin hanyar rashin arziki wanda mahaifinta ya jefa ta ciki sabo da

jahilci.

Kamar yadda qasashenmu a wannan zamani akwai waxanda

suke yiwa ‘ya’yansu auren dole ba tare da wata hujja ba. Don haka

lalle waliyyai da suka haxa da ‘yan uwa, da mahaifi su ji tsoron Allah.

kamar yadda a yanzu al’amarin har ya kai ga cewa wasu lokuta har da

iyaye mata da kakannin mata waxanda basu da wani haqqi na walicci

ko yin dole to amma sai ka gansu suna yiwa yarinya auren dole su

bayar da ita ga wanda ba taso sabo da masalaharsu ba ta yarinyar ba.

Ya ku bayin Allah! haqiqa mawallafin littafin Fiqhussunnah (Sayyid

Sabiq) a cikin babin wajibcin neman izinin mace kafin aurar da ita

yana cewa:

Duk da irin savani da aka yi dangane da waliccin mace

ya zama wajibi a fara jin ita ra’ayin macen don a sami

amincewarta kafin xaurin aure kasancewar aure

mu’amala ce ta har abada, kamar yadda zama ne na haxin

gwiwa tsakanin namiji da mace, to idan kuwa haka ne, ba

ta yadda za a samu dauwamar haxin kai, kuma soyayya

da danqon kauna su xore matukar ba a sami yarda ba. To

bisa wannan ne shari’a ta hana yiwa mace auren dole

budurwa ko bazawara, ta hanyar tillasta mata ta auri

wanda ba ta so. Kamar yadda shari’ah ta sanya xaura

mata aure kafin neman yardarta xaya daga cikin

66

abubuwan da suke sa aure ya qi inganta, ya kuma ba ta

damar ta nemi a warware shi don yin watsi da nuna fin

qarfi da waliyinta ya yi wajen xaura mata aure.

(Fikhussunnah, juz’i na 2, shafi na 89-90).

Ya ku bayin Allah! lalle tilasta mace akan auren dole haqqine kawai

na waliyyi da ke da ikon yin tillas, to amma duk da haka bai halalta a

qyale shi ya yi amfani da hakan a matsayin wata hanya ta zaluntarta

ba, in har kuwa ya tabbata cewa ya yi nufin cutar da ita kamar aurar

da ita ga fasiki ko mara lafiya kama kuturu ko mahaukaci ko

dandaqaqqe to bai halalta ya tillas ta taba. Haka nan kuma haramun

ne a gare shi ya jingin ta, wato waliyyi ya hana matar da take

karkashin waliccin sa yin aure sabo da takurawa da zalunci ba tare da

wata maslaha ba. Haka kuma Allah Maxaukakin Sarki ya haramta

hakan a inda yake yin kira ga waliyyai da cewa:

To kada ku (waliyyansu) hana su su auri mazansu (da

suka sake su) (Baqarah: 323).

Don haka in har aka samu cewa waliyyi da ke da izinin yin tilas yayi

nufin cutarwa ne ko dai ta hanyar take-takensa da aka gani koya faxa

da bakinsa, kamar kasancewar matar ma’aikaciya ce da yake cinye

albashinta, ko yana amfana da hidimar da take yi masa, ta yadda zai yi

asarar dukkan waxannan da zarar ya aurar da ita, to ba shakka

haqqinsa na yin tilas ya faxi.

Haqiqa abin da yake gudana a yau a wannan qasashe namu ta

yadda za ka iske waxanda ba su da ikon yin tilas suna yin hakan varna

ce babba, domin kuwa yin tilas haqqine kawai na mahaifi da ya cika

sharuxan yin haka.

Haka nan mafi yawa daga cikin malaman fiqhu da suka haxa da

Imam Malik da Shafi’i da Ahmad bin Hambal suna ganin cewa,

yardar waliyyi da amincewarsa na xaya daka cikin sharuxan ingancin

aure, kuma mace wacce take mai hankali kuma baliga in ta kasance

budurwa waliccinta zai zamo na dole ne, ta yadda al’amarin aurar da

67

ita zai kasance ne a hannun waliyyinta shi kaxai in kuwa ta kasance

bazawara ce to waliccinta na tarayya ne a sami yardar waliyyinta da

amincewarta ita kanta. Sun bayar da dalilin yin haka daga Alqur’ani

da sunnar annabi mai martaba.

Dalilin da suka dogara da shi daga littafin Allah shi fadin Allah

Madaukakin Sarki:

To kada ku (waliyyansu) hana su auri mazansu idan sun

yarda da juna a tsakanin su da alheri (Bakara: 232).

Daga sunnah kuma faxinsa tsira da aminci su tabbata a gare shi.

Mace bata aurar da mace, kuma mace bata aurar da

kanta, duk wata mace da ta yi aure ba tare da izinin

waliyinta ba to auren ta vatacce ne, vatacce ne, vatacce

ne, in har ya sadu da ita to tana da sadaki na abin da ya

halalta na farjinta, in kuma aka yi jayayya to shugaba

shine waliyyin wanda bashi da waliyyi”1 haka nan ya zo

a hadisin Abu Musa yana cewa: Annabi tsira da amincin

Allah su tabbata a gare shi yace: “ Ba aure sai da

waliyyi2.

Yaku bayin Allah! Haqiqa walicci ga mace a lokacin aure girmama

mace ne, da martabata ta yadda Allah ya sanya mata wani wakili da

zai kare ta ya kuma tsare mata haqqoqinta yayin xaurin aure, domin

kuwa da ace itace za ta xauki nauyin yin hakan da kanta, da kunya ta

rinjaye ta ta sarayar da da yawa daka cikin haqqoqinta yayin xaurin

aure. wannan fa ta vangaren abin duniya da ya shafi kayan aure

kenan, a xaya vangaren kuma wanda shine mafi muhimmanici wanda

ya zavar miji da ya dace, ma’abocin halaye masu kyau da riqo da

addini, wanda zai faranta mata rai ya kuma kare haqqoqinta ba shakka

1Subulussalam, juz’I na 3 shafi na 128

2 Abu Dawud da Tirmidhi suka ruwaito

68

waliyi ya fi kowa ikon yin hakan kasancewarsa mafi rinjayen lokuta

mutum ne da ya fita gogayya da hango Haqiqanin al’amura. Kamar

yadda son rai na xan wani lokaci na iya fizgar macen da take son aure

ta shaqu da saurayin neman auren ta saboda kwalliyarsa ba tare da

wani zurfin tunani ba, son zuciya da qarancin tunani su vebe ta, ta

hango wata maslaha a matsayinta ta gaske ta hanyar irin shigar da

yake qarya da yaudara. Ba shakka wannan ta tava faruwa a Maiduguri

inda aka samu wani saurayi ya yaudari wata budurwa da ta shaqu da

shi sabo da kwalliyarsa ta fili, duk dacewa mahaifinta ya tanadar mata

miji nagari wanda ya dace da ita, wanda kuma ya yi alqawarin cewa

zai barta ta cigaba da karatu, to amma sai taqi ta bawa mahaifin nata

haxin kai, bayan ‘yan uwanta sun sha fama wajen qoqarin janyo

hankalinta, taqi sai kawai suka aura mata wanda ta zavawa kanta,

bayan sun haifi xa xaya kawai sai ya yi amfani da wannan dama ya

hana ta ci gaba da karatun nata, da kuma aikin da take yi na koyarwa,

aka wayi gari a koda yaushe yana tuhumarta da zina, sannan bayan ta

haifa masa ‘ya’ya biyar cikin wahala da tsanani mahaifinta kuma ya

rasu, aka wayi gari ita da mahaifiyyarta a kullum ba abin da suke fama

dashi in banda talauci, sai ya kama zarginta da cewa shi yana ma

zarginta da shakkar cewa ‘ya’yan nasa ne, duk da cewa kuwa shi

mazinacine wanda har ta kai ga waxansu lokuta takan same shi tare da

matan maqotanta a gidan haya, kamar yadda take faxa, sannan kuma

ya kan fita daga gida don zuwa wajen waxansu matan na daban. Duk

lokacin da ta nemi ya sake ta sai ya yi sauri ya rigata zuwa wajen

alqali, ya yi kararta wajen alkali da cewar yana son ta fanshi kanta.

Hakan nan daga qarshe sai ya zo mata da wata shawara cewa tunda

dai shi yana shakkar kasancewar waxancan ‘ya’yan nata uku ba na sa

ba ne, abin daya fi shine su kashe su gaba xayansu su huta shi da ita,

da dai ya ga taqi amincewa sai yace to shi zai kasheta ya shaqe ta, da

nufin kashe ta, ta yi ta qoqarin qwatar kanta har dai Allah dai ya bata

ikon kuvuta daga gare shi kamar yadda ta bayyana.

A lokacin da ta nemi taimakon mahaifiyarta ita kuwa ta ce ba za

ta iya taimaka mata da komai ba.

69

To anan ne nake cewa wannan shine sakamakon savawa iyaye

Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

Kuma mun yi wasiyya ga mutum game da mahaifansa

biyu uwarsa ta xauke shi a cikin rauni akan wani rauni,

kuma yayensa a cikin shekara biyu (muka ce masa) ka

gode mini da kuma mahaifanka biyu makoma zuwa

gareni kawai take. Kuma idan mahaifanka suka tsananta

maka ga ka yi shirka dani ga abin da baka da ilimi a gare

shi to kada kayi musu xa’a. Kuma ka aboce su a cikin

duniya gwargwadon shari’ah, kuma ka bi hanyar wanda

ya mai da al’amari zuwa gare ni, sannan zuwa gare ni

makomarku take, sannan in baku labari game da abin da

kuka kasance kuna aikatawa (Lukman 14-15).

Ina roqon Allah ya yi mana albarka ni daku cikin fahimtar Alqur’ani

mai girma, ya kuma amfane ni ya amfane ku da abin dake cikinsa na

ayoyi da anbato mai hikima, Allah ya yi mana gafara ni da ku, lalle

shi Maiji ne kuma Masani.

70

Huduba Ta Biyu:

Godiya ta tabbata ga Allah mai girma, wanda shine mai

dauwamammen iko, da kyautatawa wanda ya umurci mace da suturta

jikinta da lazimtar ladabi, wanda kuma a bisa wannan ne kowanne

gida yake kafuwa kuma ya ginu. Kuma muna shedawa cewa babu

abin bautawa da gaskiya sai Allah, muna kuma shedawa Annabi

Muhammadu bawansa ne kuma Manzonsa ne wanda shine yake cewa:

Akwai dinarin da zaka bayar wajen xaukaka addinin

Allah, da dinarin da za ka bayar don ‘yanta bawa, da

dinarin da za ka yi sadaka da shi ga miskini, da dinarin da

za ka bayar wajen kula da iyalinka, wanda duk ya fi

giman lada a cikinsu shine wanda kabayar ga iyalinka”1

da alayensa da sahabbansa ka yi qarin aminci a gare su.

Ya ku bayin Allah! Iyaye masu haqqin yin dole Haqiqa shari’ah ba ta

ba ku dama ku aurar da ‘ya’yanku mata ba tare da izininsu ba, a

matsayin wata hanya ta cutar da su ba. Domin kuwa wancan haqqi da

aka ba ku na yin dole yana tabbata ne kawai idan bai bayyana cewa,

kuna da nufin cutar da su ta hanyar aurar da su ga fasiqi ko mahaukaci

ko dandaqaqqe, kamar yadda auren dole da mahaifi zai yiwa ‘yarsa an

taqaiceshi da waxansu qa’ijoji waxanda suka haxa da:

Na farko: ya kasance mahaifin bai hukunta cewa ‘yarsa baliga ta yi

hankali ba, in kuwa ya hukunta hakan to bashi da haqqin yi mata dole.

Na biyu: ya kasance buduwar da ba ta tava aure ba. In kuwa ta yi suka

rabu da mijinta to bashi haqqin yi mata dole koda kuwa ba ta gushe

tana budurwa ba, ya kuma kasance mijin ya dace da ita, idan ya

1 Imam Muslim

71

kasance mijin bai dace da ita ba ko kuma akwai cutarwa to mahaifi

bashi da haqqin yi mata dole.

Duk da cewa yana da haqqin yin dole ga waxanda muka ambata a

cikin ‘ya’yansa ana nemansa da ya yi shawara da ‘yarsa budurwa

baliga a cikin al’amarin aurenta, saboda abin da ya zo a cikin hadisi

“bazawara ta fi cancanta da yiwa kanta zavi fiye da waliyinta, buduwa kuwa sai a nemi izininta, izininta shine ta yi shiru” 1 wananan hadisi

yana nuna mana cewa akwai banbancin hukunci tsakanin bazawara

wacce ita ta fi haqqi ta yi zavi da kanta, budurwa kuwa ba ta da zavin

haka abin da za a yi mata kawai shine shawartarta, da neman izininta

yadda za a faranta mata rai, domin da ace budurwa da bazawara duk

hukuncinsu xaya ne da hadisi bai banbanta su da neman izininta ba,

Allah Madaukakin Sarki yana cewa:

Kuma akwai daga ayoyinSa Ya halitta muku matan aure

daga kanku, domin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya

sanya soyayya da rahama a tsakaninku. Lalle a cikin

wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani (Rum:

21)

Ya ku yan’uwa! Ku yi salati ku yi sallama ga mavuvvugar rahamar

Ubangiji wanda ya kankama akan shimfixar bautar Allah, wanda

kuma shine ya san Allah Haqiqa nin sani ya kuma ji tsoransa

haqiqanin jin tsoro, shugabanmu Annabi Muhammadu annabin

rahama, don Allah ubangijin mu da Mahalincin mu ya yi muku

umarni da hakan a inda yake cewa:

Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, Ya ku

waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku

yi sallama domin amintarwa a gare shi (Ahzab: 56)

1 Imam Muslim

72

Muna roqon Allah ya yarda da shugabanmu da Abubakar da Umar da

Usman da Ali da sauran sahabbai baki xaya. Ya ubangijin mu kada

kabar wani zunubi namu a wannan wuri face ka gafarta shi, kada

kabar wani baqin ciki face ka yaye shi, ko wata buqata daga cikin

buqatun duniya da na lahira wacce a cikinta akwai yardarka mu kuma

a cikinta akwai maslahar mu face ka biya mana ita ka sauqaqa ta ya

Ubangijin halitta.

Yaku bayin Allah! Lalle Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90), ku miqe zuwa sallah Allah ya yi muku rahama.

73

9

Ni’imar Da Ke Cikin Aure

Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa muna yaba masa muna

neman gafararsa, muna neman taimakonsa, muna tuba a gareshi, muna

dogara da shi, muna kuma neman tsarin Allah da daga sharrin

kawunanmu, da miyagun aiyukanmu, muna kuma shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah kuma Annabi Muhammad bawansa ne

kuma manzonsa ne, Allah ya yi daxin tsira a gare shi da alayensa da

sahabbansa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:

Yaku bayin Allah! Ku ji tsoran Allah kuyi masa godiya

bisa halitta muku matan aure daga kanku, domin ku natsu

zuwa gare ta, kuma Ya sanya soyayya da rahama a

tsakaninku, lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga mutane

masu yin tunani.

Ba shakka aure babbar ni’imace da Allah ya yiwa dan Adam maza da

matan su wacce Allah ya halitta musu ko ya yi musu umarni dashi ya

kuma kwaxaitar da su akan yinsa, Allah Maxaukakin Sarki yace:

ku auri abin da ya yi muku daxi daga mata; biyu-biyu, da

uk-uku da huxu-huxu, sannan idan kun ji tsoron ba za ku

yi adalci ba, to (ku auri) guda ko abin da hannayenku na

dama suka mallaka…. (Nisa’i: 3)

Kuma annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace: “ya ku jama’a da matasa duk wanda yake da iko a cikin ku to ya yi aure

74

domin shi ne abu mafi sa a runtse ido yafi bayar da kariya ga farji”1

Hakan nan manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi

a lokacin da yake maida martani ga waxansu mutane xayansu yace:

Ni zan yi ta sallah har abada”, shi kuma na biyu yace: “ni

zanta yin azumi tsawan rayuwa ba zan sha ba”, shi kuma

na uku yace: “ni kuma zan qauracewa mata ba zan yi

aure ba”, sai manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi yace: “shin kune kuka ce kaza da kaza?

to wallahi ni na fi ku jin tsoron Allah da taqawa a gare

shi, amma ni ina azumi ina kuma sha, sannan ina yin

sallah na kuma inyi barci, kuma ina auran mata, duk

wanda ya savawa sunnah ta ba ya tare dani.

Kuma lalle ne Haqiqa, mun aika waxansu manzanni daga

gabaninka, kuma muka sanya matan aure a garesu da

zuriyya” (Ra’ad: 38).

Don haka yin aure aikine da umarnin Allah, da aiki da da umarnin

manzonsa, da kuma samun jinqai da rabauta duniya da lahira. Kuma

yin aure bin hanya ce ta manzannin Allah, kuma duk wanda ya bi

tafarkin manzannin Allah ba shakka za a tashe shi da su ranar lahira,

kamar yadda a cikin aure akwai biyan buqata da farin ciki, da samun

kwanciyar hankali. Bugu da qari kuma a cikin yin aure akwai bayar

da kariya ga farji da tsare mutunci da runtse idanu, da nisantar fitina.

Kamar yadda a cikin aure akwai yawaita al’ummar musulunci, domin

ta hanyar yawaita ne al’umma za ta yi qarfi a rinqa jin tsoronta a

sauran al’ummomi, ta kuma samu ikon dogara da kanta matukar dai

tayi amfani da kowacce baiwa tata kamar yadda Allah ya umarce ta,

kamar yadda a cikin yin aure akwai tabbatar da alfahari da annabi tsira

da amincin Allah su tabbata a gare shi zai yi da al’ummarsa ranar

1 Imam Ahmad da Abu Dawud

75

alqiyama. Domin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a

gare shi yace:

Ku auri mata da kuke qauna kuma masu haihuwa, don

zan fi sauran al’ummomi yawan mabiya da ku a ranar

alqiyama1

Hakan nan a cikin yin aure akwai samar da iyali, da kusanto da

mutane da junansu, domin surukunta ‘yar uwar dangantaka ce. Allah

Maxaukin Sarki yace:

Kuma shine ya halicci mutum daga ruwa, sai ya sanya shi

nasaba da surukunta, kuma Ubangijinka ya kasance mai

ikon yi (Alfurqan: 54).

Hakan nan a cikin aure akwai samun lada da kyakkyawan sakamako,

ta hanyar tsayuwa da haqqoqin mata da ‘ya’ya da kula da su.

Kuma aure sanadi ne na samun wadata, da yawaitar arziki, ba

kamar yadda ‘yan jari hajja da masu raunin tawakkali suke riyawa ba,

kamar yadda Allah Maxaukakin Sarki ya faxa:

Kuma ku aurar da gwauraye daga gareku, da salihai daga

bayinku da kuyanginku, idan sun kasance matalauta ne

Allah zai wadatar da su daga falalarsa. Kuma Allah

Mawadacine, Masani (Nur: 32).

Hakan nan ya zo a hadisi da aka karvo daga annabi tsira da amincin

Allah su tabbata a gare shi mutum uku haqqin Allah ne ya taimake su

sai a cikinsu ya ambaci wanda ya yi aure da nufin kamewa (daga barin

zina)2

1 Abu Dawud da Ibn Majah

2 Sunan Albaihaqi

76

Hakan nan an ruwaito sayyidina Abubakar Assiddik yace: “ku yiwa Allah biyayya a cikin abin da ya yi muku umarni da shi na yin aure, shi kuma zai cika muku alqawarin da ya yi muku na wadata ku”. An

Karvo daga Ibn Abbas Allah ya yarda da su “Allah ya kwaxaitar da mutane akan yin aure ya kuma yi muku alqawari wadata dacewa: Idan sun kasance matalauta allah zai wadatar da su” (Nur 32). Haqiqa aure

sanadi ne na gyaruwar kowane mutum, kuma sanadi ne na gyaruwar

al’umma ta fuskar addini da kyawawan xabi’u, a rayuwarsu ta yau da

ta nan gaba. Kamar yadda yake hanyace ta kare fitintinu da ke iya

tasowa sanadiyyar barinsa ko rashin damuwa dashi a sanadiyar

abubuwan da ke iya hana mutum yinsa.

Ba shakka yana da muhimmanci matuqa mu mayar da hankali

wajen nazarin matsololi da ke hana mutane yinsa da nufin kaucewa

mummunan tasiri da rashin yinsa ke jawowa. Waxannan matsaloli za

mu iya cewa guda uku ne muhimmai:

Kauracewar da dama daga cikin matasa maza da mata daga

aure, to da yawa daga cikinsu za ka iske ba sa son aure da hujjar cewa

aure yana hana cigaba da karatu, ba shakka wannan hujja ce mai rauni

kasancewar aure ba shine abin da zai hana cigaba ba da karatu da

samun nasarar samun ilimi ba. Kai a maimakon haka ma yana iya

kasancewar wani taimako ne wajen yin hakan, domin kuwa a duk

lokacin da mutum nagari ya yi dace da mace tagari aka samu danqon

soyayya a tsakaninsu kowanne ya zamo abokin taimakawa abokin

zamansa wajen karatunsa, da magance matsalolin rayuwa, kuma sau

da yawa za ka samu yawancin mutane sunayin dace, kuma sau da

yawa matasa maza da mata Allah yana yi musu baiwa da su samun

hutu da kwanciyar hankali wajen karatun na su wanda hakan yana

taimakawa. Don haka ya kamata da matasan da suka ruxu da waccan

hujja su ake dubawa don su gyara kuskurensu, su kuma tanbayi

abokansu waxanda suka yi aure, suka kuma ga alheri da kwanciyar

hankali a sanadiyyar auren wanda da hakan ne wancan tunani; zai

gushe.

Hakan nan menene zai yiwa mace amfani idan ta kammala

karatun da ba ta da buqatarsa, wanda a sanadiyyarsa kuma sai ta rasa

77

jin daxin aure da rayuwa ba tare da haihuwa ba, ta wayi gari ba ta da

‘ya’yan da za su tuna da ita bayan mutuwar ta.

Matsala ta biyu:

Wacce takan hana aure da samun alfanu mai matuqar yawa da

ke cikinsa, ita ce ta qin aurarwa da waxansu azzaluman waliyyai kan

yiwa ‘ya’yansu da sauran wanda ke da haqqin waliccin aurar da su, ba

shakka irin waxannan waliyyai ba sa jin tsoron Allah, kuma ba su

kiyaye haqqin waxanda suke qarqashinsu ba, irin waxannan waliyyai

suna mayar da walittakar da Allah ya damqa a hannunsu ta zamo abin

neman abin duniya, ba shakka wannan cin dukiyane ta hanyar varna.

Kamar yadda zaka iske cewa a lokacin da wani wanda ya cancanta a

addininsa da mutuncinsa ya zo sai su ba shi uzurin cewa wani ya riga

shi, suna yin wannan qarya ne saboda ko dai wata mugunta a

zuciyarsu ko don neman abin duniya. Ba shakka qin amincewa da

wanda ya cancanta a addini da kyawawan halaye savawa Allah ne da

manzonsa kuma cin amana ne, kuma tozarta quruciyar mace ne, kuma

lalle Allah zai yi musu hisabi akan haka ranar da dukiya da ‘ya’ya ba

za su yi amfani ba sai wanda ya iske Allah da kuvutacciyar zuciya.

Yanzu don Allah ace irin waxannan waliyyai suna da tausayi

kuwa da son addini kuwa? Su yanzu ba za su auna su gani ba da za a

ce sune aka hana aurar waxanda suke so yaya za su yi? Shin wannan

kaxai bai ishe su su yi tunani ba a lokacin da suke hana ‘ya’ya su auri

wanda ya cancanta a addini da kyawawan halaye?

Yanzu ace waxannan irin waliyyai ba za su ji tsoron Allah ba a

irin wannan bala’i da suke jawowa kansu? Da irin bala’in abin da suke

jawowa waxanda suke qarqashinsu. Don haka ma’abota ilimi suka

samar da mafita daga irin wannan matsala inda suka ce: duk lokacin

da waliyyi ya qi amincewa ya aurawa yarinya wanda ya cancanta ta

kuma amince da shi to waliccin zai koma ga mai biye masa. Wato a

misali idan mahaifi ya qi aurar da ‘yarsa ga wanda ya cancanta ta

fuskar addini da kyawawan halaye to haqqin nasa zai koma ga wanda

ya fi kowa cancanta da waliccin bayan shi, don haka sai wanda ya fi

kowa kusanci da shi ya aurar da ita. Waxannan sun haxa da ‘yan

uwansa ko ‘yan uwan mahaifinsa ko ‘ya’yansu.

78

Ba shakka idan mai neman aure ya kasance bai cancanta ba, ko

dai ta fuskar addininsa da xabi’unsa kuma ta ce ta amince da shi, shi

kuma waliyin ya qi amincewa, to yana da haqqin yin hakan, kuma

babu laifi a kansa koda kuwa za ta ci gaba da zama babu aure ne har ta

mutu, domin qin amincewar tasa alfanunta ne da kuma sauke nauyin

amanar da take wuyansa.

Matsala ta uku: wacce take hana aure da samun alfanunsa mai

tarin yawa itace tsadar sadaki da kayan aure, wanda ako da yaushe

suke faman hauhawa har aka wayi gari aure ya zamo kamar wani abu

mai kamar wuya, ko mai matuqar wuya ga masu son yin aure ta yadda

sau da yawa mutum ba zai iya yi ba sai ya ci bashi, ta yadda zai zama

kamar bawan mai binsa bashi: Haqiqa hanyar warware wannan

matsala ita ce masu faxa aji daga cikin waliyyan ma’aurata su fahimci

babban maqasudin aure su kuma san matsayin mace wacce Allah ya

sa su waliyyai a kanta, su fahimci cewa mace ba kadara ba ce da za a

sayar ko aqi sayarwa gwargwadon abin da aka kashe mata kuxi.

Haqiqa aure ba ana yinsa ne da manufar samun dukiya ba, a

maimakon haka shi aure sanadiyya ce ta samun wadata.

Allah muke roqo ya kyautata halayen musulmi duk inda suke,

ya kuma azurta su da fahimtar addini da aiki da basira a cikinsa, ya

kuma sanya su zamo masu tsare koyarwar addininsu su zamo masu

girmama mata, masu tsayar da rukunan addini kamar yadda ya

kamata, lalle shi mai yawan kyautatawa ne mai karamci.

Ina wannan Magana tawa ina neman gafarar Allah tare daku

baki xaya da sauran musulmi maza da mata ku nemi gafararsa lalle shi

mai yawan gafara ne da rahama.

79

Huxuba ta biyu

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina kuma shedawa Muhammadu

bawansa ne kuma Manzonsa ne Allah ya yi daxin tsira da aminci, da

albarka a gare shi da alayensa da sahabbansa.

Yaku bayin Allah!

Ba shakka mace ba kadara bace, don ba shakka matsayinta ya

wuce na kadara, lalle ita amana ce babba, kamar yadda take wani

bangare na iyalin mutum don haka in muka yi tunani ta wannan

bangaren muka kuma kai ga haqiqanin manufa za mu ga cewa lalle

kuxi ba su da wata qima, don haka cika kuxin sadaki ko kayan aure

abu ne wanda bashi da wata hujja, don haka sai mu koma kamar yada

ake a zamanin manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare

shi kamar yadda sayyidina Umar yake cewa:

ya ku jama’a kada kuyi tsada wajen sadaki, domin da ace

hakan wata daraja ce a duniya ko taqawa da manzon

Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi ya fi

ku cancanta da yin haka. Manzon Allah tsira da amicin

Allah su tabbata a gare shi bai tava bayar da sadaki ga

xaya daga cikin matansa, kuma ba wacce aka tava bawa

sadaki daga cikin ‘ya’yansa da abin da yawuce auqiya

goma sha biyu ba, kuma ba shakka mutum ba zai gushe

yana biyan sadakin matarsa da tsada ba, har sai hakan ta

kasance dalilin tsanarta a zuciyarsa, har ta kaishi ya rinqa

cewa, lalle an xora min nauyi don har sai da na kusa

gazawa, ya kuma ce, sai da ya qarar da duk abin da ya

mallaka ciki har da igiyar rataya gorarsa.

Ba shakka idan muka koma ga yanayi na magabata na qwarai wajen

qaranta sadaki, al’amuran aure za su yi sauqi, albarkarsa ta yi yawa,

mata da maza kuma su amfana da yin hakan.

80

Kamar yadda tsauwalawa a al’amarin sadaki zai tilastawa maza

da mata da yawa su qauracewa aure ko su yi qoqarin haxuwa da juna

a waje, wanda yin hakan zai jawo masifu da wahalhalu masu yawa

waxanda ka iya kawo a sami sauyi na al’adu da yanayin

zamantakewar al’umma, kai a waxansu lokuta ma har da addini,

domin lalle cuxanya tana da tasiri matuqa wajen sauya waxannan

abubuwa.

Ya ku masulmai! Haqiqa akan sami da yawa daga cikin waliyyai

iyaye da waxansu da suke sharxantawa mai neman aure waxansu kuxi

da zai ba su, baya ga sadakin mace, to ba shakka yin hakan cin dukiya

ne da varna, domin kuwa shi sadaki gaba xayansa na macene. Allah

Maxaukakin Sarki yana cewa; “kuma ku baiwa mata sadakokinsu da saukin bayarwa” (Nisa: 4). sai ya jingina sadaki garesu. Sannan ya zo

a cikin hadisi daga annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi

yace: “Duk matar da ta yi aure bisa wani sadaki, ko alqawari kafin xaurin aure to nata ne, idan kuwa bayan xaurin aurene to na wanda aka bawa ne’’1

. Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah! Ku bi

umarninsa da yace ku ba mata sadakinsu, kada ku sharxantawa

kawunanku wani abu daga cikinsa, domin yin haka cin dukiyane ba

tare da haqqi ba, kamar yadda kuma wasane da waliccin aure, domin

matuqa waliyyi ya yi haka to zai janyo masa ya aurarwa wanda ya fi

bashi kuxi, ya yi watsi wanda bai ba shi ba don maslaharsa ba ta

wacce za a aurar ba, kuma ba shakka yin hakan cin amana ne da

ha’intar haqqin waliccci, don haka ku yi qoqarin sauke nauyin

amanar da take kanku ku kiyaye haqqin walicci.

Ya ku waxanda su ka yi imani; kada ku yaudari Allah da

manzansa kuma ku yaudari amanoninku, alhali kuwa

kuna sane (Anfal: 27].

Ina faxar wannan magana tawa ina neman gafarar Allah ga kai na da

ku.2

1 Albaihaki

2 Daga kundin hudubobin masallatai masu alfarma biyu, tattarawar Khairi Sa’id

81

82

10

Haqqoqin ‘Ya’ya Akan Iyayensu

Maza Da Mata

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya yiwa bayinsa baiwa ta dukiya

da ‘ya’ya, ya kuma sanya hakan ta zama jarabawa don ya tantace

waxanda za su tsaya akan sauke nauyin haqqoqinsu, ya kuma ba su

kariya daga lalacewa, ya ware waxanda za su barsu kara zube, su

zame musu asara a nan duniya da kuma ranar da za a halarto da kowa,

ina shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba

shi da abokin tarayya, mulki na sa ne kuma shine mai mulki da

karamci.

Kuma ina shedawa Annabi Muhammad bawansa ne kuma

manzonsa ne wanda yake shine mai kira zuwa ga gaskiya da shiriya,

tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi da alayensa da sahabbansa,

da waxanda suka biyo bayansu da kyaytatawa a magana da aiki da

aqida, Allah ya yi daxin tsira a garesu.

Bayan haka, ya ku mutane! Ku ji tsoron Allah, ku kuma

godewa ni’imar da ya yi muku ta waxannan ‘ya’ya waxanda Allah

ya yi muku da su, ku rene su ku koya musu ladabi bisa kyawawan

halaye, da aiyuka kyawawa, Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: ‘’Ya ku waxanda suka yi imani, ku karewa kanku da iyalanku, wata wuta wanda makamashinta mutane da duwatsu ne. a kanta akwai waxansu mala’iku masu kauri, masu qarfi, ba su savawa Allah ga abin da ya umarce su, kuma suna aikata abin da ake umarninsu” (Tahrim: 6)

Ya ku muminai! ku kare iyalanku ta hanyar buxe musu kofofin

alheri da fuskantar da su akansu, tare da qarfafa musu gwiwa akansu,

ku bayyana musu gaskiya da amfanin riqo da ita, ku kuma yi musu

umarni da riqo da ita ku bayyana musu qarya da cutarwar da take yi,

ku kuma tsawatar da su da su qaurace mata. Don ba shakka, ku masu

83

kiwo ne akansu, kuma duk wani mai kiwo za a yi masa tambaya

dangane da abin da aka ba shi kiwo. Ba shakka duk wanda ya kyautata

kulawa da su ya rabauta, duk kuma wanda ya gaza wajen kula da su

haqiqa ya halaka ya tave.

Sannan ku sanarda su ginshiqan imani, waxanda sune imani da

Allah, da mala’ikunsa, da littatafansa, da manzanninsa, da imani da

ranar qarshe, da qaddara alherinta da sharrinta, ku kuma ladabtar da

su akan lazimtar rukunan musulunci, waxanda su ne shedawa babu

abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma lalle Muhammad manzon

Allah ne, da tsayar da sallah da bayar da zakka, da azumin watan

Ramadan, da zuwa Hajji xakin Allah mai alfarma. Haka nan ku yi

musu umarni da sallah tun suna da shekara bakwai, ku dokesu in suka

qi yinta idan sun kai shekara goma.

Kamar yadda ya zama wajibi ku koya musu yadda za su yi

tsarki da yadda za su yi sallah da abin da za su faxa a sallar tasu,

waxanda za su aikata da kuma waxanda za su nisanta, ku kuma dasa

musu son Allah da girmama shi a zukatansu, ku kuma bayyana musu

ni’imomin Allah na fili da na boye kevantattu da gama-gari, don yin

hakan shi zai cusa musu son Allah da tuna ni’imominsa a zukatansu.

Haka nan ku dasa musu son annabi tsira da amincin Allah su tababata

a gare shi a cikin zukatansu, ku kuma bayyana musu abubuwan da ya

aikata na alheri babba ga al’ummarsa, sannan kuma lalle shine tsira da

amincin Allah su tabbaa a gare shi wanda ya wajaba a yiwa biyayya, a

kuma gabatar da sonsa da umarninsa akan kowanne abin halitta. Haka

nan kuma ku bayyana musu halayen annabi tsaira da amincin Allah su

tabbbata a gare shi da alayensa, da sahabbansa masu karamci, da irin

abubuwa da suka yi na ibada mai matuqar girma, da gagarumin aikin

da suka yi don tabbatar da Allah ya bawa addini musulunci nasara,

wanda hakan ne ya sa suka wuce kowa, duniya da na lahira, su ka

kuma jagoranci mutane ga aikata alheri har sai da mutanen suka shiga

addinin Allah qungiya qungiya saboda abin da suka gani na halayen

manzon Allah tsaira da amincin Allah su tabbata a gareshi da

sahabbansa ba tare da an tilasta musu ba.

84

Haka nan ya zama wajibi ku koyar da ‘ya’yanku faxar gaskiya

da aikata ta, idan kun tashi yi musu magana kada ku yi musu qarya,

idan kuma ku ka yi musu alqawari kada ku sava alqawuranku. An

ruwaito daga manzon Allah tsira da amincin Allah su kara tabbata a

gare shi yace: “Duk wanda yace da yaro zo gashi kuma bai bashi ba to ya yi qarya’’1 Domin matuqar kuma matuqar ‘ya’yanku suka ganku

kuna yin qarya to za su xauki qarya ba a bakin komai ba, kamar yadda

idan suka ga kuna sava alqawari hakan zai sa su xauki sava alqawari

ba a bakin komai ba.

Haka nan ku yiwa ‘ya’yanku horo akan kyautatawa bayin

Allah, da aiyuka na matunci ku yi musu gargaxi daga ta’addanci da

zalumci ku kuma dasa musu son muminai a zukatansu, ku nuna musu

cewa lalle mumini ga mumini kamar gini ne wanda sashensa yake

qarfafar sashensa, ku kuma nuna musu cewa abin daya zama wajibi ga

musulmi shine su zama al’umma xaya, don su taso akan sabo da juna,

da qaunar juna, da haxin kai. Ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah! ku

nemi ilimin fahimtar hukunce-hukuncen addininku, da tarbiyar

‘ya’yanku, ku tsayar da sallah. Ku yi salati ga ma’abocin muqami,

abin yabo ma’abocin tafkin da za a sha ruwansa, kamar yadda Allah

Madaukakin Sarki ya yi muku umarni da salati da sallama a gare shi

inda yake cewa: “Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56)

Ya Allah, ka yi daxin salati ga bawanka kuma manzonka,

annabinmu Muhammad da alayensa da sahabbansa. Ya Allah ka qara

yarda da shugabanmu Abubakar, da Umar, da Usman, da Ali da

sauran sahabbai baki xaya.

1 Musnad Ahmad da Sharhu assunnah na Baghawi

85

Hububa Ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina shedawa bubu abin bautawa

da gaskiya sai Allah shi kaxai yake bashi da abokin tarayya, kuma

annabi Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, Allah ya yi daxin

tsira da aminci da albarka a gare shi da alayensa da sahabbansa baki

xaya .

Bayan haka, lalle ya wajaba a gareku ku kwaxaitar da

‘ya’yanku da suka iya karatu akan karatun littafai masu amfani, da

suka hada da litattafai masu daraja kuma kuvutattu daga sauya

ma’anonin Alqur’ani da littatafan hadisi ingantattu na annabi tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi, irinsu littafin sheikh Abdur

Rahman As-sa’adi – Allah ya gafarta musu baki xaya, hakan nan

kuma litattafan tarihi ingantattu waxanda babu son zuciya a cikinsu,

musamman ma tarihin farkon musulunci kasancewar karanta tarihin

wancan lokaci zai qarawa mai karatu sanin halayen annabi tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi da sahabbansa, ya qarawa mai

karatu son su, tare da fahimtar addini da take qunshe a cikinsu, haka

nan ku gargaxe su daga karatun littatafai masu cutarwa, waxanda ka

iya yin illa ga aqidar musulmi, ko ibadarsu, ko halayensu, sannan

kuma da karanta jaridu, da mujallu masu vatarwa waxanda suke

kunshe da jefa shakku da motsa fitina, ko waxanda suka yi nazari na

wani al’amari na addini ta fuskar da bata dace ba.

Ba shakka karanta irin waxannan littatafai masu cutarwa na iya

yin tasiri ga aqidar mai karatu, da sauya yadda yake kallon abubuwa,

ba shakka waxanda za su kuvuta daga wannan sai waxanda Allah ya

yiwa baiwa da ilimi da hikimar ban-bance tsakanin gaskiya da vata,

abubuwa masu amfani da masu cutarwa.

Ya ku muminai! Lalle nauyin da Allah ya xora mana dangane

da al’amuran ‘ya’yanmu yana da yawa, mu iyaye, mazanmu da

matanmu, muna roqon Allah wanda shine ya xora mana wannan

nauyi da ya taimakawa mana, ya kuma yi mana dace wajen gyaruwa

da samun damar kawo gyara. Don ba shakka da za ace kowanne

mutum zai gyaru ya gyara iyalinsa da al’umma ta gyaru, domin

86

al’umma ba komai bace face xaixaikun mutane. Ina neman tsari da

Allah daga shexan la’ananne.

“Lalle Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90).

Ku godewa Allah bisa ni’imominsa sai ya qara muku, kuma lalle

ambaton Allah shine mafi girma, kuma Allah yana sane da abin da ku

ke aikatawa. Ina fadin wannan magana tawa ina neman gafarar Allah

gareni da ku.

87

11

Saki Shine Ke Rushe Gidajen Aure

Godiya ta tabbata ga Allah, muna neman taimakonsa, muna neman

gafararsa, muna kuma neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu,

da miyagun aiyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar haqiqa shine

shiryayye, wanda kuma ya vatar ba mai shiryar da shi, kuma ina

shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ina shedawa

Shugabanmu annabi Muhammadu bawan Allah ne kuma manzonsa

ne, ya isar da saqo ya sauke, nauyin amfana, ya yiwa al’umma nasiha

ya yi jihadi wajen xaukaka addinin Allah matuqar jihadi ya barmu

akan hanya mai haske wacce hasken darenta dai-dai yake da na

ranarta, ba wanda zai kauce daga tafarkinta sai halakakke. Allah ya yi

daxin tsira da albarka bisa alayensa da sahabbansa da mabiyansa da

wanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka, ya ku waxanda suka yi imani ku ji tsoron Allah

haqiqa nin jin tsoron sa kuma kuyi riko da addinin musulimci wanda

shine igiyar da bata tsinkewa, kuma ku nisanci duk wani nau‘ina sabo

ku sani cewa kafafuwan ku ba za su iya jurewa azabar wuta ba, kuma

ku sani cewa, mala’ikan mutuwa sai da ya qetare ku ya tafi ga

wasunku, kuma ba shakka wata rana zai tsallake waxansu ya iso gare

ku don haka ku zauna cikin shiri. Mai wayo shine wanda ya yiwa

kansa hisabi, yayi aiki domin abin da zai biyo bayan mutuwa,

kasashshe kuwa shine wanda ya biyewa son zuciyarsa ya rinqa yiwa

Allah buri,

Ya ku bayin Allah! a kullum aka wayi gari sai an bada labarai

da ke bayyana haqiqanin rayuwar da mutane suka tsinci kansu a

cikin, ta halin ko-in-kula da ladubban magana da taka-tsan-tsan da

abin da magana za ta haifar ta yadda za ka ga kalmomi suna ta faman

fitowa daga bakunan mutane amma su ba abin da ya dame su, irin

kalmomin da sau da yawa su kan iya jefa su cikin hanyoyin vata da

88

zubewar mutunci, kamar yadda za ka ga ba a xauki kalmomin a bakin

komai ba, don haka ba a waiwayawa a dubi abin da suka qunsa, irin

waxannan mutane ba su san cewa ba “Lalle wuta da tsinken ashana akan kunna ta, kamar yadda komai girman yaqi farkonsa magana ce’’ Ya ku mutane! Yanzu za ku yi mamaki idan aka ce muku kalma

xaya rak za ta iya zamowa gatarin da zai iya wargaza gidaje? ya lalata

zamantakewar aure? Shin za ku yi mamaki idan aka ce muku kalma

xaya na iya sauya rayuwar mai ita, daga rayuwa mai daxi da

kwanciyar hankali ta jefa shi cikin tashin hankali da bala’i? Shin

xayan ku zai yi mamaki idan aka ce masa akwai wata kalma guda

xaya da za ta iya motsa xaixaiku da jama’a ta haifar da buqatar a yi ta

ban baki da neman alfarma kafin a warkar da raunin da ta haifar?

Ba shakka wannan kalma itace ta kansa idanuwa kuka, ta sanya

zukata su yi baqin ciki, ta tsoratar da su, ba shakka wannan kalma ‘yar

qarama ce sai dai abin da ta qunsa yana da girma, ba shakka wannan

kalma ta kan jefa kunnuwa cikin tsoro saboda tsananinta, ta mayar da

farin ciki ya koma baqin ciki, ta mayar da murmushi ya koma yaqe,

ba shakka wannan kalma itace kalmar saki, itace saki, ko ka san

menene saki? Ita kalmar saki itace kalmar bankwana, ta rabuwa ta

rikici ta vatawa da juna. Don Allah ku bani labarin gidaje nawa

wannan kalma ta rusa, danqon zumunta nawa ta raba, da ke tsakanin

‘yan uwa da masoya. Wayyo Allah saki wane irin lokaci ne na tashin

hankali haka nan lokacine na baqin ciki, ranar da mace za ta ji da

kunnuwanta cewa an sake ta, ta share hawayenta ta yi bankwana da

mijinta, kai wannan lokaci ne damuwa wanda a lokacin ne kumatun

mace zai bushe, a lokacin da za ta tsaya a kofar gida don ta yi masa

kallo na qarshe, ta yi masa duba na bankwana, da ba za a manta da su

ba, kai wannan lokaci ne na baqin ciki a lokacin da kwanciyar hankali

za ta naxe tabarma daga farfajiyar wancan gida na musulmi mai

albarka.

Ya ku bayin Allah ; ba shakka zamantakewar aure wani nau’ine

na musamman na soyayya da ke zuciya, wanda a duk nau’oin soyayya

ba shi da abokin haxi, kasancewar shine abin da ke sa kowanne daga

cikin ma’aurata ya sami natsuwa, wanda kuma a sanadiyyarsa ‘yan

89

adam biyu su ke haxuwa ta yadda da kowanne xaya daga cikisu zai

cike gurbin da xan uwansa ya gaza, kamar yadda haxuwa da za ta kai

ga samar da wani mutum irinsu “kuma Allah ya sanya muku matan aure daga kawunanku, kuma ya sanya muku daga matan auren ku xiya da jikoki kuma ya azurta ku da abubuwa masu daxi, shin fa da qarya suke yin imani, kuma da ni’imar Allah suke kafirta? (Nahl: 72)

Ba shakka lalacewar zamantakewar tsakanin ma’aurata ta kan

kunna wutar rabuwa, yawan faxace-faxace kuma ya qara rura ta, don

da ce ma’aurata za su so junanasu so na gaskiya, kuma ko wane daga

cikinsu ya shaqu da xan uwansa da an sami qauna a tsakaninsu wanda

a sanadiyyar hakan zai qaunaci iyalin xan uwansa, domin kuwa qauna

tsakanin ma’aurata na daga cikin zamantakewa wanda hakan zai jawo

danqon zumunta tsakanin dangin kowannensu a sami danqon qauna

tsakanin ma’aurata da dangin junansu. Haka nan irin wannan danqon

zumunci shine abin da zai mamaye tunanin al’umma. Don haka duk

wani abu da za a samu na daidaito a tushen ginin al’umma zai kawo

natsuwa da kwanciyar hankali a tsakaninsu baki xaya, kamar yadda

duk wani abu da ka iya kawo barazana ga zamantakewar aure zai

zamo barazana ce gare su baki xaya, ya cutar da su ya kai su ga

halaka, haka nan kuma duk wanda bashi da alheri ga iyalinsa, ba zai

zamo alheri ga al’umma ba. Manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gareshi yace:

Mafi alherinku shine mafi alheri, ga iyalinsa kuma ni nafi

ku alheri ga iyalina, Tirmidhi ya fitar da shi da isnadi

ingantacce.

Ya ku bayin Allah! Haqiqa Manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gareshi ya faxa a shahararren hadisinsa: “ka zavi ma’abociyyar addini sai ka ga albarka” Bukhari da Muslim.

Ba shakka wannan mace ita ce wanda shari’ah ta kwaxaitar da a

nemi aurenta, ta kuma yi addu’a mara kyau ga wanda ya nemi auren

wacce ba irintaba, ya nuna ba ya sonta ya qyale ta.

90

Kuma abu ne sannanne ga kowa cewa ba ta yadda za a yi

zuciyar musulmi ta nemi mai addini har sai shi kansa ya kasance

zuciyarsa tana danfare da addini ya kasance kuma zuciya ce mai

tsarki, wanda kuwa yake da irin wannan hali ba makawa za a azurta

shi da qauna da soyayya tsakaninsa da matarsa, domin kuwa hakan na

daga nau’in kasancewar sai hali ya zo xaya ake abota, ta hanyar yin

kama da juna a xabi’u da siffofi masu kyau. Wanda kuma savanin

haka shine na kama da juna a munanan siffofi da halaye na kaskanci

waxanda ba za su samar da soyayya ko qauna ba.

Manzon Allah tsira da amanincin Allah su tabbata agareshi

yace:

Mafi alherin daxin duniya itace mace ta qwarai” Muslim

ya ruwaito shi. Hakan nan matuqa akwai addini a wajen

miji da matarsa to duk irin savawar da suka samu, da

yadda suka juyawa junannsu baya, da irin yadda

zukatansu suka yi qunci, to ba shakka sai sun sami

hanyar warware kowanne irin rikici, don babu wanda zai

tsaurara addini face ya yi galaba akansa, shi kuwa

addinin sauqine da tausasawa da rahama da yafiya,

kamar yadda yake kulawa da riqon alqawari da xaukakar

mutunci da nisanta shi da duk abin da zai iya kaiwa ga

rage daraja ko qaskanta. Haka nan duk wanda waxannan

suka zamo halayensa to ba shakka, ba zai tava qasa a

gwiwa wajen aikata abin da ake yi masa umarni da shi a

cikin fadar manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shiba ‘’Da ace zan umarci wani ya yiwa wani sujjada da na umarci mace tayiwa mijinta sujjada’’ Tirmidhi ya fitar da shi kamar yadda ya zo a

ingantattacen hadisi, da inda yake cewa “Ina yi muku wasiyya da ku riqe mata da alheri” Bukhari da Musulim

sun haxu akansa. Haka nan sakamakon addinin mace

yana bayyana ne a irin abin da ya zo a cikin hadisi

sayyidatina A’isha Allah ya yarda da ita wanda a cikinsa

91

take cewa: “Ya ku jama’a mata da ace kun san haqqoqin da mazanku suke da shi akanku da xaya daga cikinku ta rinqa share qafar mijinta da sararin fuskarta

Ba shakka, babu wautar da ta kai miji ya rinqa munanawa matarsa,

kamar yadda ba shashancin da ya kai mace ta munanawa mijinta.

Don haka, ku ji tsoron Allah ya ku bayin Allah! Kuma ku nemi sanin

hukunce-hukuncen addinininku da zamantakewarku ta aure.

Ku yi salati da sallama -Allah ya yi muku rahama – ga

fiyayyen wanda ya tsayar da sallah, ma’abocin muqami abin yabo, da

kwari wanda za a sha ruwansa, kamar yadda Allah ya yi muku

umarni da yi masa salati da sallama inda yake cewa: “Lalle Allah yana yin umarni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl:90) Ya Allah ka yi salati da aminci

ga bawanka kuma manzonka annabinmu Muhammad da alayensa da

sahabbansa. Ya Allah ka yarda da khalifofinsa shiryayyu,

shugabanmu Abubakar, da Umar, da Usman da Aliyu da sauran

sahabbai baki xaya.

92

Huxuba Ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina shedawa babu abin bautawa

da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya, ina kuma

shedawa lalle shugabanmu Annabi Muhammad bawansa ne manzonsa

ne, Allah ya qara tsira da albarka a gare shi da alayensa dasahabbansa

baki daya,

Ya ku mutane! Lalle saki kalma ce ba wanda zai yi musun

muhimmancinta da buqatar ta da ma’aurata ke da ita a lokacin da

rayuwa qarqashin inuwa xaya ta gagara, a lokacin da tsanar juna ta

kai mutuqa ta yadda zai yi wuya asami qaunar juna, to ya zama wajibi

su rabu bisa kyautatawa, cikin mutumci kamar yadda suke hulxa don

cimma waxancan manufofi ta gagara.

Kuma in sun rabu Allah zai wadatar da kowanne daga

yalwarsa, Kuma Allah ya kasance Mayalwaci Mai

hikima [Nisa’i: 30]

Kuma haqiqa Allah bai halicci ma’aurata da xabi’a iri xaya ba don

haka duk ma’auratan da suke zaton cewa su halittu ne dai-dai da juna

to ba shakka suna yin rayuwace ta mafarki domin idan ba haka ba ta

yaya miji zai yi tunanin cewa mace ta yi tunani da irin hankalinsa. Ko

ita ta yi zaton cewa ya yi tunani da yadda take ji a zuciyarta. “Kuma su matan suna da kamar abin da yake kansu, yadda aka sani. Kuma maza suna da wata daraja akansu (su matan)” (Baqarah: 228)

Haka nan ba ta yadda za a yi ace koda yaushe ana cikin zaman jin

daxi cikakke, don ba shakka wata rana sai an sami savani, guguwa ta

turnuqe. don haka sa rai da cikakkiyar kwanciyar hankali nau’i ne na

ruxin kai, don haka alamar hankali itace shirin jurewa yanayi mara

daxi da akan iya shiga tare da kaucewa yawan qorafi akansa.

“sa’annan idan kun qi su, to akwai tsammanin ku qi wani abu alhali

93

kuwa Allah ya sanya wani alheri mai yawa a cikinsa” (Nisa’i: 19)

Kuma manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a

gareshi yace:

Kada munini ya tsangwami mumina domin kuwa idan

ya qi wani hali na ta to zai amince da wani, Muslim ya

ruwaito. Wani mawaqi yana cewa:

Duk wanda yake bibiyar laifuka da nufin lalubosu, to ba

zai tava yin aboki ba har abada.

Kamar yadda zaka ga gidaje da yawa waxanda suka rasa ruhin addini

sun auka cikin muguntar juna, da qunci, matsalolin suka lulluve su ta

fuskar tunani da halaye da zamantakewa, kamar yadda an wayi gari a

yau, ana iya sakin mace a kan ma’auni xaya na nama wanda mijin ya

xamfara sakinta da shi in ta saya, ta yadda za ka ga waxannan suna

tafiya cikin duhu, suna aiyuka irin na wawaye, su rinka faxawa cikin

savon Allah, da zalunci. Kuyi salati da sallah –Allah yayi muku

rahama ga fiyayyen wanda ya tsayar da sallah, ma’abocin muqami

abin yabo, da tafki abin sha kamar yadda Allah yayi muku umarni da

hakan inda yake cewa:

Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, ya ku

waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku

yi sallama domin amintarwa a gare shi (Ahzab: 56).

Ya Allah ka yi salati da sallama ga annabi, da sauran sahabbai baki

xaya.

94

12

Yawaitar Saki Ce Take Lalata Rayuwar Aure

Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu, wanda ya raya zukatan

muminai da Alqur’ani da sunnar shugaban manzanni, Godiya da yabo

sun tabbata ga ubangijiinmu, bisa wannan falala bayyananniya, Ina

kuma shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake

bashi da abokin tarayya, mai iko kuma mai cikakkan qarfi, Ina kuma

shedawa annabinmu da shugabanmu Annabi Muhammad bawansa ne

kuma manzonsa ne, mai gaskiya da cika alqawari, ya Allah ka yi

daxin tsira, da aminci, da albarka ga bawanka kuma manzonka

Annabi Muhammad da alayensa da sahabbansa baki xaya.

Bayan haka! Ku ji tsoron Allah haqiqanin jin tsoron Allah, ku

kuma yi riqo da shiryarwar manzon Allah wanda ya xaukaka, ya ku

musulmai.

Ku sani cewa tsiran musulmi, da yin kyakkyawan qarshensa, da

samun kwanciyar hakalinsa, a duniya da lahira suna samuwane ta

hanyar yiwa kai hisabi, da tilasta ta akan bin abin da Allah yake so, da

nisanta da fushinsa. Allah Madaukakin Sarki yace:

Ya ku waxanda suka yi imani, ku bi Allah da taqawa

kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma

ku bi Allah da taqawa. Lalle Allah mai kididdigewane ga

abin da kuke aikatawa” (Hashr: 18). Hakanan manzon

Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi yace:

“halal xin da Allah ya fi qi shine saki”

95

Ya ku bayin Allah! haqiqa saki ya yi yawa a yau, a sanadiyyar rasa

tsayuwar namiji a cikin waxansu al’ummomi masu yawa, wannan

kuwa ya biyo bayan gafala da aka yi da ginshiqin hukunce-

hukuncensa, wato littafin Allah da sunnar manzonsa da waxansu

mutane suke yi suka koma dogaro da waxansu littatafai gurvatattu

waxanda suka sauya haqiqan salon zamantakewa, suka lalata

zamantakewar aurensu ba tare da sun sani ba. Kamar yadda kafafen

yaxa labarai suka xauki kaso mai yawa na wannan lefi ta fuskoki

daban-daban na kallace kallace da ake yi koda yaushe, su kuwa sai

suka yi amfani da damar wajen cusa tunani mara kyau, da ra’ayoyi

jirkitattu dangane da zamantakewar aure, wanda hakan ya jawo mata

suka manta da tarihinsu.

Sau da yawa za ka iske akwai wani abin kallo wanda mata dubu

za su kalle shi a lokaci xaya, wanda da zarar ya zauna cikin

qwaqwalarsu ya kuma mamaye tunaninsu, sai su wayi gari ba su da

ikon zavi, a cire musu duk wata natsuwa, su wayi gari suna

kwaikwayon abin da suka gani dubunnan lokuta ta hanyoyin daban-

daban, a dubunan yanayi, don haka kada kuyi mamaki bayan haka

idan mai doki ya koma kuturi, namiji ya wayi gari ya koma mace, kai

wani abin mamaki ma waxansu daga cikin kafafen yaxa labarai suna

shelanta cewa gudunmawa suke ba mace, kuma riga kafi suke bata,

irin wanda za a yiwa mutum allura da waxansu qwayoyin cuta don

gar kuwar jikinsa ta saba da su, ta yadda a lokacin da annoba ta zo

garkuwar jikin ta riga ta gane su don haka sai taba jikin kariya. Amma

a haqiqanin al’amari babu abin da suke qarawa da waxannan

abubuwa da suke da’awar magancewa sai tsanani, domin kuwa

wannan abin da waxannan kafafen yaxa labarai suke, ba komai ba ne

face haikewa annoba a lokacin da take kan ganiyarta.

Ba shakka wani mai magana yayi gaskiya da yake cewa:

Ashe magani na cutarwa yake yi, kamar yadda mashayin

giya kan yi maganin shan giya da shan giya.

96

Haqiqanin abin da yake faruwa a yau ya ku muslmi shine, cikin

gidajen musulmi suna tasirantuwa da waje, kamar yadda kowacce

guguwa ta taso da ta shafi sakaci da addini, da jahilci ta taso a waje sai

ta yi naso ta shiga cikin gidaje ta yadda ba wanda zai kuvuta daga

bala’inta sai wanda Allah ya kare.

Ya kuma kamata mu sani cewa, rayuwar aure rayuwace ta

zamantakewar al’umma, don haka ya zama tilas kowacce al’umma ta

kasance ta na da shugaba da za a koma wajensa a duk lokacin da aka

yi savanin ra’ayi ko bukata ta taso, kuma ba shakka namiji ya fi

cancanta da wannan shugabanci domin shine ya fi sanin maslaha, ya fi

iko wajen aikata abubuwa, saboda abin da Allah ya yi masa baiwa da

shi na ikon yin hakan.

Kuma ba shakka, irin waxannan abubuwan da mace take koya a

yau daga abubuwan da suke faruwa a maqotanta na hamayya da

namiji a haqqinsa na jagoranci na daga cikin sakin hanya

madaidaiciya da vata bayyananne.

Kamar yadda jagorancin namiji a gidansa ba ya nufin cewa an

bashi haqqin yin kama-karya, da nuna fin qarfi domin kuwa aure ba

alaqa ce ta bauta ba, kamar yadda ba alaqa bace ta cin moriyar jikin

mace, Ba shakka al’amrin ya wuce haka. Haka nan kuma kowanne

daga cikin ma’aurata mutum ne cikakke, yana da hankalin da zai yi

tunanin da shi da zuciya da yake so ko qi da ita, don haka ya zama

wajibi a ba mace haqqinta duk da cewa miji shine shugaba akanta.

“Kuma su matan suna da kamar abin da yake kansu, yadda aka sani“ (Bakara: 228)

Kamar yadda shugabancin namiji baya nufin ya wadatar da shi

daga matarsa, Allah Madaukakin Sarki yana cewa: “Su tufane a gareku kuma ku tufane a garesu” (Baqara: 187).

Kuma ba shakka sakin mata da ake yi ya yi yawa a yau, kamar

yadda yawancin masu saki xayan biyu ne, ko dai mutumin da ya yi

aiki da ikon da yake da shi ya yi watsi da tausayi, ya wayi gari a

gidansa shugabane mai mulkin kama-karya kawai wanda ba zai

xanxani soyayya da kwanciyar hankali ba, ballantana zaman gaskiya

da jin daxi.

97

Ko kuma mutumin da ya biyewa son zuciyarsa ya yi watsi da

nauyin shugabancin da yake kansa, ya wayi gari a gidansa ya zamo

bawa. Kamar yadda saki ya yi yawa saboda hassada da munafunci da

suka yi yawa, waxanda suka jinkirta xabi’u suka sauya yanayi, suka

mayar da qauna da haxin kai suka zamo daliline na qiyayya da

rabuwar kai. Sau da yawa za ka iske ‘yan uwan ma’aurata suna da

waxansu dalilai na bayyane da ke iya zamowa sababi na kai tsaye na

faxawa cikin rikice-rikice a waxansu lokuta uba ko uwa ko xan uwa

ko ‘yar uwa kan iya shishshigi cikin al’amarin ma’aurata wanda hakan

zai sa miji ya shiga ruxanin wanda zai goyi baya, shin iyayensa

newaxanda suka haife shi jariri, suka yi renonsa tun yana yaro

qarami? Ko matarsa wacce ta qauracewa gidansu da ‘yan uwanta da

mahaifanta duk dominsa.

Ba shakka irin waxannan matsaloli suna da wahalar warwarewa

komai qanqantarsu,

Ba shakka wannan shishshigi a cikin gidajen aure shine ke

zama barazana, ga da yawa daga cikin gidajen aure, yanzu don Allah

waxannan mutane kome suke nema da za su yi ta faman kai hari ga

gidajen aure? su rinka shigowa gidaje ta bayan gida? su kekketa

suturarsa su da alfarmar hijabansa, su wargaza zamantakewarsa su

jefa ma’aurata cikin qiyayya da juna?.

A haqiqanin gaskiya, irin waxannan mutane suna da

mummunan tasiri ga gidajen aure, waxanda sune suke haxuwa su

samar da al’umma. Ba shakka duk wani mai hankali ba zai gaza

fahimtar cewa sharrinsu sharrine da yake iya shafar kowa ba, haka nan

abin da suke aikatawa fitina ce a ban qasa da varna babba.

Ya ku bayin Allah!

Ba shakka alaqar aure, alaqace mai qarfi, kuma mai nisan zango, don

haka Allah ya yi rahama ga dukknan mutumin da ya ke kyakkyawan

hali, mai tsarkin zuciya, mai sauqin hali da tausayi, da jinqai, mai

tausayin iyalinsa, wanda ba ya xorawa mace abin da ya fi qarfinta.

Haka nan Allah ya yi albarka ga matar da ba ta neman mijinta ya yi

98

abin da ya fi qarfinsa, ba ta yi masa magana ta gatsali, manzon Allah

tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi yace: “lalle mafi sharrin mutane a wurin Allah ranar alqiyama shine mutumin da zai san sirrin matarsa, ita ma ta san sirrinsa sannan kuma ya rinqa yaxa shi’’ Abu Dawud ya rawaito. Manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi yana cewa: “Idan mace ta sallaci salloli biyar, ta kikaye farjinta, ta yi biyayya ga mijinta, za ta shiga aljanna ta duk qofar da ta ga dama “ Ibn Hibban ya ruwaito.

Daga waxannan abubuwa za a fahimci cewa miji ba shi da

wanda ya fi dacewa da ya kasance abokinsa a rayuwasa, ya nemi

taimakonsa wajen sauke nauyin da yake wuyansa, kamar mace mai

kyakkyawar zamantakewa mai nagartattun xabi’u, wacce idan ya

kalleta zai yi farin ciki, ta yi masa biyayya idan ya yi mata umarni,

kuma ba za ta bari ya ga wani abu da baya so a kanta da dukiyarsa ba,

lalle irin wannan matar itace ginshiqin gida mai daxin zama kamar

yadda itace tushen tsayuwarsa.

Salihan mata masu xa’ane, masu tsarewa ga gaibi saboda

abin da Allah ya tsare (Nisa’i: 34).

Ya ku mutane! sau da yawa kowanne xaya daga cikinmu ya kan

tsinci kansa a yanayin da shi kansa bai amince da halin da yake ciki

ba, sai dai kawai ya jure, ya kuma bawa kansa uzuri gwargwadon

yadda zai zo masa, don haka ya kamata itama zamantakewar tsakanin

ma’aurata ta zamo haka, ta yadda kowanne daga cikinsu zai nemawa

xan uwansa mafita. Don ba shakka mumini a kullum shine yake nemo

uzuri, shi kuwa munafuki sai dai ya nemo kura-kurai, don haka ya

zama tilas a kauda ido daga kura-kurai in har ana son zamantakewa ta

yi dai-dai. “Ko akwai wanda bai taba kuskureba? wanda ko yaushe yake yin dai-dai”.

Kamar yadda babu abin da zai sauqaqa matsalolin rayuwa da

wahalhalu ga ma’aurata kamar junansu, kamar yadda ba wanda zai

rage raxaxin masifar da ta same shi ga kansa, ko waninsa kamar

matarsa, ga mace kuma mijinta, domin da haka ne wanda masifar ta

99

aukawa zai ji cewa yana da wani mutum na daban da zai qara masa

qwarin gwiwa ya xauke masa rabin nauyin masifar da ta auka masa.

Mu duba yadda uwar muminai Khadija Allah ya qara yarda da ita,

matar manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, yadda

ta zame masa kamar zuciyarsu xaya take a duk lokacin da wata masifa

ta same shi, ta kasance gareshi kai kace ba ta tava cewa babu ba, in

banda a kalmar shahada. Kamar yadda ba ta gushe ba tana qarfafarsa,

da kwantar masa da hankali kai kace a kullum haifar masa da sabon

farin ciki take yi saboda tausasassar zuciya, ta yi amfani da dukiyarta

wajen tallafa masa ta yi amfani kalamanta wajen xauke masa kewa da

cewa: “Ko kaxan wallahi Allah ba zai tava tozarta ka ba, domin kana sada zumunta, kana faxar gaskiya, kana xaukar nauyin talaka, kana kuma taimako bisa mastalolin rayuwa’’. Bukhari ya ruwaito.

Allah ya yi min albarka, ya yi muku albarka, a cikin fahimtar

Alqur’ani mai girma. Ina faxin wannan maganar tawa ina neman

gafarar Allah a gareni da gare ku, da kuma sauran musulmai maza da

mata ku nemi gafararsa zai gafarta muku domin lalle shi mai gafara

ne.

100

Huduba ta biyu:

Godiya ta tabbata ga Allah godiya mai yawa mai kuma tsarki da

albarka kamar yadda yake so, kamar yadda nake shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah, ina kuma shedawa lalle annabi

Muhammad bawansane kuma manzonsa ne, zavavve daga cikin

halittunsa kuma badaxinsa, tsira da amincin Allah su tabbata a gare

shi da alayensa da sahabbansa, da waxanda suka biyo bayansa har

zuwa ranar sakamako.

Bayan haka,

Anas xan Malik ya ruwaito hadisi daga mahaifiyarsa Ummu

Sulaim’yar Malahan Al-ansari Allah ya yarda da su yace: “wani xan uwa nawa ya yi rashin lafiya xan gidan Abu Xalhatu wanda ake kira da suna Umair a lokacin da abu Xalhatu baya nan sai yaronsa ya rasu, don haka sai Ummu Sulaim ta haxa shi, ta kuma ce kada ku bawa Abu Xalhatu labarin xansa ya rasu, ana haka sai ga shi ya dawo daga masallaci a lokacin kuma ta yi kwalliya, ta yi ado sai yace: Ko yaya xana yake? sai tace ai tunda yake bai tava samun natsuwa kamar ta yau ba, ta kawo masa abincin dare suka ci shi da abokansa, sannan ya je suka kwanta da ita cikin yanayi mafi cika da shaquwa da juna na tsakanin ma’aurata. Can da dare ya kawo qarshe sai tace da shi, ko menene ra’ayinka dangane da waxansu mutane da suka karvo aron wani abu, bayan sun yi amfani da shi sai masu kayan suka nemi su dawo musu da shi, sai suka nuna rashin jin dadi sai yace ‘’Lalle ba su yi adalci ba.sai tace ‘’To lalle wannan xa naka arone daga Allah, to yanzu kuma ya karvi kayansa. Nan take sai ya yi inna lillahi wa inna ilaihi raju’un ya yi wa Allah godiya” Ya kuma ce ba zan bari ki rinjaye ni a wajen haquri ba. Da gari ya waye sai ya yi sammako wajen manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, a lokacin da ya ganshi sai yace:”Allah ya yi muku albarka a darenku “

Bukhari da Musulim sun haxu akansa.

101

Allahu Akbar! Da irin wannan ne ya kamata ma’aurata su rayu,

da irin wannan ne ya kamata a yi rayuwa ta kwanciyar hankali da jin

daxi a zuciya da ‘ya’ya da dukiya. Sannan ku sani -Allah ya yi muku

rahama-’cewa kowanne daga cikin ma’aurata yana da haqqi akan xan

uwansa. Haqqine akan miji ya kula da ita, kada ya xora mata wani

abu sai wanda za ta iya, ya kuma zaunar da ita a gida wanda ya dace

da irinta, ya ilmantar da ita, ya tarbiyantar da ita ya kuma yi kishinta

ya bata kariya kada kuma ya ha’inceta, kada kuma ya rinqa nemo

laifukanta, ya kuma yi mata mu’amala ta kirki, manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa: “ina yi muku wasiyya da riqe mata da alheri” Bukhari da Musulim sun haxu akansa.

An kuma tambaye shi menene haqqin matar xayanku akansa;

sai yace ‘’ka ciyar da ita idan ka ci ka tufatar da ita idan ka tufata kada

ka doki fuska kada kace mata mummuna kada kuma ka kaurace mata

face a gida ‘’Abu Dawud ya rawaito shi.

Haka nan yana daga cikin haqqin miji akan matarsa, ta yi masa

biyayya a abin da bai savawa shari’a ba, ta kuma bi shi gidansa, kada

ta yi azumin nafila sai da izininsa, kuma kada ta yiwa wani izini da

shiga gidansa sai da izininsa, kuma kada ta fita ba tare da izininsa ba,

ta gode masa bisa ni’imominsa, kada ta musa su, ta tsare masa

addininta da mutuncinta, manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gareshi yace: “Duk matar da ta rasu alhali mijinta yana mai yarda da ita za ta shiga aljanna’1’. To wannan kenan, ku yi salati -Allah ya yi muku rahama- ga

fiyayyen halitta wanda yafi kowa a cikin mutane, kamar yadda Allah

ya yi mana umarni da haka. “Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, Ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56)

1 Tirmidhi da Hakim

102

13

Waliccin Mahaifi Nau’i Biyu Ne Na Yin Dole Da Na Izini

Godiya ta tabbata ga Allah, muna neman taimakonsa, muna neman

gafararsa, muna kuma neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu,

da miyagun aiyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar haqiqa shine

shiryayye, wanda kuma ya vatar ba mai shiryar da shi. Ina shedawa

babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad

bawansa ne kuma manzonsa ne. Bayan haka ya ku bayin Allah ku ji

tsoron Allah, haqiqanin jin tsoronsa ku kuma kiyaye dokokinsa a

sarari da voye.

Ya ku musulmai! Lalle Allah ya karrama xan adam a cikin

waxanda ya halitta ya fifita shi, ya kuma zavi waxanda ya fifita daga

cikinsu da annabta, da manzanci, daga cikin waxanda kuma ya fifita

mafificinsu shine annabi Muhammad xan Abdullah ya saukar masa da

wahayi dangane da haqqin xan adam da cewa: “kuma akwai daga ayoyinSa Ya halitta muku matan aure daga kanku, domin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya sanya soyayya da rahama a tsakaninku. Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga mutane masu yin tunani” (Rum: 21)

Kuma Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (Nisa’i:1)

Ya ku bayin Allah! abin da ake nufi da wallicci a shari’a shine

zartar da wani abu da aka faxa akan wani ba tare da banbancin cewa

ya amince ko bai amince ba shi kuwa waliyyi shine wanda zai aiwatar

da hakan, ya kuma tilastawa wani akan haka, daga cikin wannan

akwai abin da yazo faxar Allah Maxaukakin Sarki: “To idan wanda

103

bashi yake kansa ya kasance wawa ko kuwa rarrauna, ko kuwa shi baya iya shinbta, to sai waliyyinshi ya yi shibtar da adalci “ (Baqara:

282).

Hukunci waliyyi a xaurin aure shine sharaxi na tilas na

ingancin xauruwar aure. Don haka baya halalta ga mace ta aurar da

kanta, ko ta yi waliccin xaurawa wata aure, ko ta wacce fuska

budurwa ce ita ko bazawara, mai daraja ko qasqantacciya, mai hankali

ko kwarkwar, ‘ya ce ko baiwa, waliyyinta ya yi mata izini, ko bai yi

mata ba. In kuwa aka ce ta xaura auren to sai an warware shi, ko an

sadu da ita ko kafin saduwa, koda kuwa an daxe har an haifi ‘ya’ya.

To amma sai dai ba za ayi haddi akansa ba, saboda shubuha in kuma

an sami ‘ya’ya na mahaifinsu ne, za a kuma bayar da sadaki da aka

ambata in kuwa ba a ambata ba sai a bayar da sadakin irinta. Kamar

yadda hukuncinsa, irin na aure ingantacce ne ta fuskar wajabcin idda

da haramtawa mijin ‘yan uwansa na surukuntaka, da haxuwar

dangantaka. Dangane kuwa da gado, kafin a warwareshi an yi savani.

Maganar da ta ke cewa babu gado magana ce ta malam Asbagh kuma

maganace mai rauni.

Ibn al-mundhir yace: “ya tabbata daga manzon Allah tsira da amincin Allah su Tabbata a gareshi cewa “ba aure matuqar ba wali”

an ruwaito wannan hadisin daga Umar xan Khaxxab da Ali xan Abi

Xalib da Abdullahi xan Mas’ud da Ibn Abbas, da Abu Huraira Allah

ya yarda da su. Shine abin da suka tafi akansa. kamar yadda kuma

shine abin da A’isha ta tafi akansa Allah ya yarda da ita, kuma shine

ra’ayin Sa’id xan Musayyib da Alhasan Albasri da Umar xan Abdul-

Aziz da Jabir xan Zaid, da Sufyan As-sauri da Ibn Abi Laila da Ibn

Shibrimata da Ibn Almubarak da Ashshafi’i da Ubaidullah xan Hasan

da Imam Ahmad da Ishaq da Abu Ubaida da sauran xaukacin

ma’abota ilimi. Kuma ibn Almundhir yana cewa: “ba a sami wani daga cikin sahabbai da ya savawa wannan ba”

Daga cikin dalilan da suka tabbatar da hakan akwai abin da

Aisha Allah ya yarda da ita ta ruwaito cewa, manzon Allah tsira da

amincn Allah su tabbata a gare shi cewa: “duk matar da ta yi aure ba tare da izinin waliyinta ba to aurenta vatacce ne, aurenta vataccene,

104

idan kuma ya sadu da ita tana da sadaki da abin da ya halalta na farjinta, idan akai faxa to shugaba shine waliyin wanda ba shi da waliyyi 1.

Da kuma abin da Ibn Majah ya ruwaito da Dar-quxni daga Abu

Hurairah Allah ya yarda da shi, daga manzon Allah tsira da amincin

Allah su tabbata a gareshi yace "mace ba ta aurar da mace, kuma mace ba ta aurar da kanta mazinaciya itace take aurar da kanta”2.

Da kuma abin da aka ruwaito daga Ikrima xan Khalid yace:

“wata rana hanya ta tava haxa waxansu matafiya sai wata mace bazawara ta damqa al’amarinta a hannun wani mutum wanda ba waliyyinta ba ya aurar da ita, sai labari ya iske Umar sai ya sa aka yiwa wanda ya aurar da ita bulala ya kuma soke aurenta”. Shafi’i da

Dar-quxni suka ruwaito. An kuma karvo daga Shafi’i yace: “babu wanda yake da tsanani a sahabban manzon Allah dangane da auren mace ba tare da waliyyi ba, kamar Ali Allah ya yarda da shi domin ya kan yi bulala idan an yi shi" Darquxni ya ruwaito.

Haka nan an sanya sharuxa guda bakwai ga waliyyi kafin auren

da ya xaura ya inganta waxanda sune: Hankali, yanci, balaga,

kasancewarsa namiji, musulunci da rashin haramar hajji ko umra, da

rashin tilastawa. Haka nan akwai waxansu sharuxa biyu da aka yi

savani akansu, waxanda sune: adalci da shiriya, haka kuma makaruhi

ne waliccin fasiqi matuqar an samu waliyyi adali, to amma idan ya

xaura auren ya yi, kamar yadda shiriya ba sharaxi ce ta walicci ba,

kasancewar wauta ba ta hana walicci, don haka idan aka samu wawa

mai faxa aji yana iya xaura aure ba tare da izinin waliyyinsa ba

kuma ba tare da izinin wacce ke qarqashin ba, to amma mustahabbine

ya nemi izinin ta da izinin waliyyinsa a matsayin mustahabbi kawai

ba sharaxi ba.

Wauta nau’i biyu ce:

1 Abu Dawud da Tirmidhi suka ruwaito

2

105

a. wauta amma akwai addini, da hankali, da basira, duk wanda aka

siffanta da haka to ana xaukarsa a matsayin wawa mai faxa

aji, domin babu warwarar juna tsakanin faxa aji da wauta, don

ba tilasne idan akwai ra’ayi ya zamo an samu hangen nesa ba.

b. wauta haxe da raunin ra’ayi da basira da tauyaya wajen gane

abubuwa. Dangane da wawa mai faxa aji, mun bayyana

ingancin waliccinsa, da ingancin auren da ya xaura duk da cewa

mustahabbi ne waliyinsa ya duba abin da aka aiwatar, kamar

yadda yake da ikon soke shi to amma idan an riga an xaura

auren to ya inganta. Shi kuwa mai raunin ra’ayi ba shi da ikon

waliccin aurar da ‘yarsa ko watanta, kamar yadda ba shi da ta

cewa wajen zavarwa wacce yake yiwa walicci miji, kamar

yadda aka yi savani dangane da wanda zai yi waliccin xaura

mata auren shin mahaifinta ne, ko wanda aka yiwa wasiyya.

Ya ku bayin Allah! Shi kansa mahaifi bai inganta ya kasance waliyyi

ba har sai waxancan sharuxa bakwai da suka gabata sun cika akansa,

idan ko ya kasance haka to waliccin nasa ya kasu gida biyu: walicci

mai dole , da na izini dangane da walicci na dole mahaifi yana da shi

ga nau’i uku na 'ya’yansa mata waxanda sune: mahaukaciyar

budurwa da bazawara yarinya wacce ba ta balaga ba, kamar yadda

yake da shi ga ‘ya’yansa nau’i uku ne na maza waxanda sune:

mahaukaci da karamin yaro da wawa.

Dangane da wakilcinsa akan waxanda muka gabatar daga

‘ya’yan mahaifi yana da ikon ya aurar da su ga wanda ya so, ba tare

da izininsa ko shawararsa ba, ko da kuwa ta hanyar yi musu dole ne,

sai dai idan da wanda yake da nakasa da za ta tilasta soke auren, idan

hakane to ba shi da ikon yi musu dole akan auren su. Kamar yadda

yana da ikon aurar da su ga wanda bai dace da su ba, da wanda yake

qasa da matsayinsu ta fuskar dukiya, da sadaki qasa da na irinsu, haka

nan ba su da magana a irin wannan auren ko su ko wasunsu to amma

a cikin wannan akwai qarin bayani.

Idan mahaukaciya ta kasance budurwa to yana da ikon yi mata

tilas, yarinya ce ita ko bazawarace baliga, ba tare da banbancin cewa

106

haukan nata na koda yaushe ne ko kuwa yakan yanke ta hanyar

kasancewa ta kan warke a waxansu lokuta, kamar yadda ba wajibi

bane a jira lokacin warkewar ta, haka nan kuma bazawara, baliga

kuma haukanta xorarre ne to ita ma yana da ikon yi mata dole, ko da

kuwa ta haifi ‘ya’ya kuma xanta ba shi da magana matuqar akwai

waliyyi, kuma matuqar tana da shiryayye kasancewar ana gabatar da

waliccin mahaifi akan nasa idan kuwa harta kasance takan warke a

waxansu lokuta, to ba shi da ikon yi mata dole, sai ya jira lokacin

warkewarta. Haka nan mahaukaciya idan ba ta haihu ba, kuma ba

wanda aka yiwa wasiyya da ita, to al’amarinta yana hannun alqali

haka nan idan mahaifin nata ya kasance shima mahaukaci ne.

2. Dangane da budurwa kuwa, mahaifinta na da ikon yi mata dole,

yarinya ce ko babba ko baliga, ba tare da banbancin cewa tana farkon

balagarta ne irin wacce ana qirga ta a matsayin 'yan mata ko wacce ta

xau tsawon lokaci tana zaune a gidan mahaifinta ba tayi aureba harta

kai ko da shekara sittin ne, ta zamo wacce ta xauke tsammanin aure.

Kasancewar mahaifi yana da ikon yiwa 'yarsa wacce ta xauke

tsammanin aure shine abin da ya fi shahara a mazahaba. Ku ji tsoron

Allah ya ku bayin Allah, ku nemi sanin hukunce hukuncen addinin ku

ko kuwa ku rabauta da abin da Allah ya siffanta a faxarsa: "gidajen Aljannar zama, suna shigarsu su da waxanda suke kyautata daga iyayensu da matansu da zuriyarsu kuma mala’iku suna shiga zuwa gun su ta kowacce kofa "(Ra’ad: 23).

Ina faxar wannan magana tawa ina roqon Allah ya gafarta

mana, ni da ku da kuma sauran musulmi maza da mata ku nemi

gafararsa zai gafarta muku don shi mai yawan gafara ne mai rahama.

107

Huduba ta Biyu:

Godiya ta tabbata ga Allah wanda yake hukunci da gaskiya, da Adalci

kuma shine mafificin masu hikima, kuma mafi tausayin masu tausayi,

ina kuma shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, shi kaxai

yake bashi da abokin tarayya. Wanda shine abin bauta na farko da na

qarashe, kuma ina sheda cewa shugabanmu Annabi Muhammad

manzonsa ne kuma ya aiko shi da addinin gaskiya, don ya xaukaka shi

akan kowanne addini. Wanda kuma shine fiyayyen halittarsa baki

xaya, Allah ya yi daxin tsira a gareshi da alayensa da sahabbansa

masu tsarki da ikhlasi da waxanda suka biyo su da kyautatawa zuwa

ranar sakamako.

Bayan haka, ya ku bayin Allah! Lalle walicci dole yana faxuwa

akan budurwa a lokuta guda biyu:

Na xaya: lokacin da mahaifinta ya hukunta shiryuwarta, wato ya sakar

mata akala saboda abin da ya gani ya kuma sani na kyawun tunaninta,

don haka sai ya hukunta cewa, ta shiryu sai dai waliccinsa zai ci gaba

da kasancewa akanta, koda bayan hukunta shiriyarta, to amma

waliccin nasa ya sauya daga waliccin yin dole izuwa na neman izini

da zavi, ta yanda zai zamo ra’ayinta shine abin la’akari a kowanne

al’amari nata, ta yadda waliyyanta wanda shine mahaifi zai zamo

baya da haqqin komai sai xaura mata aure, haka ma xaukar nauyinta

ba zai faxi akansa ba har sai ta yi aure mijinta ya sadu da ita.

3. Bazawara yarinya kuwa wacce ba ta balaga ba, hukuncinta hukunci

ne na budurwa yarinya dai-dai da dai-dai wato waliyyinta na da ikon

yi mata dole, saboda qarancin shekarunta wanda shine dalilin yin

dolen. Kuma babu banbancin zamowarta bazawara ne ta hanyar aure

ingantacce, ko waninsa matuqar dai an gusar da budurcinta ko ta

wacce hanya ne. Mahaifi nada haqqin waliccin dole akanta matuqar

dai bata balaga ba. Idan kuwa ta zama bazawara ta hanyar aure ya

mutu kafin ta balaga, sai kuma ta balaga kafin aure na biyu to ba za a

108

yi mata dole ba, to malam Suhnun yana ganin cewa za a yi mata tilas,

a kowanne irin hali. Dangane kuwa da yarinya qarama wacce ta zamo

bazawara ta hanyar wani abu da ya bijiro, kamar sanda ko ta hanyar

tsalle, ko duka ko zazzavi ko tunkuxowar jinin haila, hukuncinta irin

na qaramar yarinya ne, idan kuwa ta zama bazawara ta hanyar

haramci kamar zina ta haihu a sanadiyyar haka waliccin yin dole zai

cigaba da kasancewa akanta.

Kamar yadda za a gabatar da mahaifinta a wajen walicci akan xanta

na zina, ko wanda ta samu ta hanyar faxe, to amma idan budurwa

baliga ta zamo bazawara ta hanyar aure, ko dai ingantacce ne ko

vatacce ba tare da banbancin kasancewarsa vatacce ko wanda da aka

yi savani akansa, ko wanda aka haxu akansa, to amma za a xage masa

haddi saboda shubuha, ta walicci. Waliccin mahaifi zai sauya zuwa ga

waliccin izini, duk wacce aka aurar da ita nau’in auren da an haxu

akan vacinsa, to amma zai kawar mata da haddi saboda shubuha.

kuma mijin ya sadu da ita, ya gusar da budurcinta sai kuma ta rabu da

shi ta hanyar warwarewar aure, ko saki, ko mutuwa mahaifinta ba zai

yi mata dole ba, don kuwa za a xauki auren ne a matsayin aure

ingantacce, saboda za a sadar da yaro ga mahaifinsa a kuma kawar

masa da haddi. Kamar yadda iddarta za ta yi ne a gidan mijinta wanda

take zaune a cikinsa, kuma babu banbancin kasancewarta wawiya ko

natsatstsiya, to amma idan auren ya kasance wanda aka haxu akan

vacinsa, ba a kuma kawar masa da haddi ba, to mahaifi na iya yi mata

dole, kasancewar za a sadar da shi da zina ne, domin kuwa an mayar

da ita bazawara ne ta hanyar haram.

Ku yi salati da sallama ga fiyayyen halitta shugabanmu Annabi

Muhammad, kamar yadda Ubangijinmu ya yi mana umurni da yin

hakan, “Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, Ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56). Tsira da aminci su tabbata

a gareshi da alayensa da sahabbansa baki xaya ya ku bayin Allah!

“Haqiqa Allah yana yin Umurni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe

109

jama’a, yana yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90)

ina mai faxar wannan magana tawa ina neman gafarar Allah a gare ni

da ku da duk wanda ya yi imani ya musulunta, daga kowanne zunubi

sai ku nemi gafararsa lalle shi mai yawan gafara ne mai rahama.

110

14

Savani Tsakanin Ma’aurata Da Hukuncin Adalai

Godiya ta tabbata ga Allah, muna neman taimakonsa, muna neman

gafararsa, muna kuma neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu,

da miyagun aiyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar haqiqa shine

shiryayye, wanda kuma ya vatar ba za ka tava samar masa majivincin

lamari mai shiryar da shi ba, ina shedawa babu abin bautawa da

gaskiya sai Allah, kuma Annabi Muhammad bawansa ne kuma

manzonsa ne.

Bayan haka, ya ku bayin Allah! Ku ji tsoron Allah haqiqanin

jin tsoronsa, kuma ku sani cewa duk lokacin da aka sami savani

tsakanin ma’aurata, lamarin zamantakewa ya yi tsamari a tsakaninsu,

to ko dai cutarwar daga matar take, ko daga mijin ko kuma dukkansu

biyun, in kuwa har al’amarin ya rikice aka rasa gane wanda ya shiga

haqqin wani to ga yadda za a lalubo bakin zaren, idan an gano cewa

cutarwar daga mace take ta zamo fanxararriya kenan, abin da ake nufi

da fanxararriya itace wacce take savawa mijinta, ta dena yi masa

biyayya, irin biyayyar da ta zamo wajibi akanta ta yiwa mijin, ko

kuma ta yi watsi da haqqin Allah Maxaukakin Sarki ya xorawa mace

ta bijirewa mijinta ko dai ta hanyar hana shi saduwa da ita, ko ta hana

shi jin daxi da ita koda kuwa ba ta hanyar saduwa bane, ko ta fita

zuwa wani wuri ba da izininsa ba, ta je inda ba ya so ko ta rufe masa

kofa ko ta hana shi shiga ko ta ha’ince shi a dukiyarsa ko ta aikata

alfasha, haka nan za ta kasance fanxararriya idan ta yi watsi da

haqqoqin Allah Maxaukakin Sarki ta hanyar dena tsarki ko wankan

janaba, ko ta sava wani abu da Allah Maxaukakin Sarki ya wajabta

mata. Allah Maxaukakin Sarki yace: “kuma waxanda kuke tsoron bijirewarsu to ku yi musu gargaxi kuma ku qaurace musu a cikin

111

wuraren kwanciya, kuma ku doke su. sannan kuma idan sun yi muku xa’a, to kada ku nemi wata hanya a kansu.” (Nisa’i:35)

In ana son magance matsalar fanxarewar mace to sai za abi

waxannan matakai kamar yadda ya zo a cikin nassin ayar na farko

shine wa’azi, wa’azi: shine ambaton abubuwan da za su tausasa

zukata ta hanyar kwaxaitarwa dangane da ladan biyayya ga miji, da

tsoratarwa game da azabar da take tattare da sava masa, da farko

mijine zai yi mata wa’azi da fatan ko za ta gyaru da wa’azinsa, idan

kuwa hakan ta ci tura sai liman ya yi mata, wa’azin ko wani da ke iya

wakiltarsa a irin waxannan al’amura a lokacin da ya kai masa qararta,

to idan kuwa har wa’azin mijin ko na liman bai yi amfani ba, sai ya

yi niyyar qaurace mata.

Abu na biyu: qauracewa: qauracewa itace dena saduwa da ita,

da qauracewa kwanciya da ita a shimfixa xaya, amma abin da ya fi

shine ya qaurace mata wata xaya, kamar yadda zai iya yin qari akan

hakan, to amma kada ya kai wata huxu. Idan kuma qauracewar ba ta

yi amfani ba sai ya doketa, duka wanda ba matsananci ba.Ya halalta

ga mijin ya yi duka ba mai tsanani ba matuqar qauracewar da wa’azi

ba su yi amfani ba. duka mai tsanani shine wanda zai sa mace ta sha

wahala wanda ka iya karya qashi ko ya raunata jiki. Miji ba shi da

haqqin yin dukan da ya wuce iyaka, koda kuwa yana sane da cewa ba

za ta dena abin da takeyi ba sai ya yi hakan, kamar yadda idan ya yi

mata duka mai tsanani to ya zamo xan ta’adda, ita kuma tana da

haqqin ta nemi saki ta kuma nemi a rama mata, saboda haka, dukan da

aka yi izini da shi shine duka mara tsanani, tare da kaucewa fuska,

kamar yadda abin da zai sa ayi dukan shine kasancewa dukan zai yi

amfani idan kuma ya san cewa ba zai yi amfani ba to ya kamata kada

ya daketa domin dukan ba zai sa ta dena abin da takeyi ba wannan

kuwa ya samo asali ne kasancewar duk wata hanya da za abi matuqar

ba za ta kai ga inda akeso ba shari’a ba za ta amince abi ta ba. To

amma fa wannan ya taqaita ne kawai ga duka, banda wa’azi da

qauracewa, waxanda miji zai aikata su koda kuwa ba ya zaton cewa

za su yi amfani.Wani abin lura shine kada ya tsallake xaya daga cikin

112

matakai zuwa wani da zaton cewa matakin da ya zo kafinsa ba zai yi

amfani ba.

Abu na huxu shine horo ta hanyar dukiya, matuqar miji yana da

ikon ladabtar da matarsa ko kuma ta hanyar yanke hukuncin alkali ne

to amma sai bai aikata hakan ba, to tana da haqqin kulawa ko kuwa ta

rinjaye shi ne, saboda da qabilancin danginta ne kasancewarsu mutane

ne irin waxanda ba za a iya zartar da hukunci akansu ba, idan haka ne

to ba ta da haqqin kulawa. Idan kuwa cutarwar ta hanyar miji ce, ya

kasance yana dukanta ko cutar da ita ko qaurace mata, ko tsine mata,

ko zagi ko cin zarafi, ita kuma tana son zama da shi haka ba ta son a

raba aurensu, ta kuma kai qara wajen shugaba ta tabbatar da cewa

yana cutar da ita, ko dai ta hanyar kawo hujja ko shi ya amsa da

kansa, ko al’amarin ya bazu, to shugaba zai bi waxannan matakai don

jan kunnen sa:

1. Shugaba zai yi masa wa’azi, ya ja kunnensa ya yi iyaka

qoqarinsa wajen hana shi gwargwadon ikonsa.

2. Idan wa’azi kuma da jan kunne ba su yi amfani ba, to sai ya yi

mata Umurni da ta qaurace masa a wurin kwana.

3. Idan qauracewar ba ta yi amfani ba sai ya yi masa barazana da

xauri ko duka. Malam Almuwaq yace: “haqiqa malamai sun ce ana iya xaure miji to amma ba zan iya tuna wani wuri da suka ce xaure mace ba”.

4. Idan barazanar ba ta yi amfani ba sai ya yi Umurni da dukansa

gwargwadon ijtihadinsa, to amma an shimfixa sharuxa guda

biyu kafin akai ga shugaba ya doke shi kamar haka; na farko sai

an tabbatar da cewa yana cutar da ita. Na biyu sai yana da

tabbas ko yana da cikakken zaton dukan zai yi amfani wajen jan

kunnensa idan kuwa har ba a tabbatar da cewar ya qetare iyaka

ba, kuma ba zaton cewa dukan zai yi amfani to ba abun da

shugaba zai yi masa inba wa azi da jankunne ba tare da duka ba,

hakan nan baya cikin nau’in cutarwa ya hanata fita yawon miqe

kafa ko na shaqatawa, ko kuma ya doketa duka mara tsanani a

sanadiyyar qin yin Sallah da abubuwan da suke kama da haka

ko a dalilin zai yi mata kishiya.

113

Kamar yadda ba shi da ‘yancin rufe kofa ya hanata shiga gida, haka

nan ba zai hanata kasuwanci na saye da sayarwa ba, matuqar ba fita

take yi ba, ko kevewa da wanda ba muharraminta ba, ko yana ji mata

tsoron lalacewa dalilin yin hakan. bai wajaba miji ya saki matarsa

fajira ba, kamar yadda ba za a tilasta masa ya saketa ba, kamar ta

kasance ba ta salla ko azumi ko ba ta wankan janaba, amma yana da

ikon ladabtar da ita to ya cigaba da zama da ita, in kuma ya ga dama

yana iya rabuwa da ita kamar yadda ya halalta ya karvi abin fansa

daga gare ta a matsayin khul’i. Wannan kenan, duk wanda ya san matarsa tana zina bai halalta

ya cutar da ita da niyyar ta fanshi kanta ba, idan kuma itace da kanta

tayi h akan ba tare da cutar da ita ba, to ya halalta ya karva.

A lokacin da dukkan waxannan matakai guda hudu ba su yi

amfani wajen jan kunnensa ya dena zaluntarta da cutar da ita ba, ta

kuma nemi saki sai shugaba ya sakar masa ita, ko ita kanta ta fanshi

kanta bisa sharuxan da muka ambata a baya dangane da cutarwa. Ina

faxar wannan magana tawa ina mai roqon gafarar Allah gare ni da

ku, da sauran musulmai maza da mata, ku nemi gafararsa lalle shi

Mai yawan gafarane Mai rahama.

114

Huxuba Ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah, godiya mai yawa, mai albarka a cikinta,

kamar yadda Ubangjinmu yake so kuma ya yarda, ina shedawa babu

abin bautawa da gaskiya sai shi, shi kaxai yake ba shi da abokin

taraiya, ina kuma shedawa Annabi Muhammad bawansa ne kuma

mazonsa ne wanda ya fifita, kuma badaxinsa tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi da waxanda suka biyo su da kyautatawa har zuwa

ranar sakamako

Ya ku bayin Allah! Idan lefi ya kasance na ma’auratane su

biyu kuma kowanne daga cikinsu yana da’awar cewa na xaya ne, a

misali kowanne yana iqrarin xayan yana dukansa sai a aika masu

hunkuci guda biyu.

Ko yaushe ya kamata a aika masu hukunci biyu?

Ana aikawa da su ne a duk lokacin da aka sami keta haqqoqi

daga ma’aurata biyu, aka tabbatar da cewa kowanne daga cikinsu

yana shiga cikin haqqin xan uwansa to sai shugaba ya yi musu wa’azi

ya kuma ja musu kunne, sannan ya doke su gwargwadon ijtihadinsa.

haka idan mace ta yi kukan miji yana cutarta sai ta kai qararsa

wajen shugaba, sannan qorafin yayi yawa ba tare da wata hujjaba ba,

ko kuma kowannensu yana qorafi ba hujja a irin wannan yanayi

shugaba zai Umurci miji ya zaunar da ita tsakanin mutane biyu adalai

nagari, waxanda da za a iya karvar shedarsu, ya xora musu nauyin sa

ido akan al’amuaransu, da gano cutarwar da ake yi mata, kuma

matuqar ta natsu da su to bai halalta a mayar da al'amarin hannun

wasunsu ba.

Haka nan shugaba zai nemo labarinta daga maqotanta da kuma

waxancan mutane biyu da ta natsu da su, ya kuma halalta a karvi

shedarsu, to idan suka bada sheda akan cutarwar da yake yi mata, ya

tabbata cewa mijine yake shiga haqqinta, to sai ya bi matakan ladabtar

da shi da suka gabata, in har tana son ta cigaba da zama da shi ta

kuma aminta cewa ba zai cutar da ita ba. In kuma tana son rabuwa da

shi to sai ya sakar masa ita ta fuskar da muka bayyana.

115

Idan kuwa suka bayar da shedar cewa bijirewar daga ita ne to

sai yabi matakai da suka gabata wajen jan kunnenta. To idan kuwa

daga sune gaba dayansu sai yayi musu wa'azi yayi musu gargadi ya

dokesu gwagwadon ijtihadinsa

idan kuma qorafi ya yi yawa aka cigaba da rikici da samun

matsaloli, kuma aka kasa gane mai cutarwa don a gusar da cutarwar to

sai shugaba ya aika masu hukunci biyu daga vangaren kowanne daga

cikinsu. Ibn Asim a cikin Tuhfa yace "idan aka tabbatar da cutarwa ta yi tsanani, ga mace daga mijinta ta yi ta faman qara, a aika da masu hukunci biyu, da za su yi hukunci kamar yadda alqur'ani ya hukunta"

Allah Maxaukakin sarki yana cewa: “Ya ku waxanda suka yi imani, ku bi Allah da taqawa kuma rai ya dubi abin da ya gabatar domin gobe, kuma ku bi Allah da taqawa”.

Ina roqon Allah ya yi min albarka, ni da ku, a cikin fahimtar

Alqur’ani mai girma. Ina faxin wannan maganar tawa ina neman

gafarar Allah a gareni da gare ku, da kuma sauran musulmai maza da

mata ku nemi gafararsa zai gafarta muku domin lalle shi mai gafara

ne. “Haqiqa Allah yana yin Umurni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin da aka qi da rarrabe jama’a, yana yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl: 90)

116

15

Shar'anta Aika Masu Hukunci Biyu

Huxuba ta Xaya

Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa muna kuma neman

gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da

munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai vatar da

shi, wanda kuma ya shiryar babu mai vatar da shi. Kuma ina shedawa

babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ina shedawa

Shugabanmu Annabi Muhammadu bawan Allah ne kuma manzonsa

ne. Allah ya yi daxin tsira bisa alayensa da sahabbansa da waxanda

suka biyo su da kyautatawa har zuwa ranar sakamako.

Ya ku mutane! Ku ji tsoron Allah ku kuma yi masa godiya da

ya halitta dominku mata daga kawunanku don ku sami nutsuwa da su,

ya kuma sanya qauna da tausayi a tsakaninku, lalle a cikin wancan

akwai ayoyi ga mutane masu tunana.Yaku bayin Allah! Asalin masu

hukunci biyu faxin Allah Maxaukakin Sarki: “Kuma idan kun ji tsoron savawar tsakaninsu, to ku aika da wani mai sulhu daga mutanensa da wani mai sulhu daga mutanenta. Idan sun yi nufin gyarawa, Allah zai daidaita tsakaninsu (ma’auratan). Lalle ne Allah ya kasance Masani Mai jarabawa” (Nisa’i: 85). Kuma kamar yadda aka

gani a abin da ayar ta bayyana cewa, masu hukuncine guda biyu kuma

daga cikin ‘yan gidansu, haka nan kuma aikin da aka xora musu shine

su yi sulhu, Umurnin da aka yi kuma na aikawa da su ana maganane a

cikinsa da shugabanni, da sarakuna, da jagorori, haka nan kuma ana

aike sune in an ji tsoron savani a tsakanin ma'aurata biyu. Haka nan

Usman xan Affan ya aika Abdullahi xan Abbas Allah ya yarda da su

shi da Mu'awiyya xan Abi Sufyan, Allah ya yarda da su labarin abin

da ya faru da Aqilu xan Abu Xalib da matarsa Fatima ‘yar Utbatu xan

117

Rabi'atu, xan Abbas yace: “An aikeni ni da Mu'awuya a matsayin masu hukunci aka ce mana in kuna ganin za ku hada ku haxa in kuma rabawa za ku yi ku raba," Ma'amar yace: “labari ya isheni cewa wanda ya aika su shine Usman xan Affan Allah ya yarda da shi” Da kuma

abin da Abdur-Razzaq ya fitar daga Ubaidatu Assalmani yace: “Na halarci majalisin Ali xan Abi Xalib a lokacin da wata mata ta zo masa da mijinta, kowanne daga cikinsu tare da wata tawaga ta mutane, sai kowanne suka fitar da mai hukunci, sai yace da masu hukunci biyu: "ko kun san abin da yake kanku ? Idan kun ga za ku haxa ku haxa in kuma kun ga za ku raba ku raba." Haka nan ba’a sharxanta amincewar

ma'auratan biyu ba, Qurxubi yana cewa: wannan isnadi ne ingantacce

kuma tabbatacce da aka ruwaito daga Ali ta hanyoyi tabbatattu daga

Ibn Sirin daga Ubaidatu. Haka Abu Amru ya faxa: Wannan maganar

ta sayyidina Ali Malik ya fitar da ita a Al-muwatta a bayanin saki

babin abin da ya zo dangane da masu hukunci biyu. Da kuma abin da

ya fitar da shi daga Abu Salama yace: In masu hukunci biyun sun ga

dama su raba in kuma sunga dama su hada."Haka nan Sha'abi ya fitar

da hadisi irinsa.

Sharuxan masu hukunci biyu:

An sharxanta wa ingancin masu hukunci biyu kowannensu ya kasance

musulmi, 'yantacce, baligi, namiji, adali, shiryayye, da fahimta

dangane da abin da ya shafi hakan, su kuma kasance daga 'yan

uwansu. Don haka kafiri ko bawa ko qaramin yaro bai inganta su yi

hukunci ba. Haka nan kasancewa namiji sharaxi ne don haka

hukuncin mace bai inganta ba, haka kuma jagorancinsu, kasancewar

shi mai hukunci shugabane da ya zama wajibi a yi koyi da shi. Haka

nan adalci shima sharaxi ne don haka wanda ba adali ba kamar yaro

ko mahaukaci ko fasiqi, duk waxannan hukuncinsu baya inganta.

Haka nan natsuwa, don haka hukuncin wawa baya inganta

domin shi wawa kasancewar shima yana buqatar kasancewa

qarqashin wanda zai yi masa walicci don haka ba zai zamo adali ba,

ko da kuwa ya fi duk waxanda suke raye a zamaninsa nagarta,

kasancewar xaya daga cikin sharaxin adalci shine ya kasance babu

118

wanda yake walicci akansa. Haka nan kuma idan wawa ya kasance ba

ya zaman kowa wato ba shida waliyyi ya kuma kasance ba adali bane

to ba za a karvi hukuncinsa ba. To amma wanda ya siffantu da abin da

ake xauka a matsayin adalci to adaline.

Dangane kuwa da fahimta akan haka: Abin da ake nema daga

wanda zai yi hukunci ya kasance ya fahimci hukunce hukuncen da

suke da dangantaka da cutarwa tsakanin ma'aurata. Don haka ba ya

inganta a sa jahili da bai san abin da aka xora masa nauyinsa ba ya yi

hukunci, domin sharaxi ne ga duk wanda za a xorawa nauyin wani

al'amari ya san hukunce-hukuncensa na shari'a, don haka wanda ba

masani ba hukuncinsa baya inganta, sai dai idan zai shawarci malamai

a abin da zai yi hukunci da shi. Idan ya yi hukunci da abin da suka ba

shi shawara to za a zartar da hukuncin nasa.

Kamar yadda kuma an sharxanta cewa, tilas ne daga 'yan uwan

miji a samu mai hukunci da mai hukunci daga 'yan uwan mata,

wannan sharaxi wajibi ne domin masu hukunci biyu ba za su kasance

ba sai daga ‘yan uwan miji da na matar saboda abin da nassi ya zo da

shi, kuma kasancewar sune suka fi sanin abin da ke faruwa tsakanin

ma’auratan, suka fi sanin xabi’unsu, don haka za su fi kowa iya sanin

hanyoyin da za su gyara tsakaninsu, don haka sun fi cancanta fiye da

wani bare. Sannan kasancewar suna daga cikin ‘yan uwansu, hakan

zai fi ba su dama su yi qoqari matuqa wajen yin gaskiya da kaiwa

qololuwa wajen tausasawa.

Idan kuwa a ‘yan uwansu ba a sami wanda zai dace da hakan

ba, sai a aika waxanda ba su ba daga waxanda ba na kusa da suba,

kuma mustahabbi ne su kasance waxanda suka sansu, in ba haka ba to

a samo a maqotansu don maqoci ya fi kowa sanin halin da maqocinsa

yake ciki.

Ina faxin wannan magana tawa ina mai neman gafarar Allah

gare ni da ku da sauran musulmi maza da mata daga kowanne zunubi,

ku nemi gafararsa zai gafarta muku lalle ne shi mai yawan gafara ne

mai yawan rahama.

119

Huxuba ta biyu

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina kuma shedawa babu abin

bautawa da gasikya sai Allah, kuma annabi Muhammad bawansa ne

kuma manzonsa ne, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi Allah

ya yi albarka a gare shi da alayensa da sahabbansa.

Ya ku mutane! Ya zama wajibi ga masu hukunci biyu su yi

sulhu tsakanin ma’aurata biyu ta kowacce fuska mai yiwuwa, Allah

Maxaukakin Sarki yace: “idan sun yi nufin gyarawa Allah zai daiadaita tsakaninsu” (Nisa’i: 35). Ma’ana idan masu hukunci biyun

suka yi nufin gyarawa to Allah zai haxa kan ma’auratan biyu.

Wannan ita ce maganar Abdullahi xan Abbas da Mujahid da waxansu

su ka tafi akansa. Abin da da ake nufi da gyara a nan shine aikata abin

da ya fi zamowa gyara tsakanin ma’aurata biyu, ba wai lalle ana nufin

sulhu wanda yake savanin rabuwa ba, don sau da yawa yana

kasancewa abin da ya fi zamowa gyara shine a rabu, kamar yadda

yake iya kasancewa kuma cigaba da zama aure.

Wajibi na farko da ke kan masu hukunci shine, su haxa kansu

bisa zaman lafiya, da kyautata mu’amala matuqar sun sami damar yin

hakan. Idan kuwa suka gano wanda yake yin zalunci sai su karvi

haqqi daga gareshi su damqawa abokin zamansa, su tilasta shi akan

janye cutarwar, za su yi hakan ne da farko ta hanyar wa’azi da jan

kunne da hana shi, idan sun dawo sun koma yadda suke to sai su

qyalesu, idan kuwa sun ga kansu ya rabu, an kasa shirya tsakaninsu,

kuma al’amarin yaqi ci yaqi cinyewa bayan sun yi iyakar bakin

qoqarinsu wajen hada kansu iyakar iyawarsu, bayan sun tunatar da su

Allah da zaman tare, amma abinda ya fi zama dole shine su nemo

wanene ya fanxare a cikinsu, idan har suka gano wanda ya fanxare a

cikinsu don matuqar sun gano wanda ya fanxare al’amarin zai zo

musu da sauqi. Daga nan kuma in sun ga cewar rabuwar itace tafi to

shike nan.

Hanyar da za su bi wajen gano haka kuwa itace, kowanne ya

keve da xan uwansa, kevewa wacce ba za ta savawa shari’a ba, ya yi

120

masa magana da cewa, kai kuwa menene yake vata maka rai dangane

da abokin zamanka? In har kana da buqata ko ki na da buqata zamu

nuna masa laifinsa. Bayan sun saurari kowanne, sun tattara bayanai,

sai a duba idan ya tabbata cewa miji shine yake da laifi yake cutar da

ita ba ya son cigaba da zama da ita sai su sakar masa ita, ba tare da

fansa ba, in har taqi amincewa da cigaba da zama dashi, in kuwa ta

yarda da za ta ci gaba da zama da shi to ba za hukunta saki ba, kuma

igiyar auren tana nan a hannunsa, in kuwa ya so ya ci gaba da zama da

ita taqi amincewa to sai su yi hukunci da saki ba tare da biyansa

komai ba, kamar yadda muka ambata, kasancewar cutarwar daga

gareshi take.

Idan kuwa ya tabbata cewar laifin na matar ne kuma itace take

kawo savani, shi kuma yace yana son ta fanshi kanta, da abin da suka

ga ya dace da bangarorin biyu, ko kuwa za ta kai ga ta yi fansar kanta

da abin da ya qaru akan sadakinta ne. Idan kuwa ba ya son ta fanshi

kanta ya ga kuma cewa zai ci gaba da zama da ita a matsayin matarsa,

to sai su damqa masa amanar ta, su yi masa wasiyya da ya riqe ta da

alheri ya kuma yi hakuri da cutarwarta gareshi. A nan masu hukunchi

ba su da wata magana da ta wuce yin wasiyyar. Don haka da za su

raba tsakaninsu a dai-dai lokacin aka gano cewar cutarwar daga gareta

ne, shi kuma miji bai amince da ta fanshi kanta ba, ba za ayi la’akari

da rabawar masu hukunci ba, za ta kuma cigaba da kasancewa matar

aure. Kamar yadda hakan daliline mai qarfi cewa, su ko dai ba masu

ilimi bane ko kuma ba adalai ne ba. Wasu kuma suka ce za a zartar

da shi a kuma tilasta wa miji ya karvi fansa ta fuskar sauya

mummunan abu, domin kasancewarta tana savon Allah ne.

Idan kuwa suka kasa haqiqance komai, a ka cigaba da samun

matsala fa? An yi bayani mai tsawo akan hakan a manyan littatafai.

Idan kuwa suka gano cewa rashin kirkinsu ne su duka biyun ta yadda

kowannensu yana da laifi wajen cutar da xan uwansa, to saki ya zama

wajibi ba tare da fansa ba, wajen da yawa daga cikin malamai in har

bata yarda da cigaba da zama dashi ba kamar yadda waxansu manyan

malamai suka nuna da suka haxa da Addirdir da Assawi.

121

Ba shakka ginshiqin da aka xora al’amarin masu hukunci biyu

shine nassin Alqur’ani Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “Kuma idan kun ji tsoron savawar tsakaninsu, to ku aika da wani mai sulhu daga mutanensa da wani mai sulhu daga mutanenta. Idan sun yi nufin gyarawa, Allah zai daidaita tsakaninsu (ma’auratan). Lalle ne Allah ya kasance Masani Mai jarabawa” (Nisa’i: 85).

An samo cewa Qurtubi yana cewa: “wannan nassi ne daga Allah maxaukain Sarki cewa, su alqalai ne ba wakilai ba, ba kuma shedu ba. Bisa wannan in sun ga cewar za su raba tsakanin ma’aurata biyu to ya halalta su raba, za a kuma zartar da ita, haka nan ba banbanci ko hakan ya zo dai dai da hukuncin alkalin garin ko ya sava masa koda kuwa shine ya naxa su, kamar yadda ba banbanci ko ma’auratan biyu sun wakilta su su yi hakan ko ba su wakilta su ba, ko ma’auratan biyu sun amince a raba ko basu amince ba, koda kuwa sune suka naxa su, kasancewar su masu hukunci ne da nassin da ya gabata, da kuma abin da muka ruwaito a baya daga Ali da xan Abbas da Abu Salama da Sha’abi Allah ya yarda da su.

- Masu hukunci biyu na iya yin hukunci da sakin matar da aka

sadu da wacce ba a sadu da it aba.

- Idan masu hukunci biyu suka yi hukunci da raba aure za a zartar

da sakinsu ko da fansa ko ba fansa. Allah Maxaukakin Sarki

yace: “kuma idan kun ji tsoron savawar tsakaninsu, to ku aika da wani mai sulhu daga mutanensa da wani mai sulhu daga mutanenta. Idan sun yi nufin gyarawa, Allah zai daidaita tsakaninsu. Lalle ne Allah ya kasance Masani, Mai jarrabawa.” (Nisa’i: 35). Ina roqon Allah ya yi mana albarka ni daku cikin fahimtar

Alqur’ani mai girma, ya kuma amfane ni ya amfane ku da abin

dake cikinsa na ayoyi da anbato mai hikima. Tsira da amincin

Allah su tabbata ga shugabanmu Annabi Muhammad da

alayensa da sahabbansa. ina wannan magana tawa ina neman

gafarar Allah mai girma a gare ni da ku.

122

16

Hukuncin Cutar Da Mace Da yin Saki A sanadiyyar

Cutarwa

Huxuba ta Xaya

Godiya ta tabbata ga Allah kuma ina shedawa babu abin bautawa da

gaskiya sai Allah, kuma ina shedawa Shugabanm annabi Muhammadu

bawan Allah ne kuma manzonsa ne, ya isar da saqo, ya sauke nauyin

amana, ya yiwa al’umma nasiha ya yi jihadi wajen xaukaka addinin

Allah matuqar jihadi ya barmu akan hanya mai haske wacce hasken

darenta dai-dai yake da na ranarta, ba wanda zai kauce daga tafarkinta

sai hallakakke. Allah ya yi daxin tsira da albarka bisa alayensa da

sahabbansa da mabiyansa da wanda suka biyo su da kyautatawa har

zuwa ranar sakamako.

Bayan haka, kuji tsoron Allah ya ku bayin Allah! Ku kuma yi

masa biyayya, ku ji tsoron ranar da ba za a zalunci wata rai ba ko da

gwargwadon nauyin qwayar zarra ne. “kuma wani rai mai xaukar nauyi bai xaukar nauyin wani rai. Kuma idan ran da aka nauyayawa kaya yayi kira (ga wani mataimaki) zuwa ga kayansa, ba za a xauki komai ba daga gare shi, kuma ko da (wanda ake kiran) ya kasance makusancin zumunta ne” (Fatir: 18). “Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (Nisa’i:1).

Ya ku bayin Allah! Haqiqa, cutar da mace na daga cikin

abubuwan da Allah ya haramta ga mazaje, manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi yace: “wanda ya fi kowa cikar imani shine wanda ya fi kowa kyawun halaye, kuma zavavvu daga

123

cikin ku sune zavavvu ga matayensu” Tirmizhi ya ruwaito. Kuma mai

tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace: “mafi alkhairin maza acikin al’ummata sune waxanda ba sa yin ta’addanci ga matansu, suke tausaya musu, kuma basa zaluntar su duk wanda yake da mata yaqi tufatar da ita da abin da zai suturce al’aurarta, kuma yaqi ciyar da ita da abin da za ta qoshi da shi, shugaba yana da haqqin ya raba su” daga Badruz zaujaini.

Ya ku mutane! haqiqa cutar da mace ya kan kasance kodai ta

hanyar cutar da jiki ko dukiya, idan ya kasance da jiki ko dai ya

kasance mai sauqi ko bayyananniyar cutarwa mai tsanani, hakan

kuma tana iya kasancewa mai maituwace ko ya kasance sau xaya,

haka nan mace tana iya sharxanta cewar ba zai cutar da ita ba, tun a

lokacin xaurin aure, kuma tana iya qin sharxanta hakan, kamar yadda

tana iya haxa sharaxin nata da rantsuwa ko ba ta barshi tare da

rantsuwa ba.

To ko yaushe ne ake yin saki a cikin waxannanal’amura?

Amsar wannan tambaya ita ce za ta bayyana mana sharuxan da suka

zama wajibi kafin a saki mace saboda cutarwa. Mafi girman ginshiqi a

cikin su shine mace ta nemi ayi sakin, domin tana da zavin cigaba da

zama da shi in ta ga dama, duk da cewa yana cutar da ita, in kuwa ta

kasance qaramace to za a yi aiki ne da maganar waliyyinta wajen

rabuwa ko cigaba da zama.

Abu na farko: idan miji ya cutar da dukiyar matarsa ba tare da

ta kasance tana da wani sharaxi akan hakan ba, to sai shugaba ya hana

shi yin hakan, ya kuma nemi ya biya kuxin da ya xauka, idan ya sake

maimaitawa bayan hana shi sai shugaba ya yi masa horo ba tare da

sakar masa ita ba. Idan kuwa cutar da dukiyar tata taci gaba da

faruwa, to nan ba za ayi aiki da maganar mace wawiya wacce aka

wakilta wani akanta ba, a maimakon haka za ayi aikine da maganar

waliyyinta. Savanin cutarwa ta jiki wacce ba za ayi aiki da maganar

waliyyinta ba sai dai idan ita ce ta wakilta shi.

Abu na biyu: cutarwa da shari’a ta xauka a matsayin cutarwa a

shari’ance itace cutarwar da mace take da haqqi in an yi mata ta nemi

saki, itace wacce ake yi ta hanyar aikata duk wani abu da miji zai yi

124

wanda bai halalta ya aikata shi a shari’ance ba, kamar ya qaurace mata

ba tare da wani dalili na shari’aba, ko da kuwa ta hanyar qin yi mata

magana ne, ko juya mata fuska a wurin kwanciya, ko zaginta, ko tsine

mata, ko zagin iyayenta, a misali yace da ita “yar karnuka” ko ‘yar tsinannu” ko ‘yar kafiri” a irin wannan yanayi ana iya sakar masa ita

gwargwadon ijtihadin alkali, kamar yadda za a ladabtar da shi a kuma

sakar masa ita, idan ya sadu da ita ta dubura. Kuma kafin a yi saki sai

an tabbatar da gaskiyar cutarwar.

Abu na uku: Hanyar tabbatar da cutarwa da aka yiwa xaya daga

cikin ma’aurata takan tabbata ne ta daya daga cikin abubuwa guda

biyu, ko dai ta hanyar samun hujja ko ta hanyar samun labari mai

yawa, wanda kuma ya fi kowanne daga cikin waxannan hanyoyi shine

ya tabbatar da bakinsa da cutarwa.

i- Hujja: ya zama wajibi kafin a karvi hujja sai ta cika

waxannan sharuxxan:

Shedar adalai guda biyu ko su wuce haka, haka nan tilas

ne su kasance maza biyu, shedar namiji xaya da mata

biyu ba zata wadatar ba, kamar yadda shedar mutum

xaya da rantsuwa ita ma ba za ta wadatar wajen adalci

ba.

Tilas ne su ganewa idanuwansu cutarwar, saboda

maqotakarsu da ma’aurata ko kusancinsu ko abin da ya

yi kama da haka.

Tilas ne shedun su yi sheda akan ya doketa ko ya cutar da

ita ba tare da wani lefin da zai tilasta hakan ba.

Tilas ne shedun su tabbatar da cewa ba su san cewa

wanda yake cutar da itan ya dena ya tuba ba, in kuwa ba

haka ba alkali ba zai yi aiki da shedarsu ba. Haka nan

idan mijin ya yi da’awar cewar ta amince ya sadu da ita

ta bayan ta nemi araba su, ita kuma ta gaskata shi to

haqqin ta ya faxi ba tare da banbancin kasancewarta

jahila ko mai ilimi ba, ko da kuwa ta yi da’awar jahilci ba

za a yi mata uzuri ba. Haka nan kevancewa tsakaninsu da

125

amincewarta bayan ta nemi saki yana da hukunci iri xaya

dana saduwa, kasancewar idan aka sami savani dangane

da saduwa ko rashin ta za a yi aiki ne da maganar wanda

yace an sadu.

ii- samun labari ta hanyoyi da yawa daga bakin maqota mata da

masu

hidima da sauransu cewa, lalle wane yana dukan matarsa

wance ko yana zaginta ba tare da haqqi ba ko yana barinta

da yunwa, ko juya mata baya a makwanci ko ba yayi mata

magana, ko ma ko wane irin abu daza a iya lissafawa a

matsayin cutar da ita. Hakanan shedar mutum biyu adalai

tana iya wadatarwa daga yaxuwar labari tsakanin mutane da

yawa da maqota da cutar da ake yi. To amma an fi son a

sami shedu masu yawa. wannan shine abin da ya fi shahara a

mazhaba kuma shine abin da ake aiki da shi kamar yadda ba

ya halalta ayi aiki da labarin mata wajen shedar cutarwa su

kaxai kasancewar saki yana daga cikin dangogin haddi, don

haka bai halalta a yi aiki da shedar mata su kaxai ba, ya

zama tilas labarin ya watsu a same shi a tsakaninsu da

waxansu da suka haxa da ‘yan aiki da makota.

Abu na huxu:

Cutarwa mai sauqi da wacce ta yi tsanani, Imam Malik Allah ya

yi masa rahama yace: “bamu sami wani abu sananne ba dangane da kasancewar cutarwa mai sauki ko mai tsanani ba” Wato kamar dai ya bar shi ga al’adar ma’aurata masu rikici da

juna duq abin da shugaba zai yi ijtihadinsa gwargwadon

al’adunsu, kuma a wannan ba a aiki al’adun garin alqali.

Abu na Biyar: shin tilasne cutarwa ta maimaitu?

Malamai sun banbance tsakanain cutarwa mai sauqi da cutarwa

mummuna ta sarari, sai suka haxu akan cewa mace na da ikon

neman saki idan miji ya cutar da ita mummunar cutarwa ko da

126

kuwa sau xaya ne, in har ta tabbatar da hakan da xaya daga

cikin hanyoyin tabbatarwa.

Idan kuwa cutarwar ta kasance mai sauqi ce, ba mummuna ba an

sharxanta cewa sai ta maimaitu. Haka nan sai an yawaita samun

qorafi wajen alkali tare da tabbatar da hakan a gabansa don ya yi masa

wa’azi ya ja masa kunnensa ya yi masa gargadi, to idan ya qi ji, ta

nemi saki sai a amsa mata.

Abu na shida: Yadda ake tabbatar da cutarwa a gaban shugaba:

duk macen da take qarqasih mijinta za ta kasance ne ko dai ta

sharxanta cewa ba zai cutar da ita ba, tun lokacin xaurin aure, misali

ta ce in har ya cutar da ita to al’amarin ta zai kasance a hannunta. ko

kuma ta kasance ba ta sharxanta hakan ba. To koma dai menene daga

cikin waxannan halaye guda biyu mace za ta nemi saki ne ta hanyar

xaukaka al’amrinta zuwa wajen shugaba. Ta kuma tabbatar masa da

cewar ana cutar da ita ta xaya daga cikin hanyoyin cutarwa da muka

ambata, kuma bata da ikon sakin kanta kafin ta kai al’amarinta zuwa

ga shugaba da ta tabbatar masa. Haka nan kuma sai ya nemi jin ta

bakin miji har dai ya tabbatar cewa ba shi da ragowar wani uzuri da za

a iya masa. Ana yin saki ne a lokacin da miji ya cutar da matarsa saki

xaya marar kome ba tare da banabancin cewar ba ita bace ta saki

kanta ko shugaba ne ya sake ta ba. Kamar yadda ba ta da iko sai na

saki xaya, ko da kuwa an yi saki ya wuce sau xaya. Malamai suka ce

mace tana da ‘yanci na tilasta mijinta ya sake ta saki xaya mara kome

a dalilin cutarwa da mijinta ya keyi mata.

Ya ku ‘yan uwa! Ku yi salati da sallama ga shugabanmu,

msoyinmu kuma mai ceton mu, annabi Muhammad kamar yadda

Allah ya yi muku Umurni da yi masa salati in da yace: “Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, ya ku waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin amintarwa a gare shi” (Ahzab: 56). Ya Allah ka yi daxin tsira da aminci a gareshi da

alayensa da sahabbansa aminci mai yawa. Ina fadin wannan magana

ina neman gafarar Allah a gare ni da ku, da sauran musulmi maza da

mata daga kowanne zunubi, ku nemi gafararsa zai gafarta muku don

shi Mai yawan gafara ne Mai yawan rahama.

127

Huxuba Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah wanda shine masanin abin da ke cikin

zukata da abubuwanda aka voye a cikin rai, ina gode masa, tsarki ya

tabbata gareshi, ina kuma gode masa a bisa abin da ya yi mana na

ni’imomi da falala mai tarin yawa, ina kuma shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah kuma ina shedawa annabi Muhammad

bawansane kuma manzonsa ne, wanda shine mai tsarki wanda aka

tsarkake, mai babban asali da tsarki tsira da amincin Allah da albarka

su tabbata a gare shi da alayensa da sahabbansa ma’abota falala da

abubuwan al’ajabi da mabiyansu da kyautatawa har zuwa ranar

sakamako.

Bayan haka, ya ku bayin Allah! Ku sani cewa tausayi ba yana

nufin tausayi ba tare da aiki da hankali ba, ko kuma jin qai ne da zai

savawa adalci da tsari ba, ko kaxan ba haka ba ne, tausayi wata

dabi’ace kawai dake kare haqqoqin baki xayansu. Don haka a duk

lokacin da aka samu savani tsakanain ma’aurata biyu ko xaya daga

cikinsu ya cutar da xaya, to ya zama tilas a xaukaka al’amarin zuwa

ga shugaba, saboda abin da Allah ya wajabta musu, Allah

Maxaukakin Sarki yana cewa: “Kuma in sun rabu Allah zai wadatar da kowanne daga yalwarsa, Kuma Allah ya kasance Mayalwaci Mai hikima [Nisa’i: 30]

Ina roqon Allah ya yi mana albarka, ni da ku baki xaya wajen

fahimtar Alqur’ani mai girma ya kuma amfane mu ni da ku da abin da

yake cikinsa na ayoyi da Ambato mai hikima, ya kuma karva mana ni

da ku domin shi mai ji ne kuma masani. Ku miqe zuwa sallah Allah

ya yi muku rahama.

128

17

Rabon Kwana Da Adalci Tsakanini Ma’aurata

Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa muna kuma neman

gafararsa, muna neman tsarin Allah daga sharrin kawunanmu, da

munanan ayyukanmu, duk wanda Allah ya shiryar babu mai vatar

dashi, wanda kuma ya vatar babu mai shiryar da shi. Kuma ina

shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma ina shedawa

Shugabanmu Annabi Muhammadu bawan Allah ne kuma manzonsa

ne. Bayaban haka kuji tsoron Allah yaku bayin Allah, haqiqanin jin

tsoron Allah kukiyaye dokokin sa a sarari da boye Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa: “Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (Nisa’i:1)

Yana kuma cewa: “ku auri abin da ya yi muku daxi daga mata; biyu-biyu, da uku-uku da huxu-huxu, sannan idan kunji tsoron ba za ku yi adalci ba, to (ku auri) guda ko abin da hannayenku na dama suka mallaka….” (Nisa’i: 3) yana kuma cewa: “Kuma ba za ku iya yin adalci ba a tsakanin mata ko da kun yi kwaxayin yi. Saboda haka kada ku karkata, dukan karkata har ku barta kamar wadda aka rataye. Kuma idan kun yi sulhu, kuma kuka yi taqawa, to lalle ne Allah ya kasance Mai gafara, Mai jinqai.” (Nisa’i:129).

Haka kuma manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a

gareshi yace: “duk wanda yake da mata biyu a qarqashinsa sai ya karkata zuwa guda xaya daga cikinsu zai zo ranar tashin alqiyama, yana jan xaya daga cikin varin jikinsa a qasa ko a karkace” 1 ya ku

mutane! Haqiqa dukkan wanda ya auri mace biyu ya zamo tilas ya yi

1 Musnad Ahmad da sunan Ibn Majah

129

adalci tsakanin su, wannan abu ne da ya tabbata da nassin Alqur’ani

da sunna da haxuwar malamai. Allah Maxaukakin Sarki yana cewa:

sannan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to (ku auri) guda ko abin da hannayenku na dama suka mallaka….” (Nisa’i: 3) yana kuma

cewa: “kuma ku yi zamantakewa da su da alheri…” (Nisa’i: 19)

Kamar yadda kuma manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace:

Duk wanda ya kasance a qarqashinsa akwai mace fiye da

xaya sai ya karkata ga xaya daga cikinsu zai zo ranar

tashin Alqiyama yana jan varin jikiinsa a kasa ko kuma a

karkace1

An kuma karvo daga Anas daga annabi tsira da amincin

Allah su tabbata a gareshi ya kasance yana da mata tara

ya kasance idan ya raba kwana tsakanainsu, baya

dawowa wajen ta farko har sai bayan kwana tara. Imam

Muslim ya ruwaito shi. Haka nan al’ummata ta haxu

gaba xayanta akan wajabcin adalci, don haka duk wanda

bai yi adalci tsakanin matansa ba ya savawa Allah

Maxaukakin Sarki, ya savawa manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi don haka limancinsa

ba ya inganta, haka ma shugabancinsa ko karvar

shedarsa. kuma duk wanda ya yi jayayya da wajabcinsa

za a nemi ya tuba tsawon kwanaki uku idan bai tuba ba,

to za a kashe shi don zama kafiri a lokacin da ake neman

tubansa. (Duba: kifayatu attalib arrabani juz’i na uku shafi na 135).

Ya ku bayin Allah! lalle vangaren da ya zama wajibi na raba dai-dai

shine rabon kwana banda sauran abubuwan da suka haxa da saduwa

da soyayya “kuma ba za ku iya yin adalci ba a tsakanin mata ko da

1Malaman hadisai biyar suka ruwaito shi.

130

kun yi kwaxayin yi. Saboda haka kada ku karkata, dukkan karkata har ku barta kamar wadda aka rataye. Kuma idan kun yi sulhu, kuma kuka yi taqawa, to lalle ne Allah ya kasance Mai gafara, Mai jinqai.”

(Nisa’i:129) malamai sun ce duk wanda ba zai shiga qarqashin iko ba,

to ba zai shiga qarqashin wajabci ba, kamar yadda adalci wajen

soyayya da qauna da saduwa wannan shine abin da manzon Allah

tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yake roqon Allah kada ya

kama shi da laifi akansa inda yake cewa: “ya ubangiji wannan rabo na ne cikin abin da na mallaka, kada ka kama ni da laifin abin da kai kaxai ka mallakeshi ni ban mallake shi ba”1

adalci da aka yi Umurni

da shi wanda bawa zai yi wanda yake da iko akansa shine wanda ya

shafi rabon kwana, in har kuwa ba zai iya yin adalci a cikinsa ba ya

haramta gare shi ya auri mace fiye da xaya Allah Maxaukakin Sarki

yana cewa:

idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to (ku auri) guda

ko abin da hannayenku na dama suka mallaka.. (Nisa’i:

3)

Don haka da ake kore musu adalci wani wuri aka kuma tabbatar da shi

a wani wuri, hakan ya nuna akwai adalci kala biyu, adalcin da aka

kore wanda ya shafi abubuwa waxanda mulkine na Allah Maxaukakin

Sarki. Shi kuwa adalci da aka yi Umurni da shi shine duk abin da xan

adam yake da iko akansa, kamar yadda karkata wacce ta halalta ta kan

kasance tsakanin mata wacce aka hana ita ce wacce miji zai karkata

gaba xaya.

Abin da ya zama wajibi shine daidaito tsakanin mata a wajen

kwana ya bar al’amarin saduwa ga xabi’a da bukatarsa, to amma duk

da haka bai kamata ya yi zalunci a cikinsa ta yadda zai taqaita shi ga

xaya daga cikinsu don ya yi tanadin wata saboda ya fi sha’awar wata

ba, ba shakka yin hakan cutarwa ne ga wacce take da wannan daren,

kuma yin hakan abune da aka yi hani akansa. kamar yadda mijin da

1 Al mustadrak ala sahih al hakim

131

ya zama wajibi akansa ya yi adalci wajen rabon kwana shine miji

wanda yake baligi, mai hankali, mazaunin gida ba matafiyi ba, kuma

babu banbanci tsakanin kasancewar sa ‘yantacce ko bawa, mai lafiya

ko mara lafiya, rashin lafiya da zai iya kewaye gidajen matansa. Matar

da za a yi mata rabon kwana kuma tana da sharuxa guda biyu:

Na farko: ya kasance ya sadu da ita, idan bai sadu da ita ba to ba ta da

haqqin kwana.

Na biyu: ta zama wacce za a iya saduwa da ita in har ta kasance

qaramace ba a iya saduwa da ita, ko da kuwa an sadu da ita, to amma

idan ya sadu da ita matar za a iya saduwa ita to ya zama tilas a raba

kwana da ita. haka ma kuma idan ba za a iya saduwa da ita ba, saboda

wani dalili na shari’a ko na al’ada ko na xabi’a to ya zama wajibi

araba kwana da ita, waxannan sun haxa da mai haila, da mai jinin

biqi ko wacce take aikin hajji ko Umra a lokacin, haka nan wacce

mijin ta ya yi rantsuwa ba zai sadu da ita ba, da wacce ya yi mata

zihari da mai larura a farji ta qari da mahaukaciya da kuturwa da mai

tsukakken farji, da mai qari da mai warin farji dukkan waxannan za a

raba kwana da su. Kamar yadda ba banbanci tsakanin mace musulma

da ma’abociyar littafi da ‘yantacciya, da baiwa, da mai lafiya da mara

lafiya, koda kuwa rashin lafiya na iya hana saduwa, rabon kwana

tsakanin dukkan waxannan da kuma mace musulma ‘yan tacciya mai

lafiya mai tsarki baliga wacce aka sadu da ita duk dai-dai suke da juna

wajen kwana, dangane kuwa da tsawon lokacin rabon shine dare da

yinin da ke biye da shi, saboda manzon Allah tsira da amincin Allah

su tabbata a gareshi ya kasance yanayin hakan. Kamar yadda yake

kuma abu ne da aka samo ta hanyar ruwayoyi mutawatirai daga

wurinsa tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, haka nan rabon

kwana na wajibi shine na dare banda rana. Haka nan ana so a fara da

dare kasancewar shine lokacin kwanciya, matukar dai ba dawowa ya

yi daga tafiya ba, in kuwa hakane to an bashi zavi ya sauka wajen duk

wacce ya ga dama a lokacin da ya dawo. kamar yadda mijin bashi da

ikon ragewa akan dare xaya da yini, ko yayi qari sai da amincewarsu

kasancewar su sune suke da haqqi akan hakan, kuma duk abin da

suka amince da shi ya zama tilas miji ya yi aiki da shi. To amma fa

132

wannan idan matan nasa sauna gari xaya ne ko abin da za a iya yi

masa hukunci da gari xaya idan kuma suka kasance a garuruwa biyu

to ya halalta ayi rabon kowacce juma’a ko wata xai-xai, ko wata

biyu-biyu gwqargwadon abin da zai yiwu, ba tare da cutarwa ba,

kuma haramun ne miji ya shiga wajen kishiyarta a ranar kwanan ta sai

in da wata buqata; buqatar da ba ta jin daxi ba, ya halalta ya gaisa da

kishiyar ta da tambayar halin da take ciki a bakin kofa ba tare da ya

shiga ba, idan kwana ya wuce ta hanyar wucewar lokacinsa ba za’a

ramawa wacce darenta ya wuce ba, ba kuma za a sauya mata da wani

ba, duk a waxannan ba banbanci tsakanin wucewa ta hanyar uzuri ko

ba da uzuri ba, ko kuma ya zalunceta ta hanyar kwana a xakin

kishiyarta kwana biyu, ko kuma ya kwana ne a masallaci a ranar duk

ba za a ramaba. Akwai wasu abubuwa da bai halalta miji ya yi ba sai

da yardar matansa, miji ba shi da ikon qari a kwana xaya da yini ko ya

rage sai da yardarsu, kamar yadda ya gabata, haka nan ba zai zaunar

da su gida xaya ba wanda za su yi tarayya wajen kayan amfani da

suka haxa da wurin wanka da xakin girki da banxaki ba, sai sai da

amincewarsu. Duk wacce ta amince da zama da kishiyar ta a haka,

sannan daga baya ta nemi cin gashin kanta ba za a amsa mata ba, sai

dai idan wani abu ne ya faru da ya jawo hakan. idan kuwa ya zaunar

da matansa a gida xaya kowacce mace tana da xakin ta da xakin

girkinta da xakin wankanta, da ban xakinta na kanta yana da ikon

yin hakan, su kuma ba su da zavi akan hakan kasancewar ya cika

musu haqqinsu na cin gashin kai, kamar yadda miji yana da haqqin

kiransu wani gida nasa na musamman, kowacce a ranar kwananta in

sun yarda da hakan, in kuwa ba haka ba to ba shi da haqqin tilasta su,

amma abin da ya fi dacewa shine ya je gidan kowacce daga cikisu

ranar kwananta, saboda manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata a gare shi haka yake aikatawa. Haka nan ana iya fifita wata

cikin mata matuqar xayar ta yarda da hakan, abin da ake nufi da

fififtawa shine ya fifita kishiyarta akan ta ta hanyar kwana a wurinta

koda yaushe, ko kuma ya yiwa wannaan kwana biyu ita kuma xaya ya

yi mata biyu, in ta yarda kamar yadda ya halalta ya sadu da kishiyarta

a ranar ta, in mai kwanan ta yarda, to amma bai halalta ya sadu da

133

xayarsu a gaban xayar ba, da ittifaqin malamai, ko da kuwa sun yarda

da haka, kamar yadda bai halalta ya kwanta shimfixa xaya tare da su

ba, ko da kuwa ba saduwa zai yi da suba koda kuwa sun yarda, kamar

yadda ba zai shiga da su xakin wanka tare ba koda kuwa sun yarda,

don dukkan waxannan wurare ne da ake zaton buxewar al’aura da

motsa kishi, kamar yadda ya savawa mutunci. Idan mace mai kwana

ta rufewa mijinta qofa, ta hana shi shiga kwanciya a wurinta ta hanyar

yin wani abu da ya hana hakan to za a xauke ta a matsayin mace

wacce ta fanxare don haka ya halalta ga mijin ya kwana a xakin

kishiyarta a wanna daren.

Haqqin kwana wajen mace amarya,

Yaku bayin Allah! Ku sani cewa duk wanda ya auri budurwa alhali

yana da waxansu matan ya zauna wurinta kwana bakwai, in kuwa

bazawarace ya aura zai zauna kwana uku daga nan kuma sai ya faro

lissafi tsakanain ta da kishiyoyinta, ko da sauran matansa ba kuma

dolene sai ya rama musu ba. Saboda faxin manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi yace: “budurwa tana da kwanaki bakwai bazawara kuwa kwana uku”1

a wata riwayar kuma yace: “in kina so in yi miki kwana bakwai in kuma kina so in yi miki kwana uku sannan in kewaya”2, sai manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata agareshi ya bayyana cewa kwana uku ba za a ramasu ga

bazawara ba.Wannan kuma ya samo asaline kasancewa mace Amarya

tana bukatar qarin xauke kewa da walwala don kunyarta ta ragu

duhun kanta ya yi sauqi wanda hakan na buqatar lokaci mai xan

tsawo kafin hakan ta faru, kamar yadda budurwa ta fi bazawara

buqatar hakan, sai aka qara mata kwanakin. Wannan kuma haqqin na

ita matar da ta shigo gida ta yadda ba shi da haqqin qyaleshi sai da

izininta, in kuwa bai yi ba zai rama mata saboda nassin da ya gabata

saboda abin da muka ambata na bukatarta da xauke kewa da cire mata

damuwa.

1 Muwaxxa Malik Takhrijin AbdulBaqi

2 Muwaxxa Malik Takhrijin AbdulBaqi

134

Ya ku bayin Allah! haqiqa aure xabi’ace da Allah Maxaukakin

Sarki ya sanyawa bayinsa hanyar abin da ya sanya musu na sha’awa,

don a samu zuri’a a tsakaninsu da wanzuwar jinsin xan adam, sannan

kuma sunnar Allah ce ta cika raya qasa da kare zuciya da tsare zuri’a

da gina rayuwar iyali da kuma sauke haqqoqin aure da sada zumunta

da taimakon juna da yiwa juna alkhairi da sauransu. Allah

Maxaukakin Sarki yan cewa:

ku auri abin da ya yi muku daxi daga mata; biyu-biyu, da

uk-uku da huxu-huxu,” (Nisa’i: 3) kuma manzon Allah

tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace: “duk

wanda yake da wadatar yin aure bai yi aure ba, ba ya tare

dani” ku yi salati da sallama ga fiyayyen halittun Allah,

annabin rahama kamar yadda mahallicci ya yi mana

Umurni da haka a inda yake cewa: “Lalle Allah da

mala’ikunsa suna salati ga annabi, ya ku waxanda suka yi

imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku yi sallama domin

amintarwa a gare shi (Ahzab: 56)

Ya Allah, ka yi daxin salati ga bawanka kuma manzonka, annabinmu

Muhammad da alayensa da sahabbansa.

135

Huxuba ta Biyu:

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina shedawa babu abin bautawa

da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya, ina

kuma shedawa shugabanmu Annabi Muhammad bawansane kuma

manzonsa ne, tsira da amincin Allah su qara tabbata a gare shi ya yi

masa albarka da alayensa da sahabbansa.

Bayan haka:

Ya ku musulmai ku sani cewa, idan miji ya so yin tafiya to idan

a cikin matansa akwai wacce ba za ya iya yin tafiya da ita ba, aka

kuma samu cewa a cikinsu akwai wacce ta fi tausaya masa da bin

Umurninsa, to wannan zai ba shi uzurin ya yi tafiya da ita, ya kuma

zamo uzuri ga xayar na rashin tafiya da ita, idan kuma su ka yi dai-dai

da juna, sai a duba tafiyar idan ta aikin hajji ce ko yaqi to sai ya yi

quri’a a tsakanin su, ya tafi da wacce quri’arta ta fito, daga nan kuma

ba dole ba ne ya ramawa wacce bai yi tafiyar da ita ba kwanakinta ba

bayan dawowarsa, zai sake lissafin raba kwanaki ne kawai a

tsakaninsu.

Idan kuwa tafiyar ta kasuwanci ce an yo ruwayoyi guda biyu,

xaya ta ce za ayi quri’a, xayar kuma ta ce ba za a yi quri’a ba. Don

haka zavi ya rage gare shi. dalilin da ya sa muka ce zai yi quri’a a

tsakaninsu shine kasancewar annabi tsira da Amincin Allah su

tabbbata a gareshi yana yin quri’a ne.

Ya zo a hadisin da aka haxu akansa (Bukhari da Muslim) daga

Aisha Allah ya yarda da ita ta ce: “lalle annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya kasance idan ya yi nufin zai yi tafiya sai ya yi quri’a tsakanin matansa, duk wacce quri’arta ta fito sai ya fita tare da ita” wannan kuwa ya samo asali ne kasancewar ba wacce a cikinsu ta

fi wata cancanta. Dalilin kuwa da ya sa aka kevance tafiya aikin hajji

da yaqi saboda kasancewarsu sun fi qarfi ta fuskar kasancewarsu duk

jinsin farilla ne, kuma manzon Allah tsira da amincin Allah su

tabbata gare shi bai yi quri’a a savaninsu ba, don haka ana yin ta ne

don koyi.

136

Lalle Allah yana yin umurni da adalci da kyautatawa

ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin

qi da rarrabe jama’ah, yana yi muka gargaxi tsammanin

ku kuna tunawa (Nahl: 90)

137

18

Kyautar Kwana Da Sayar Da Shi

Godiya ta tabbata ga Allah kuma ina shedawa babu abin bautawa da

gaskiya sai Allah, kuma ina shedawa Shugabanm annabi Muhammadu

bawan Allah ne kuma manzonsa ne, ya isar da saqo ya sauke, nauyin

amana, ya yiwa al’umma nasiha ya yi jihadi wajen xaukaka addinin

Allah matuqar jihadi ya barmu akan hanya mai haske wacce hasken

darenta dadai yake da na ranarta, ba wanda zai kauce daga tafarkinta

sai hallakakke. Allah ya yi daxin tsira da albarka bisa alayensa da

sahabbansa da mabiyansa da wanda suka biyo su da kyautatawa har

zuwa ranar sakamako.

Bayan haka, Ya ku mutane! ina yi muku wasiyya da ni kaina da

jin tsoron Allah ku ji tsoronsa. Allah ya yi muku rahama, ku kuma

kasance masu kyautatawa domin Allah Maxaukakin Sarki yana tare

da waxanda suke jin tsoronSa da waxanda su ke masu kyautatawa.

Ya ku mutane! Lalle tsaida adalci al’ada ce da duk wata

al’umma mai daraja ta gaje shi, ta ke kuma samar masa da kariya,

suke kuma gina tsare tsare don tabbatar da cewa ya tabbata ya kuma

kankama a jikinsu. Haka nan adalci abu ne da ya wajaba a yiwa

kowanne mutum na kusa da na nesa, mai qarfi da mai rauni,

mawadaci da matalauci, mazaunin gida da matafiyi, mata da ‘ya’ya

masu hidima da sauransu.

Kyan adalci da qaunarsa abubuwa ne da tun asali aka cusawa

zukata, don haka zukata suke jin daxi idan sun ga alamun adalci

matuqar dai son zuciya bai yi rinjaye ba. Saboda wani al’amari da ya

shafeta musamman ba.

Ya ku bayin Allah! Yana daga cikin adalcin miji ya sanya

kwanan matarsa daga gareta kamar yadda ya halalta ta bayar da

kyautarsa ga kishiyarta idan ta ga damar yin hakan.

138

Asalin inda aka samo wannan mas’ala shine hadisin A’isha

Allah ya yarda da ita. “Haqiqa Saudatu ‘yar Zam’atu ta bayar da kyautar kwananta ga A’isha Allah ya yarda da ita, don haka annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi ya ke raba mata kwananta da na A’isha” Bukhari da Muslim suka ruwaito. Da kuma wani

hadisin na ta dangane da faxar Allah.

“ Babu laifi akansu su yi sulhu a tsakaninsu, kuma yin sulhune mafi alheri” (Nisa’i: 128) sai tace itace mace da take qarqashin

namiji, amma ba ta burgeshi sosai, sai ya yi nufin sakinta ya auri wata,

sai tace da shi ka cigaba da riqe ni kada ka sakeni, sannan ka auri wata

a maimakon haka na halalta maka ciyarwa da rabon kwana a gare ni,

shine faxin Allah maxaukakin sarki: “ ba bu laifi akansu su yi sulhu a tsakaninsu, kuma yin sulhune mafi alheri” (Nisa’i:128). A wata

ruwayar kuma ta ce: “shine namiji ya ga wani abu da ya hana matarsa ta burge shi da ya shafi tsufa ko waninsa, sai ya yi nufin rabuwa da ita, sai tace masa ka cigaba da riqeni ka raba ka bani duk abin da kaga dama, sai ta ce to ba laifi idan suka yi yarjejeniya akan hakan”. To ta

wannan fuskar za mu ga cewa mace da za ta yiwa mijinta kyautar

kwananta, ko ta yi wa kishiyarta, idan har kishiyar ta yi kyautar tilas

ne sai mijin ya karva. Haka nan yana iya mayar da kyautar ga wacce

ta yi kasancewar ta na iya yiwuwa yana da wata buqata gurin wacce ta

yi kyautar. kamar yadda wacce ta yi kyauta ba ta da ikon karve

kyautar tata matuqar mijin ya karva, in kuwa ta yi kyautar nan ga

mijin ba za ta kasance ta shi bace ta yadda zai ba wacce ya ga dama a

maimakon haka za a xauki kwanan nata ne kamar babu shi, don haka

sai kwanan ya koma ga wacce ta ke biye da ita, to idan sun kasance su

huxu ne to rabon kwanan zai zamo na uku ne, idan wacce ta yi

kyautar ita ce mai biyewa wacce yake xakinta sai ya kwana a xakin

wacce ke biye da ita haka nan za a ci gaba.

Haka nan mace wadda ta yi kyauta da kwananta na da ikon

janye kyautarta duk loqacin da ta so, ko dai a dalilin tsananin kishi ta

yadda ba za ta iya cika alqawarin ba. kamar yadda ba banbanci

tsakanin kyautar da aka iyakance da loqaci da wacce ba a iyakance ba.

Haka nan wacce ta bayar da kwananta tana iya janye sauran da suka

139

rage amma banda waxanda suka wuce. kamar yadda miji na iya sayen

kwanan mace daga wurinta ya musanya shi da wani abu da aka

ambata ya zamo rana xaya ko fiye da haka ko na dundundun, ya na

iya kevance wata daga cikin matansa da abin da ya saya, kamar yadda

kuma ya halalta kishiya ta sayi kwanan kishiyarta da ga wurinta ta

yadda za ta kevanta da abin da ta saya.

Kamar yadda ya halalta mace ta ba mijinta wani abu don ya ci

gaba da riqeta kada ya saketa ko da tana da kishiya ko ita kaxai ce.

kamar yadda wata ta daban wacce ba matarsa ba ta na iya bawa miji

wani abu don ya ci gaba da riqe matarsa kada ya rabu da ita. kuma

karvar da miji zai yi baya cikin cin dukiya ta hanyar varna, koda kuwa

ya so ne ya fifita wata a kanta sai ta qi amincewa sai ya bata zavi

kodai saki ko ta amince da fifitawar sai ta yi masa izini saboda haka

dangane da da wannan akwai maganganu guda biyu, to amma an

rinjiyar da halalci saboda qissar Saudatu ‘yar Zam’at Allah ya yarda

da ita.

Kamar yadda miji yana iya bawa mace wani abu don ta cigaba

da zama da shi kada ta nemi rabuwa da shi, ko saboda ta kyautata

zama da shi, kamar yadda ita ma za ta iya ba shi wani abu don ya

kyautata zama da ita.

Ya Allah ka yi daxin tsira da aminci da albarka ga bawanka

kuma manzonka annabi Muhammad da alayensa da sahabbansa. Ya

Allah ka yarda da halifofi shiryayyu shugabanmu Abubakar da Umar

da Usman da Ali da sauran sahabbai ba ki xaya.

140

Huxuba ta Biyu

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina kuma shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah, ina kuma shedawa shugabanmu Annabi

Muhammad bawansane kumsa manzon ne. Allah ya yi xaxin tsira da

aminci da albarka a gareshi da alayensa da sahabbansa.

Ya ku bayin Allah! lalle akwai waxansu fitintinu a al’amarin

kishiyoyi, kishiyar mace ita ce matar mijinta. haqiqa an fitini mata ta

wanna fuskar da bala’i nau’i biyu, bala’in kishi “haqiqa Allah ya rubuta kishi ga mata” da kuma bala’in yi musu kishiya: “biyu-biyu da uku-uku da huxu-huxu. (Nisa’i: 3) don haka wacce aka jarabce ta da

kishi da kishiya sai ta yi haquri tana da ladan wanda ya yi shahada.

kasancewar idan ba ta yi haquri ba hakan na iya kai ta ga kafirci ko

ridda, sau da yawa akwai matan da suka kafirce a sarari ko dai sun

sani ko ba su sani ba, a loqacin da suka yiwa Allah katsalandan

saboda ya halalta yin kishiya, ko kuma ga manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi saboda ya auri mace fiye da xaya,

wannan shine halin da yawa daga cikin waxanda suka samu miji ya yi

musu kishiya. Dangane kuwa da wacce ba ta samu miji ba sai kaji

tana cewa da babu gara ba daxi, kuma da hanau qara mannau”

Kamar yadda waxanda su kai fito na fito da nassosin da suka

shar’anta auren mace fiye da xaya sun manta cewa wanda ya

shar’anta hakan shine wanda ya halicci maza da mata. Kamar yadda

suka halalta baxala da yin qawaye, don haka sai aka jarabcesu da

cututtuka wanda hakan zai qarfafi shari’ar auren mace fiye da xaya

wacce ta haramta baxala da fasiqanci.

Ya ku bayin Allah! Ku ji tsoron Allah a kawunanku, kuma ku

yi aiki da shari’ar Allah, hakanan ku yi qoqarin taimakon juna, da

fahimtar juna da soyayya su yi muku jagoranci don hakan shine halin

musulunci, kamar yadda ya zama wajibi musulmi su aikata shi. Ya

Allah ka xaukaki musulunci da musulmai ka kuma qasqantar da

kafirci da kafirai, ka rusa maqiya addininka kuma ka taimaki bayinka

masu kaxaita Allah.

141

Ya Allah ka amintar da mu a cikin qasashenmu, kuma ka gyara

mu mazanmu da matanmu da jagoranmu, ka gyara jagororin musulmi

baki xaya lalle kai mai iko ne bisa kome, ya Allah ka gafarta mana da

‘yan uwanmu da suka riga mu imani kuma kada ka sanya qunci a

zukatanmu ga waxanda suka yi imani, ya Allah lalle kai mai Tausayi

ne mai rahama. “Ya Allah ka bamu mai kyau a cikin duniya, ka bamu mai kyau a lahira, kuma ka tsare mana azabar wuta” (Baqara: 201)

“Lalle Allah Yana yin umurni da adalci da kyautatawa ma’abocin zumunta, kuma Yana hani ga alfasha da abin qi da rarrabe jama’ah, Yana yi muku gargaxi tsammanin ku kuna tunawa (Nahl:

90).

Ina roqon Allah ya yi mana albarka, ni da ku baki xaya wajen

fahimtar Alqur’ani mai girma ya kuma amfane mu ni da ku da abin da

yake cikinsa na ayoyi da Ambato mai hikima, ya kuma karva mana ni

da ku domin shi mai ji ne kuma masani. Ina roqon Allah ya gafarta

min, ya gafarta muku. lalle shi mai yawan gafara ne mai rahama.

142

19 Bin Iyaye

Huxuba ta Xaya

Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa muna yaba masa muna

neman gafararsa, muna neman taimakonsa, muna tuba a gareshi, muna

dogara da shi, muna kuma neman tsarin Allah daga sharrin

kawunanmu, da miyagun aiyukanmu, muna kuma shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah kuma Muhammad bawansa kuma

manzonsa, Allah ya yi daxin tsira a gare shi da alayensa da

sahabbansa har zuwa ranar sakamako.

Bayan haka:

Ya ku mutane! Ku ji tsoron Allah ga abin da ya wajabta muku na

haqqinsa da kuma haqqin bayinsa da yake kanku, kuma lalle mafi

girman haqqi da yake kanku shine haqqin iyaye da haqqin ‘yan uwa

makusanta domin kuwa Allah ya sanya kowanne haqqi a matakin da

ke biye da haqqinsa wanda yake haxe da na manzonsa. Allah

maxaukakin sarki yace:

Kuma ku bautawa Allah, kada ku haxa wani da shi, kuma

ga mahaifa ku yi kyautatawa, kuma ga ma’abocin

zumunta (Nisa’i: 36).

Allah maxaukakin sarki yace:

kuma mun yiwa mutum wasiyyar kyautatawa ga

uwayensa.”(Ankabut: 8). Kamar yadda ya bayyana

dalilin hakan don jan hankalin ‘ya’ya da kwaxaitar da su

su kula da wannan wasiyya da cewa : “uwarsa ta xauke

143

shi a cikin rauni akan wani rauni” (wato rauni akan wani

raunin da wahala wacce akan wata ta ciki da kuma

loqacin haihuwa), sannan renonsa da da xaukarsa da

shayar da shi kafin a yaye shi Allah maxaukakin sarki

yana cewa: “kuma yayensa a cikin shekaru biyu (muka ce

masa) “ka gode min da kuma mahaifanka biyu, makoma

zuwa gareni kawai take (Luqman: 14).

Kuma ba shakka manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a

gareshi ya gabatar da bin iyaye akan jihadi a cikin hanyar Allah.

Hadisi ya zo cikin Bukhari da Muslim daga Abdullah xan

Mas’ud Allah ya yarda da shi yace: “Na tambayi manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi cewa wanne aiki ne Allah ya fi so? Sai yace: “bin iyaye”sai nace sannan wanne? Sai yace: “jihadi a cikin hanyar Allah”

Ya zo kuma a cikin sahihu Muslim cewa, wani mutum ya zo

wajen manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace:

Ina yi maka mubaya‘a bisa hijira da jihadi ina neman

lada daga Allah sai yace: “shin iyayenka biyu akwai

wanda yake da rai? Sai yace: sai yace qwarai kuwa su

duka biyu suna da rai, sai yace: “kuma kana neman lada

gurin Allah? Sai yace: qwarai kuwa, sai yace: “koma

wajen iyayenka ka kyautata zama da su” haka nan a cikin

wani hadisi da isnadinsa mai kyau ne cewa yayi; wani

mutum yace: “ya ma’aikin Allah ni ina sha’awar jihadi

ne kuma na kasa yinsa, sai yace: “shin daga cikin

iyayenka akwai wanda ya yi saura? sai yace: mahaifiyata,

sai yace: “ka kiyaye haqqoqin Allah wajen kyautata mata

in kayi hakan to ka yi hajji, ka yi Umra, ka yi jihadi,”

Haka nan Allah ya yi wasiyya ga kyautatawa iyaye a duniya ko da

kuwa sun kasance kafirai ne, ko da kuwa suna Umurtar xansu wajen

tarayya da Allah wajen bauta sai dai ba zai yi musu biyayya ba wajen

144

yin kafirci ba. Allah yace: “kuma idan mahaifanka suka tsananta maka ka yi shirka game da addini, ga abin da baka da ilimi gareshi, to kada ka yi musu xa’a. Kuma ka mu’amalance su a cikin duniya gwargwadon shari’a, kuma ka bi hanyar wanda ya mayar da al’amari gareni” (Lukman: 51).

Haka nan ya zo a cikin sahihai biyu (Bukhari da Muslim), daga

Asma’u ‘yar Abubakar Allah ya yarda da su tace: “mahaifiyata ta zo wurina alhalin tana mushrika, wacce Abubakar ya sake tun a Jahiliyya sai ta zo wajen ‘yarta Asma’u a Madina bayan sulhun hudaibiyya. Sai Asma’u tace: sai na nemi fatawar manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi nace: mahaifiyata ta zo tana son in kyautata mata, shin ina iya kyautatawa mahaifiyata ya ma’aikin Allah? Sai yace: “qwarai kuwa ki kyautatawa mahaifiyarki”. Ya ku musulmai! kyautatawa iyaye yana kasancewa ta hanyar

yi musu abin kirki, da kyautata musu ta fuskar yi musu magana da aiki

da dukiya. Kyautata musu a magana shine ka yi musu magana da

tattausan harshe, da magana mai daxi, ta hanyar amfani da kalamai da

ke nuna girmamawa. kyautata musu ta hanyar aiki kuwa shine yi

musu hidima, da hannunka gwargwadon iko wajen biyan buqatunsu

da taimakonsu a cikin al’amuransu, da sauqaqa musu a cikin

al’amuransu, da yi musu biyayya a cikin duk wani abu da ba zai cutar

da kai a addininka ko duniyar ka ba, kada ka manta Allah yana sane

da duk wani abu da zai cutar da kai, in ka yi wani abu don kawai ka

sava musu bayan a haqiqanin gaskiya ba zai cutar da kai ba. kyautata

musu da dukiya kuma ya qunshi wadata su da dukiyar ka a duk

loqacin da suka buqaci hakan cikin daxin rai ba tare da kayi musu

gori ba ko ka cutar da su ba. A maimakon haka ka basu kana jin cewa

su ne suka yi maka alheri ta hanyar karvarsa da yin amfani da shi.

Kuma kamar yadda kyautatawa iyaye yake kasancewa a loqacin

da suke raye, haka nan yana kasancewa bayan rayuwarsu. Haqiqa

wani mutum daga Banu Salama ya zo wajen annabi tsira da amincin

Allah su tabbata a gareshi yace: ya manzon Allah shin akwai wani abu

na kyautatawa iyaye ne da yayi saura bayan rasuwarsu? Sai manzon

Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yace: “qwarai kuwa,

145

yi musu addu’a, da nema musu gafara da zartar da wasiyyarsu, da sadar da zumuntar da ba za ta sadu ba sai da su, da girmama abokansu1

.

Allahu Akbar! Lalle kyautatawa iyaye abu ne mai girma, wanda

ya game komai, ciki har da girmama abokansu da sada zumunta da su

duk yana cikin kyautata musu.

Haka nan ya zo cikin Sahih Muslim daga Abdullah xan Umar

xan Khaxxab Allah ya yarda da su, cewa ya kasance ya bi wata

hanyar Makkah yana haye da jaki yana hutawa akansa idan ya gaji da

hawa taguwa, sai wani balaraben qauye yazo wucewa, sai yace: kai ne

wane xan wane? sai yace: qwarai kuwa, sai kawai ya ba shi jakin,

yace da shi “hau wannan” ya kuma ba shi wani rawani da ke kansa

yace da shi, “xaura akanka” sai suka ce da Abdullahi xan Umar xan

Khaxxab Allah ya yarda da su sai yace: “lalle wannan ya kasance abokin Umar kuma na ji manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi yana cewa: “yana daga cikin kyautatawa iyaye mutum ya sadar da zumunta da masoyin babansa”2

Ya ku musulmai! Wannan shine bayanin matsayin kyautatawa

iyaye da girman martabarsu, sakamakonsa kuwa shine lada mai yawa

a lahira da sakamako kwatankwacinsa a nan duniya don ba shakka

duk wanda ya kyautatawa iyayensa, ‘yayansa’ za su kyautata masa.

haka nan yana daga cikin kyautatawa iyaye yaye musu baqin ciki

kamar yadda ya zo a cikin sahihai biyu (Bukhari da Muslim) daga

hadisin da Umar Allah ya yarda da shi a qissar mutum uku waxanda

kwana ya kama su a wani kogo sai suka shige, sai wani dutse ya toshe

qofar kogon da su suna ciki sai xayan su yace: “ya Allah haqiqa ya kasance ina da iyaye biyu tsofaffi sun manyanta kuma na kasance bana ciyar da wani kafinsu ko iyali ko dukiya, sai wata rana neman abin kiwo ya sa nayi nisa ban dawo wajensu ba har suka yi barci, a loqacin dana tatso musu abincinsu sai na same su sun yi barci, sai naci gaba da tsayuwa da qwarya a hannuna ina jiran farkawarsu har sai da

1 Sunan Ibn Majah

2 Musnad ashshihab al kada’I da Sunan Ibn Majah

146

alfijir ya keto sannan suka ta shi suka ci abincinsu, ya Allah idan nayi wannan ne don neman yardarka ka yaye mana abin da muke ciki na wannan dutse, sai dutsen ya buxa xan kaxan, sai suma abokansa su kayi tawassuli da kyawawan aiyukan su sai dutsen ya buxe gaba xaya, suka fito suna tafiya da qafafunsu” kuma haqiqa kyautatawa iyaye na

jawo yalwar arziki, da nisan kwana, da kyakkyawan qarshe. An karvo

daga Ali xan Abu Xalib Allah ya yarda da shi, lalle annnabi tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi yace: “duk wanda zai yi farin cikin Allah ya yi masa nisan kwana, ya yalwata masa arziqinsa, ya kuma kare shi daga mummunan qarshe to ya ji tsoron Allah, ya kuma sadar da zumunta”.1 haka nan kyautatawa iyaye shine qololuwar nau’in

sadar da zumunta domin sune waxanda suka fi kowa kusanci da kai ta

fuskar dangantaka.

1 Mussnad Ahmad da Sahih Albukhari

147

Huxuba ta biyu:

Godiya ta tabbata ga Allah shi kaxai, ina kuma shedawa babu abin

bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake ba shi da abokin tarayya,

ina kuma shedawa Annabi Muhammad bawansa ne kuma manzonsa

ne, tsira da amincin Allah da albarkarsa su tabbata a gareshi da

alayensa da sahabbansa.

Ya ku mutane!

Haqiqa ba ya dacewa da duk wani mai hankali da ya san falalar

kyautatawa iyaye da kyakkyawan sakamakonsa a duniya da lahira,

sannnan kuma ya yi watsi da shi ya qi tsayawa da shi, ko kuma ya

sava musu ya yanke zumuntarsa, haqiqa Allah maxaukakin sarki ya yi

hani da savawa iyaye a loqacin da kyautata musu ya fi kowanne

tsanani. Allah maxaukakin sarki yana cewa: “kuma Ubangijinka ya hukunta kada ku bautawa kowa face shi, kuma game da mahaifa biyu ku kyautata musu ko da xayansu ya kai ga tsufa a wurinka ko dukansu biyun, to kada kace musu tir, kuma kada ka tsawace su kuma ka faxa musu magana mai karamci. Kuma ka sassauta musu fukafukan tausayawa na rahama kuma kace Ubangiji ka yi musu rahama kamar yadda suka yi reno na ina qarami” (Isra’: 23-24)

A irin wannan yanayi na kaiwar iyaye matakin girma ake

samun rauni na jiki da na hankali, kamar yadda a waxansu lokuta ma

sukan kai mafi qasqancin shekaru wanada shine dalilin damuwa ko

kuma qosawa da su, to a irin wannan loqaci ne Allah ya yi hani da ya

nuna qosawarsa da iyayensa biyu, ya yi masa Umurnin ya yi musu

magana ta giramamawa, ya kuma qasqantar da kansa daga gare su ya

kuma shimfixa musu tausayi, ya yi musu magana irin ta wanda bai

xauki kansa a bakin komai ba a gabansu, ya yi musu mu’amala irin ta

mai hidima wanda ke qasqantar da kansa a gaban maigidansa, don

tausaya musu da kyautata musu, ya kuma roqa musu jin qai a wurin

148

Allah, kamar yadda su ka ji qansa a loqacin yana qarami a loqacin

yana cikin tsananin buqata suke rene shi.

Lalle ya zama wajibi akan mumini ya tsayu akan kyautatawa

iyayensa, kada kuma ya manta da kyautatawar da suka yi masa yana

qarami, baya iya amfanar kansa ko ya kare kansa daga cutarwa, ita

kuwa mahaifiyarsa ta hana idanunta barci don shi yayi barci, saboda

shi ta hana jikinta hutu saboda shi ya huta, shi kuwa mahaifinsa ya

karaxe ko ina ya rasa kwanciyar hankali, saboda tunanin yadda zai

samo musu abin da za su rayu da shi, ya kuma kula da shi don haka

kowannensu ya wajaba a gareshi ya kyautata musu sakamakon

aikinsu.

Ya zo a cikin Sahihai biyu (Bukhari da Muslim) daga Abu

Huraira cewa, wani mutum yace: “ya manzon Allah a cikin mutane waye ya fi cancanta in kyautatawa mu’amalata? Sai yace: mahaifiyarka, yace: sannan wa? Yace: “mahifiyarka”sai yace: sannan wa? Yace: “mahaifiyarka” yace: sannan wa? Yace: “mahaifinka”

Muna roqon Allah ya bamu dacewa da kyautatawa iyayenmu

mata da maza, ya kuma ba mu damar yin hakan don Allah da

kyakkyawan nufi da tsayuwa akan dai-dai, lalle shi mai yawan kyauta

ne kuma mai karamci.

Ina faxin wannan magana tawa ina neman gafarar Allah gare ni

da gare ku, ku nemi gafararsa don shi mai yawan gafara ne mai yawan

jinqai.

149

20

Aikin Mace Da Matsayinta A Musulunci

Huxuba ta Xaya

Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu, kyakkyawan sakamako

na ga masu taqawa, kuma babu qiyayya sai ga azzalumai, kuma ina

shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah wanda shine

majivincin lamarin salihai, ina kuma shedawa shugabanmu Annabi

Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, wanda shine cikamakin

annabawa shugaban mursalai, jagoran masu hasken goshi da qafafuwa

da alayensa da sahabbansa da waxanda suka biyo su da kyautatawa

har zuwa ranar sakamako.

“Ya ku waxanda suka yi imani! Kubi Allah da taqawa akan

haqqin binsa da taqawa kuma kada ku mutu face kuna masu

sallamawa’’ (A’li-imran: 102). “Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne”.

(Nisa’i: 1) Allah maxaukakin sarki yana cewa: “Allah yana yi muku wasiyya a cikin ‘yayanku’, namiji yana da rabon mata biyu. Idan sun kasance mata ne fiye da biyu kuwa, to suna da biyu daga kashi uku xin abin da ya bari, kuma idan ta zamo guda ce (kawai), to tana da rabi. kuma iyayensa biyu ko wanne xaya daga cikinsu yana da kashi xaya daga cikin kashi shida xin abin da ya bari idan yana da xa (na miji), idan ko ba shi da xa kuma, iyayensa ne kawai zasu gajeshi to uwa tana da xaya daga cikin uku, sannan idan ‘yan’uwa sun kasance gare shi, to uwarsu tana da xaya daga cikin kashi shida bayan wasiyya wacce ya yi ko kuwa bashi. Ubanninku da ‘ya’yayenku ba ku

150

sani ba, waxannen su ne mafi kusantar amfani a gareku. hukunci ne daga Allah. lalle ne, Allah ya kasance masani ma haikima”

(Nisa’i:11)

Haqiqa Allah Maxaukakin Sarki ya saukar da sura guda a cikin

littafinsa wacce ya kira da surar mata,wacce ita ce sura ta uku a

manyan surori bayan fatiha, don haka za mu ga cewa an gabatar da

mace a farkon Alqur’ani mai girma, kamar yadda a duk Alqur’ani

babu surar da aka kira ta da sunan maza, ko sura da sunan annnabi

Adam amincin Allah ya tabbata a gareshi, sai dai a cikinsa akwai

suratul Maryam, da suratul Al’imran, da suratul Mujadalat, da suratul

Mumtahana, dukkan waxannan surori ne da manyan darussan da suke

koyarwa, shine mace da girman darajarta da xaukakar matsayinta da

kuma muhimmancin ta da musulunci ya ba ta. Ba shakka Allah

Maxaukakin Sarki ya ambaci mata a cikin suratul nisa’i, ya kuma rufe

ta da ambaton mata. aya ta farko tana cewa: “Ya ku mutane ku bi Ubangijinku da taqawa, wanda ya halicce ku daga rai guda, kuma ya halitta daga gare shi ma’auransa, kuma ya watsa daga garesu masu yawa maza da mata. Kuma kubi Allah da taqawa wanda kuke roqon juna da (sunan) Shi, da kuma zumunta lalle ne Allah ya kasance akanku Mai tsaro ne. (Nisa’i:1) ya kuma cika ayoyinta da ambatonsu

inda yake cewa: “kuma idan sun kasance ‘yan’uwa maza da mata, to namiji yana da misalin rabon mata biyu… (Nisa’i:176).

Sai aya ta farko ya tabbatar da asalin xan Adam guda xaya ne

maza da mata da: “ya ku mutane lalle babanku xaya ne dukka daga Adam kuke, adam kuwa an halicceshi daga qasa” Bazzar ya ruwaito

kamar yadda ya zo a cikin aljami Assagir. Aya ta qarshe kuma, sai

ya ambaci haqqinta na mallaka da kasonta na gado da ta riqe kuxi ta

ci gashin kanta. A suratul Mujadala kuma ya tabbatar da haqqinta ne

na kai qara idan tana da qorafi da kuma wajabcin sauraron qarar tata

idan ta kai qara, Allah maxaukakin sarki yace: “lalle Allah ya ji maganar wadda ke yi maka jayayya game da mijinta, tana kai qara ga Allah” (Mujadalah: 1). Wannan mata kuwa itace Khaulatu ‘yar

Sa’alabatu, wata rana Umar xan Khaxxab Allah ya yarda da shi ya

zo wucewa yana haye da jaki, mutane suna tare da shi, sai ta tsayar da

151

shi loqaci mai tsawo ta yi masa wa’azi tace: “ya Umar a da ka kasance ana kiranka Umair, sannan aka kira ka da Umar ,sannan aka kira ka da Amirul Muminin, ka ji tsoron Allah ya kai Umar, duk wanda ya tabbata zai mutu ba shakka zai ji tsoron gafala, duk wanda ya sakankance da hisabi zai ji tsoron azaba”, shi kuwa sai ya yi tsaye

kawai yana sauraran maganarta.

Sai aka ce masa: ya Shugaban Muminai me ya sa ka tsayawa

wannan tsohuwa na tsawon loqaci haka? Sai yace: “wallahi da za ta tsare ni tun daga farkon safiya har zuwa qarshen yammaci ba zan gushe ba in ban da lokutan sallolin farilla, ko kun san wannan wacce tsohuwa ce? Ita ce Khaulatu ‘yar Sa’alabatu wacce Allah ya ji maganar ta daga saman bakwai, shin kuna ganin cewa ubangijin halittu zai ji maganarta, Umar kuma yaqi ji, (Tafsirin Tabari 17: 269)

A nan sai musulunci ya tabbatar mata da haqqin kai qara da

neman haqqinta, a duk loqacin da ta ga dama, ga duk wanda ta ga

dama. Kamar yadda aka tabbatar a littafin (al-qada’a) da (adda’awa).

Allah kuma ya rusa al’adar nan ta zihari ta jahiliyya da li’aninta a

dalilin kawo qararta da kai komo wurin manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi. wanda ada su zihari da li’ani duk

su a wrinsu saki ne, don haka sai aka sanyawa zihari kaffara kamar

yadda aka yi bayani a fasalin zihari, wanda da zarar ya yi kaffara to ta

koma matarsa kamar yadda take a baya.

A cikin suratul Muntahana kuma an daidaita tsakanin maza da

mata ta fuskar amincewa da mubaya’arsu bisa musulunci, aka kuma

tabbatarwa da mace haqqin hijira daga qasar abokan gaba a loqacin

da ta musulunta da rabuwa da mijinta kafiri wanda bai musulunta ba.

Ya ku bayin Allah! An saukar da sura ta musamman aka kira ta da

suna suratut Xalaq wanda a cikin ta aka yi bayanin saki filla-filla da

hukunce-hukuncen idda don kare martabarta da kyakkyawan sunanta,

da martabar tsatsonta, da zuriyarta. Don Allah ku dubi yadda

musulunci ya kula da mace ya kuma ba ta muhimmanci. ku duba

yawan abubuwan da ya shar’anta mata, da yawan ayoyin da aka

saukar, da yadda ake ta anbatonta a Alqur’ani aka kuma kira surori da

sunanta a Alqur’ani, da kuma yawan wasiyyoyin da aka yi don a

152

kyautata mata don a kare matsayinta, aka wajabta girmama ta da kare

haqqoqinta, a matsayinta na uwa da ‘ya da matar aure, da ‘yar uwa

muharrama da wacce ba muharrama ba. To amma duk da haka sai ka

ga waxansu mata na jayayya da wannan addini mai girma. Haka nan

bai dai-daita tsakaninta da maza ababen tausayi ba. Allah Maxaukakin

Sarki yana cewa annabi Adam amincin Allah ya tabbata a gare shi

yana yi masa gargaxi da Iblis, la’anar Allah ta tabbata a gareshi.

“Sai muka ce, ya Adamu! Lalle ne wannan maqiya ne

gareka da kuma ga matarka, saboda haka ya fitar da ku

daga aljannah ka wahala” (Taha: 117).

Sai ya kevance shi da wahala, ban da ita bai ce ku wahala ba, to amma

wai duk da haka sai kaji mata wai tana burin kasancewa kamar namiji.

Ya ku bayin Allah! Ba shakka mace bata son saki bata qaunar saki,

tana kuma tsanar saki musamman ma idan kansu ya haxu da mijinta.

Haka nan Allah Maxaukakin Sarki ba ya son saki, annabi tsira da

amincin Allah su tabbata a gare shi yana yin fushi da saki, haka nan

mala’iku suna yin fushi da saki domin ko duk abin da Allah yake

fushi da shi, mala’iku ma suna fushi da shi. Domin Allah yana cewa

ga wanda yake so: “lalle ne ni ina son wane kuma ku soshi” haka nan

zai ce dangane da wanda yake qi “lalle ne ni ina fushi da wane kuma ku yi fushi da shi” Ahmad ya ruwaito shi.

Iblis kuwa la’anar Allah ta tabbata a gare shi, yana son saki,

yana qaunar ayi saki, haka nan yana bayar da sakamako idan an yi

saki, haka nan duk shaixan na mutane da na aljanu suna son saki,

musamman ma idan ya kasance tsakanin ma’aurata ne masu kirki

masu qaunar juna da son addini.

Ya ku ‘yan’uwa na a imani! Don Allah ku dubi abin mamaki

wai duk da waxannan abubuwa da ake faxawa mumini amma sai kaga

yayi saki, musamman ma a loqacin da za’a iya dai-daitawa, akwai

sauran qauna da soyayya komai qanqantarta, haqiqa manzon Allah

tsira da amincin Allah su tabbata gare shi yana cewa:

153

Lalle kada mumini ya musgunawa mumina, in yaqi wani

hali nata zai amince da wani. Ahmad ya ruwaito.

Don haka idan zamantakewa ta qi daxi so da qauna suka yanke aka

rasa yadda za a yi a dai-daita tsakanin miji da matarsa, kuma mace

taga cewa tana son ta wayi gari ita ce zata rinqa saka maimakon a

saketa, ta rabu da miji maimakon ya rabu da ita don tana ganin cewa

sakinta qasqanci da wulaqanci ne, kuma saki abu ne mai arha qaddara

ce da bata da qima, tana son ta wayi gari ta ce masa na sakeka, da abin

da zai biyo bayan hakan shine nadama,ba shakka da wuya ka samu an

yi saki kuma kowa yana farin ciki sai dai a manyan laifuka da

munanan halaye da mugwayen xabi’u, a loqacin da ba ta yadda

za ayi a sami haxin kan juna, wanda saboda irin wannan yanayi ne aka

shar’anta saki.

Ya ku bayin Allah! A duk loqacin da saki ya auku sai nadama

ta biyo bayansa, miji ya wayi gari yana faxa a cikin ransa ina ma da

ace mahaifiyarsa ba ta haife shi ba, ita kuwa mace ta rinqa cewa: “in

da na mutu kafin wannan loqaci da tuni an mance da ni”. Wannan

yana faruwa ne kasancewar matuqar saki ya auku to ba za a iya janye

shi ba, kamar yadda idan ya kai uku ko da wanda ba kome ne to ba

yadda za a yi. Don Allah ku yi nazari ku gani cewa rantsuwa ana iya

yi mata kaffara ta hanyar ciyar da miskinai goma, shi kuwa saki ba shi

da wata kaffara sai rabuwa. “Kuma lalle ne Allah bai zama mai zalunci ga bayinsa ba” (Al-imran: 182). Haka nan a loqacin da akai

saki suka yi nadama baki xayansu tana iya yiwuwa su haxu a voye ko

su qirqiri wata kalma ta qarya ya faxawa alqali, da zaton cewa zasu

iya voyewa masanin fili da voye; ko kaxan, “lalle shi yana da sanin asirin da abin da ya fi voyuwa” (Xaha: 7).

Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi. Ya ku

waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku

yi sallama domin amintarwa a gare shi. (Ahzab: 56)

154

Huxuba ta biyu

Godiya ta tabbata ga Allah wanda ya halicci namiji da mace, wanda

yake shine mai fararwa da dawowa, wanda yake da tsananin kamu,

wanda shi yake aikata abin da yayi nufi, ina yaba masa, ina gode

masa, don ta hanyar gode masa ne ni’ima take dawwama. kuma ina

shedawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah shi kaxai yake, ba

shi da abokin tarayya, kuma ina shedawa shugabanmu Annabi

Muhammad bawansa ne kuma manzonsa ne, Allah ya yi daxin tsira da

aminci a gareshi da alayensa da sahabbansa.

Bayan haka, Ya ku ‘yan’uwa! Ku ji tsoron Allah zai gyara

muku aiyukanku ya kuma gafarta muku zunubanku, duk wanda ya yi

xa’a ga Allah da manzonsa haqiqa ya rabauta rabo mai girma. Allah

maxaukakin sarki yace:

Maza masu tsayuwa ne akan mata saboda abin da Allah

ya fifita sashensu da shi akan sashe, kuma saboda abin

da suka ciyar daga dukiyoyinsu. To salihan mata masu

xa’a ne, masu tsarewa ga gaibi saboda abin da Allah ya

tsare. (Nisa’i: 24).

Ya ku bayin Allah! Wai ko menene ya ke sa mace take son ta kasance

itace a sama? Bayan kuma Allah Maxaukakin Sarki ya halicci namiji

sama da mace? Ya sanya mace qarqashin namiji? domin kuwa har

larabawa su kan ce wance a qarqashin wane take wato matarsa ce,

Allah Maxaukakin Sarki yana cewa: “Allah ya buga wani misali domin waxanda suka kafirta matar Nuhu da matar Luxu, sun kasance a qarqashin wasu bayi biyu daga bayinmu salihai sai suka yaudaresu, saboda haka ba su wadatar musu da komai ba daga Allah ba” (Tahrim:

10). Ba shakka Allah ya sanya namiji sama da mace da dukkan

abubuwan da za su ba shi dama ya tsayu da aikinsa wanda Allah ya

halicce shi dominsa, kamar yadda ya sanya mace ta banbanta da shi da

kowanne abu da zai bata dama ta yi aikin da aka halicce ta dominsa.

155

Don haka sai ya sanya namiji sama da ita da darajoji “kuma maza suna da wata daraja a kansu” (Baqara: 228) haka nan da fifiko, “ maza masu tsayuwa ne a kan mata, saboda abin da Allah ya fifita sashensu akan sashe” da kuma ciyarwa “ saboda abin da suka ciyar daga dukiyoyinsu”(Nisa’i: 34), haka nan a wurin sheda: “to idan basu zamo maza biyu ba, to namiji guda da mata biyu daga waxanda kuka yarda da su daga shedu”(Baqara: 282). Haka nan ta fuskar addini, “suna yin tasbihi a gareshi a cikinsu, safe da maraice waxansu maza” (Nur: 36-

37).

Ku saurara! Ku yi salati da sallama ga rahama mai shiryarwa da

ni’ima mai yawa, annabinmu Muhammad manzon Allah tsira da

amincin Allah su tabbata a gareshi, lalle Allah yana yi muku Umurni

da haka yace:

“Lalle Allah da mala’ikunsa suna salati ga annabi, ya ku

waxanda suka yi imani! Ku yi salati a gare shi, kuma ku

yi sallama domin amintarwa a gare shi. (Ahzab: 56)

Allah ya yi daxin tsira da aminci a gareshi da alayensa da

sahabbansa.

Ya Allah ka yarda da halifofinsa shiryayyu, Abubakar, da Umar, da

Usman da Ali da sauran sahabbai da tabi’ai da waxanda suka biyo su

da kyautatawa har zuwa ranar sakamako. ka haxa mu da su da

afuwarka da kyautatawarka ya mafi karamcin masu karamci.

Lalle Allah yana yin umurni da adalci da kyautatawa

ma’abocin zumunta, kuma yana hani ga alfasha da abin

qi da rarrabe jama’ah, yana yi muku gargaxi tsammanin

ku kuna tunawa (Nahl: 90).

Ku miqe domin yin sallah, – Allah ya yi muku rahama.