gudummuwar malamai da jami'ai wajen aikin hajji
TRANSCRIPT
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai
da Malamai Masu Gabatar Da Bita Wajen
Gudanar Da Aikin Hajji Cikin Sauqi
Na
Ahmad Bello Dogarawa Sashin Koyar Da Aikin Akanta, Jami’ar Ahmadu Bello, Zaria
A Matsayin Takarda Da Aka Gabatar Wajen Taron Qara Wa Juna Sani, Da
Hukumar Kula Da Jin Daxin Alhazai Ta Jahar Neja Ta Shirya Wa
Jami'anta Da Malamai Dake Gabatar Da Bita Ga Maniyyata Aikin Hajji
Asabar, Sha'abaan 8, 1429 (Saturday, August 9, 2008)
Shafi na 1 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
1. GABATARWA
Akwai kusan ayoyin Alqur'ani guda talatin da tara (39) da suka yi magana
a kan Hajji.1 Waxansu ayoyin sun bayyanar da Hajji a matsayin xaya daga
cikin rukunan Musulunci, waxansu kuma suka bayyana ayyukan Hajji, da
manufofi, da hikimomi, da falala, da alheran da aikin ya qunsa.
Allah ( ) Ya shar’anta Hajji don tabbatar da manufar tauhidi da
samar da cikakkiyar `yan’uwantaka, ta yadda Musulmi daga kowane
vangare na duniya ke haxuwa a Makka don gabatar da ayyukan bauta da
samun tarbiyya, da gyaran zuciya da guzurin duniya da lahira.
Wannan takarda ta qunshi tattaunawa ce game da Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malaman da ke Gabatar da Bita wajen Gudanar da Aikin Hajji cikin sauqi. A matsayin shimfixa, takardar za ta yi tsokaci a
kan matsayi da falalar Hajji a Musulunci, da kuma yadda ake samun hajjun
mabrur ( ), wato, aikin Hajji nagartacce/karvavve.
1 Baqara (2:125-128; 158; 189; 196; 197-203); Aal Imraan (3:96-97); Maa'idah (5:1-2; 95-
97); Taubah (9:3; 19; 28); Hajj (22:27-37).
Shafi na 2 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
An raba sauran bayanan da ke qunshe a cikin takardar gida uku: gava ta
gaba za ta yi magana ne a kan matsayi da falalar Hajji a Musulunci, da
kuma yadda ake samun hajjun mabrur. Kashi na biyu zai yi magana a kan
gudummuwar da jami'an hukumar Alhazai da malaman da ke gabatar da
bita za su ba da wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. Vangare na uku
zai qunshi godiya da kammalawa.
2. HAJJI A MUSULUNCI
Hajji na xaya daga rukunan Musulunci guda biyar. Alqur’ani da Sunnah da
Ijma’i duk sun tabbatar da wajibcin yin aikin Hajji sau xaya a cikin
rayuwa2 a kan kowane mukallafi (musulmi, baligi, mai hankali), namiji ko
mace, mai `yanci, da ke da iko (istixaa’ah).
Allah ( ) Ya ce:
Kuma Allah Yana da haqqi a kan mutane na yin Hajjin Xaki, ga wanda ya samu ikon zuwa gare shi, kuma wanda ya kafirce, lallai Allah Mawadaci ne ga barin talikai.3
Manzon Allah ( ) ya ce:
Ya ku mutane, haqiqa Allah Ya farlanta Hajji a kanku, (sabo da haka) ku yi Hajji.4
Haka nan, Manzon Allah ( ) ya ce:
Ku yi gaggawar zuwa Hajji, domin xayanku bai san abin da zai bijiro masa ba (wanda zai iya hana shi zuwa aikin Hajji daga baya).5
A magana mafi qarfi da inganci, an farlanta Hajji ne a shekara ta tara da
Hijra ( ); wato shekarar da Manzon Allah ( ) ya naxa
babban sahabinsa, Abubakar ( ) a matsayin shugaban Alhazai. A
shekara ta goma, Manzon Allah ( ) ya jagoranci dubban
2 Ko da yake aikin Hajji wajibi ne sau xaya a cikin rayuwa, duk lokacin da mutum ya yi
bakance (alwashi) cewa zai yi aikin Hajji, Hajji ya wajaba a kansa 3 Aal Imraan 3:97
4 Muslim
5 Ahmad ya ruwaito, kuma al-Albani ya ce Hasan ne a cikin Irwaa’ul Ghaleel
Shafi na 3 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Sahabbai zuwa aikin Hajjin ban kwana ( ). Ke nan, Manzon Allah
( ) sau xaya ya samu damar yin aikin Hajji a rayuwarsa, ko
da yake ya yi aikin Umrah kafin wannan lokaci.
Hajji na da falala mai yawan gaske. Daga cikin falalar Hajji akwai:
1. Hajji na kankare zunuban da suka gabata, ya rushe su, kuma ya
laqwame su. Manzon Allah ( ) ya ce:
Wanda ya yi (aikin) Hajji, bai yi jima’i (ko wani abu da zai kusantar da shi zuwa ga jima’i) ba, kuma bai yi aikin fasiqanci ba, zai koma kamar ranar da uwarsa ta haife shi (sabo da rashin zunubi)6
Haka nan, Manzon Allah ( ) ya ce wa sahabinsa `Amr
bn al-`Aas ( )
Ba ka san cewa Musulunci na rushe (zunuban da aka yi) kafin (a shige) shi ba, kuma Hijira na rushe abin da aka yi (na zunubai) kafin ita ba, kuma Hajji na rushe abin da aka yi kafin shi ba?7
2. Hajji na daga dalilai na samun `yanci daga wuta. Manzon Allah (
) ya ce:
Ba bu wata rana da Allah Ya fi `yanta bawa daga wuta fiye da ranar Arfah8
3. Hajji da Umrah na kore talauci. Manzon Allah ( ) ya
ce:
Ku bibiyi aikin Hajji da Umrah, domin suna kore talauci da zunubi kamar yadda zugazugi ke kore duddugar qarfe da zinare da azurfa.
9
6 Bukhari da Muslim
7 Muslim
8 Muslim
9 Ahmad, Tirmidhi da Ibn Majah
Shafi na 4 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
4. Hajji na xaya daga cikin ayyukan da suka fi falala. An tambayi
Manzon Allah ( ) game da ayyukan da suka fi falala,
sai ya ce:
Imani da Allah Shi kaxai, sa’an nan Jihadi, sa’an nan Hajjun Mabrur (Hajjin da aka yi shi kamar yadda Shari’a ta ce). Tsakanin hajjun mabrur da sauran ayyuka, kamar tsakanin mahudar rana ce da mafaxarta10
5. Hajji shi ne jihadi mafi falala ga mata. A’isha ( ) ta ce wa
Manzon Allah ( ) ‘Ba za mu yi jihadi ba’? sai ya ce:
A’a, kuna da jihadi mafi falala da za ku yi: Hajjun Mabrur.11
6. Hajji da Umrah su ne jihadin tsofaffi da yara da masu rauni. Manzon
Allah ( ) ya ce:
Jihadin tsofaffi da yara da masu rauni da mata shi ne: Hajji da Umrah.12
7. Mahajjata baqin Allah ne da ake ba su abin da suka roqa. Manzon
Allah ( ) ya ce:
Mai yaqi fisabilillah, da mai Hajji, da mai yin Umrah (dukaninsu) baqin Allah ne; Ya kira su, sun amsa kiran, kuma suka roqe Shi (buqatunsu) Ya ba su.
13
8. Aljanna ce sakamakon aikin Hajji. Manzon Allah ( )
ya ce:
Kuma aljanna ce sakamakon Hajjun Mabrur14
10
Ahmad da Xabaraani. Kuma Bukhari da Muslim su ruwaito da lafazin da bai kai wannan
tsawo ba 11
Bukhari, Nasa’i da Ibn Majah 12
Nasa’i 13
Ibn Majah da Ibn Hibbaan 14
Bukhari da Muslim
Shafi na 5 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Daga abin da ya gabata, Manzon Allah ( ) ya bayyana cewa
aljanna ce sakamakon Hajjun Mabrur. Imam al-Qurxubi ya bayyana
ma’anar Hajjin da ake kira mabrur a cikin tafsirinsa, kuma Ibn Hajar, a
cikin Fathul Baari, ya qarfafi cewa shi ne aikin Hajjin da aka cika
hukunce-hukuncensa kuma aka gabatar da shi yadda Shari’a ta ce, a bisa
fuska mafi cika.
Al’amuran da ke taimaka wa maniyyaci samun nagartaccen aikin Hajji
domin kai wa ga Hajjun Mabrur sun haxa da:
1. Tsarkake niyya (ikhlasi) da koyi da Manzon Allah (
) a cikin dukan ayyukan Hajji (mutaaba'ah).
2. Tattali da tanadi da kintsi ta hanyar tuba daga zunubansa, tun
kafin lokacin tafiya; neman taimako da dacewa daga Allah, da
bayyanar da tsananin buqata zuwa gare Shi, da tsoron azabarSa da
kwaxayin rahamarSa; kuvuta daga haqqoqin wasu, da mayar da
kayan da aka ba shi ajiya, da biyan bashin da ake binsa, da sanar
da `yan’uwa da maqwafta da abokan arziqi cewa zai yi tafiya,
kuma ya nemi su yi masa addu’ar dacewa da samun qabuli daga
Allah; samun tsarkakakken guzuri, kasancewar guzurin da ya ke
na haram na da mummunan tasiri a kan addu’o’in da mahajjaci zai
yi a halin da ya ke aikin Hajji; tanadi wadatacce ga iyalinsa da
sauran waxanda ke qarqashinsa gwargwadon ikonsa, kafin ya tafi
aikin Hajji; zaven abokai na qwarai waxanda za su taimaka wa
mahajjaci idan ya yi rauni, su cincixa shi idan ya gaza, su tunatar
da shi idan ya manta, su ilmantar da shi idan ya jahilta, su umurce
shi da kyakkyawa su hana shi mummuna; qoqarin fahimtar
hukunce-hukuncen aikin Hajji da ladubbansa, da abubuwan da ke
gyara shi da waxanda ke vata shi, da hukunce-hukuncen da suka
shafi tafiya da sallar qasaru, da dai sauransu.
3. Fahimtar manufa da hikimomin aikin Hajji da suka haxa da: miqa
wuya ga umurnin Allah da sallamawa tare da jawuwa gare Shi;
tabbatar da tauhidi; girmama abubuwan da Allah ( ) Ya yi
umurni da a girmama su; son Manzon Allah ( ) ta
hanyar koyi da shi a cikin ayyukan Hajji gaba xaya; tunawa da
ranar Lahira ta hanyar tuna mutuwa da barin duniya zuwa lahira a
lokacin da maniyyaci ya fito daga gidansa, da tuna likkafani a
lokacin da ya sanya haraminsa, da tuna tsayuwa a gaban Allah a
Shafi na 6 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
ranar Qiyama domin yin hisabi a lokacin da ya ga matsatsar
mutane, ya ji xaga muryoyinsu da bambancin yarensu; tabbatar da
tsoron Allah da taqawa ta hanyar kiyaye dokokin Allah domin
samun guzuri mafi alheri; samun cikakkiyar tarbiyya da
kyawawan xabi’u da suka haxa da kamun kai, kame fushi da
rashin husuma da barin jayayya mara dalili, tausasawa da
natsuwa, qanqan da kai, haquri, kyauta, da taimakon juna;
taimakekeniya da `yan’uwantaka da haxin kai a tsakanin
Musulmi; da yawaita zikirin Allah.
4. Qoqari wajen xa’a ga Allah da amfani da lokaci yadda ya dace ta
hanyar yawaita karatun Alqur’ani da zikiri da istigfari da sallar
nafila da halartar wuraren da ake yin karatu da wa’azi. Haka nan
an so mahajjaci ya zamanto mai kyauta gwargwadon iko, da
taimakon `yan’uwansa, da qoqarin kawo amfani ga juna, da
umurni da kyakkyawa da hani da mummuna, da yawaita addu’a
da roqon Allah buqatu na alheri.
5. Nisantar zunubi da savon Allah a wajen aikin Hajji, da dagewa a
kan xa’a tun daga farkon aiki har zuwa qarshe.
3. GUDUMMUWAR MALAMAI DA JAMI'AN HUKUMAR
ALHAZAI WAJEN GUDANAR DA HAJJI A CIKIN SAUQI
Hajji ibada ce da ke buqatar cikakken shiri da kintsi da tanadi da tattali
daga maniyyata, da kuma kulawa ta musamman da jagoranci da xaukar
xawainiya daga shugabanni, tare da ilmantarwa daga malamai (tun daga
matakin bita har zuwa faxakarwa da ba da fatawa a lokacin aikin Hajji).
A wannan gava, takardar za ta yi tsokaci a kan irin gudummuwar da
jami'an hukumar Alhazai da malaman da ke gabatar da bita ga maniyyata
za su ba da wajen gudanar da ayyukan Hajji cikin sauqi.
3.1 GUDUMMUWAR MALAMAI
Ilmantar da maniyyata game da aikin Hajji abu ne muhimmi, kasancewar
ya qunshi karantar da su hukunce-hukuncen aikin Hajji da ladubban da ya
kamata mahajjaci ya kiyaye tun kafin ya bar Nijeriya zuwa qasar
Saudiyyah har ya dawo. Wannan kuma aikin malamai ne. Kenan, malamai
Shafi na 7 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
na da babbar gudummuwa da za su ba da wajen gudanar da aikin Hajji
cikin sauqi da nasara.
Akwai vangarori guda huxu da malamai za su taimaka don cinma wannan
manufa:
3.1.1 Fahimtar da Maniyyata Manufofin Hajji ( )
Hajji na da manufofi. Aikin malamai ne da ke gabatar da bita su fahimtar
da maniyyata manufofin Hajji a Musulunci. Alqur'ani da Sunnah sun
bayyana manufofi guda uku na Hajji:
1. Gyaran zuciya ( ) da samun cikakkiyar tarbiyya da za ta zama
guzuri ga mutum a cikin dukan al'amura [Baqara, 197]. Dama duk
rukunan Musulunci irin wannan tazkiyya da tarbiyyar suke samar wa
wanda ya gudanar da su kamar yadda Shari'ah ta tabbatar [Baqara,
183; Taubah, 103; Ankabut, 45].
2. Ambaton Allah ( ) ta hanyar talbiyya da kabbarbari da addu'o'i
da sauran nau'o'in zikirin da ake yi a cikin ayyukan Hajji [Hajji, 37].
An ruwaito daga A'ishah ( ) cewa an shar'anta xawafi da
sa'ayi da tsayuwan Arfa da jifar jamrori ne domin a ambaci Allah.15
3. Shaida abubuwan amfani [ ] na duniya da lahira [Hajji,
28]. Imam Xabari ya ruwaito daga Mujahid cewa amfanin da ake
nufi ya haxa da kasuwanci da abubuwan da Allah Ya yarda da su
daga cikin albarkatun duniya da lahira.
Idan maniyyaci bai fahimci waxannan manufofi ba, zai iya tafka kura-
kurai. Idan kuma ya fahimta amma bai bi hanyoyin tabbatar da su ba, zai
rasa samun amfani da alherai masu tarin yawa, kamar yadda ba zai amfana
da tasirin da Hajji ke yi a cikin rayuwar Musulmi ba.
An ya kuwa, mutumin da ya fahimci waxannan manufofi zai qi tuba daga
zunubansa kafin ya bar Nijeriya, ko ya tozartar da haqqin iyalinsa don wai
zai je aikin Hajji, ko ya riqa kutsawa cikin mutane ba tare da la'akari da
waxanda ya ture ko ya taka ba, ko ya riqa yin gaggawar da ta wuce buqata
a cikin tafiya da gudanar da ayyukan Hajji, ko turereniya wajen shiga da
15
Daarimi (1780)
Shafi na 8 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
sauka daga mota, ko zaven xaki a masauki, ko rashin natsuwa wajen
dawowa daga Arfa, ko rashin la'akari da sauran mutane a wajen jifa da
xawafi?
Don haka, gudummuwar malamai ta farko ita ce fahimtar da maniyyata
manufar aikin Hajji da kuma xaukar matakan tarbiyyantar da su a kan
haka.
3.1.2 Karantar da Hukunce-hukuncen Aikin Hajji
Karantar da maniyyata na da matakai guda uku: matakin karantar da
matsayi da falala da hukunce-hukunce da ladubba da tarbiyya, tare da
bayani game da yadda ake gudanar da aikin Hajji; matakin nuna siffar
aikin Hajji a majigi ko na’urar bidiyo ko faifan CD; matakin koyar da aikin
Hajji a aikace ta hanyar amfani da alamomi (kamar ka’aba, wurin safa da
marwa, wurin jifar jamrori, da arfah) irin waxanda maniyyaci zai tarar a
can qasar Saudiya.16
3.1.3 Ba da Muhimmanci ga Janibin Tarbiyya
A vangaren tarbiyya, gudummuwar malamai ta qunshi koyar da
muhimmancin taqawa da haquri da tsantsar bin Sunnah wajen gudanar da
ayyukan Hajji da zaman lafiya da jurewa wahala da lazimtar abokai na
qwarai da kyautata wa abokan tafiya da tausaya wa waxanda ke cikin
matsala da xa’a ga shugabanni da jami’ai da biyayya ga dokokin qasar
Saudiya da kare martaba da mutuncin Nijeriya.
Nazari da bin diddigin salon gudanar da bitar aikin Hajji a Nijeriya sun
tabbatar da cewa an fi ba da qarfi ga janabin ilmantar da maniyyata
hukunce-hukunce maimakon cusa masu tarbiyya da xabi'u masu kyau da
16
Takardar da na gabatar a wajen taron qarawa juna ilmi a shekarar da ta gabata (2007) mai
taken 'Hanyoyin Horar da Maniyyata Aikin Hajji da Bunqasa Basirar Malamai masu Gabatar da Bita ga Maniyyata' ta tattauna a kan matakai guda uku na horar da maniyyata da karantar
da su vangarorin tarbiyya.Domin cinma wannan manufa, masu gabatar da bita na buqatar
amfani da sahihan littafai da ke magana a kan aikin Hajji da Umrah. Ban da littafan fiqihu da
Hadisi da ke qunshe da bayanai a kan aikin Hajji, malamai na iya amfani da littafin al-Qiraa li Qaasidi Ummil Quraa na Imam ax-Xabari; al-Idah fi Manaasikil Hajj na Imam an-Nawawi;
Awdhahul Masaalik ilaa Ahkaamil Manaasik na Abdul-Azeez al-Muhammad as-Salmaan;
Khaalisul Jumaan na Sa’ood bn Ibrahim Shuraim; al-Mughnee fi Fiqhil Hajj wal Umrah na
Sa’eed bn Abdul-Qadir; Sifatu Hajjatin Nabiyyi na Muhammad Naasiruddeen al-Albani; al-Manhaj li Muridil Umrah wal Hajj da Manaasikul Hajj na Muhammad bn Saalih al-
Uthaymeen; da Ramyul Jamaraat wa maa Yata’allaqu bihi min Ahkaam na Sharaf bn Aliyu
as-Shareef.
Shafi na 9 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
za su taimaka masu wajen gudanar da aikin Hajji cikin nasara. Wajibin
malamai shi ne bin usulubin magabata na qwarai ( ) wajen
karantarwa. Magabata sun kasance suna gabatar da janibin tarbiyya da
suluk a kan janibin koyar da ilmi.
Ban da wajibcin haquri, da taqawa, da lazimtar Sunnah, da yin xa'a da
biyyaya ga hukuma, da nisantar bidi'a da duk wani abin assha na zahiri, da
ya kamata a ilmantar da maniyyata, akwai buqatar malamai su tarbiyyantar
da maniyyata a kan waxannan vangarori guda uku:
Vangare na Farko: Matsalar Maimaita Aikin Hajji
Babu shakka, yin aikin Hajji fi ye da sau xaya abu ne mai kyau ga wanda
Allah Ya ba iko. Hasali ma, yawaita aikin Hajji da Umrah na kore talauci
kamar yadda Hadisi ingantacce ya nuna.
To sai dai kuma rashin maimaita aikin Hajji shi ya fi amfani da zama mafi
alheri ga Musulmi idan maimaitawar za ta haifar da xaya daga cikin
abubuwa guda uku:
1. Tozarta haqqin iyali da watsi da wajibinsu don kawai ana son
komawa aikin Hajji. Hakan zai kasance idan aka tafi ba tare da an
tanadar masu abin da zai wadace su ba har a dawo (wanda ya haxa
da abinci, kula da ilmi da lafiya, da muhalli), ko kuma idan ya
zamanto barinsu a gida zai jefa su cikin wani hali mai tsanani ko
mara kyau.
2. Cutarwa da quntatawa ga waxanda ba su tava zuwa ba. Hakan zai
kasance ne idan kujerun da hukuma ta tanada ba su kai yawan
mutanen da ke buqatar zuwa ba a wannan shekara, ko kuma zuwan
na shi zai haifar da qarin cunkoso mai cutarwa ga maniyyata ko
hukuma.
3. Yanke zumunta ta hanyar qin tallafa wa `yan'uwa da dangi a cikin
wani muhimmin abu da ya addabe su, kuma su ba su da halin
magance matsalar, amma shi zai iya taimakawa in ba domin ya yi
amfani da kuxin wajen biyan Hajji ba. Wannan ya sa Imam Ahmad
ibn Hanbal, da Abu Miskin, da Ibrahim an-Nakha'iy, da Ibn
Taimiyyah, da waxansu malamai masu yawa suke ganin fifiko da
Shafi na 10 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
rinjayen taimaka wa `yan'uwa mabuqata a kan maimaita aikin
Hajji.17
Sabo da irin waxannan matsaloli da aka gabatar a sama, musamman ma na
biyu, da kuma fatawoyin da manyan malamai suka ba da, ya sa qasar
Saudiya ta sanya dokar hana duk wani xan qasar Saudiya gudanar da aikin
Hajji fi ye da sau xaya a cikin kowace shekara biyar.18
Ko da yake ba lalle
ne mutanen Nijeriya su kalli matsala ta biyun ta wannan fuskar ba,
sanannen abu ne cewa matsala ta xaya da ta uku sun zama kamar ruwan
dare a Nijeriya.
Sai dai kuma wannan hukunci bai haxa da jami'an hukumar Alhazai ko
jami'an gwabnati da sauran mutanen da ake tafiya da su don taimaka wa
Alhazai wajen gudanar da aikin Hajji yadda ya kamata ba.19
Vangare na Biyu: Cutar da Alhazai wajen Gudanar da Ayyukan Hajji
Da yawa daga Alhazai na tafka varna yayin gudanar da ayyukan Hajji ta
hanyar cutar da sauran mutane, da nuna qarfi ko wauta ga jama'a, da
tattake masu rauni, da rashin tausayi da tsoron Allah, da cuxanya da
mata/maza ba tare da larura ba. Waxannan matsaloli sun fi aukuwa a wajen
xawafi da sa'ayi da jifar jamrori.
Ya kamata masu gudanar da bita su sanar da maniyyata waxannan
ingantattun bayanai:
1. Manzon Allah ( ) ya umurci Umar ibn Khattab (
) da ya yi xawafinsa daga gefe kuma ya bi a hankali wajen jifar
jamra don gudun ka da ya cutar da mutane, sabo da qarfinsa.20
2. Ibn Abbas ( ) ya hana yin turereniya a wajen xawafi,
kuma ya ce: "Idan ka tarar da mutane da yawa a wajen ruknul yamani, ka da ka tsaya don wai ka tava shi, ka ci gaba da tafiya."
21
17
Duba littafin Al-Furu' na Ibn Muflih, da Kitaabuz Zuhd na Imam Ahmad, da Al-Fataawal Kubraa na Ibn Taimiyyah don qarin bayani 18
Sanin ilmin da da da abin da ake kira za su taimaka
wa mutane fahimtar dalilan irin waxannan hukunce-hukunce. 19
Irin waxannan mutane sun haxa da malamai da jami'an kula da lafiya ko jami'an tsaro 20
Ahmad da Abdur-Razzaaq 21
Musnad As-Shaafi'i da Abdur-Razzaaq
Shafi na 11 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
3. A'ishah ( ) ta yi addu'ar rashin samun lada ga wani mutum
da ya shaida mata cewa ya tava rukn har sau biyu (2) ko uku (3) a
cikin xawafinsa. Ta ce: "Da ka ce 'Allahu Akbar' ka ci gaba da
tafiya (a cikin xawafinka) ya fi ka yi turereniya da matsatsa da
mutune wai don ka tava dutsen."22
4. Sa'ad ibn Abi Waqqas ( ) ya ce: "Idan ka samu sarari, je ka
tava. Idan kuwa ba ka samu ba, ka ce 'Allahu Akbar', ka ci gaba (da
xawafinka)23
5. Ibn Abbas ( ) ya kasance yana jin haushin wanda ke
turereniya (a wajen xawafi ko sa'ayi ko jifa) sabo da ko dai ya ji
rauni ne ko kuma ya ji wa waninsa.24
Lallai kam da maniyyatanmu za su fahimci waxannan bayanai kuma su yi
azamar aiki da su, za a samu ci gaba sosai, kuma za a daina yi wa `yan
Nijeriya kallon-biyu-ahu sabo da rashin tsari da xa'a a wajen aikin Hajji.
Vangare na Uku: Tsananta wa Kai
Waxansu Alhazanmu kan tsananta wa kansu wajen yin abubuwan da ba
dole ba ne. A wani lokacin, sukan takura kansu wajen aikata abin da babu
lada kwata-kwata. Tarbiyyantar da su a kan waxannan abubuwa tun
gabanin su bar Nijeriya zai tamaka in sha Allah wajen rage waxannan
matsaloli. Yana daga quntata da tsanantawar da Alhaji zai yi wa kansa ba
tare da dalili na Shar'iah ba:
1. Dagewa da nacewa a kan sai ya dafa multazim ko sai ya tava rukn ko ya sumbaci hajrul aswad, ko da kuwa irin wannan dagewar da
nacewar za su jawo a tattake shi ko ma a yi masa rauni. Wannan ya
sha faruwa! Duk da cewa aikata waxannan abubuwa na da falala,
maslaha da bayanan da suka gabata na hukunta cewa wani lokaci ya
fi kyau a haqura.
2. Shiga cikin hijr Isma'il da qoqarin yin addu'a a cikinsa. Ban da ma
turereniya da hakan kan jawo, babu dalili a kan falalar shiga wurin.
Hasali ma, hijr Isma'il vangare ne na Ka'aba.
22
Baihaqi 23
Baihaqi 24
Ibn Abi Shaybah
Shafi na 12 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
3. Zuwa wajen indararo (da mutane ke cewa wai nan ne saitin
Madina) domin yin addu'a, alhali hakan na jawo matsanancin
turereniya da matsatsa. Akwai wadda aka tava tattake ta har ta
suma a qoqarin yin addu'a a wurin! Maganar da Al-Qadhi Iyaad ya
yi a cikin littafin As-Shifaa cewa an so mutum ya je wurin
indararon don yin addu'a ba ta inganta ba.
4. Tsananta wa kai wajen maqama Ibrahim da zimmar yin salla a
wurin duk da irin matsatsi da turereniyar da ake samu wani lokaci.
Ko da yake an so a yi raka'a biyu a wurin, bayan an kammala
xawafi, idan hakan zai sa a tutture mutane ko a cutar da su, sai a yi
sallar a wani wurin.
5. Hawa kan jabalur-rahmah a filin Arfa ko hawa kan dutsen Uhud a
Madina. Hakan ya kan jawo haxari ga mutane da dama. Mun sha
jin labarin waxansu dun faxo daga kan dutsen, tare da cewa babu
wani dalili ko falala da ya/ta tabbata a kan hawa dutsen. Haka nan
ma, yin amfani da kuxin guzuri mai yawa wajen ziyarar buxe ido a
masaajidus sab'ah, masjidul qiblatain, rijiyar da aka ce wai zoben
Manzon Allah ( ) ya faxa ciki, da sauransu. Irin
wannan kashe kuxi mara dalili kan haifar wa Alhazai da dama
matsala, musamman idan an samu jinkiri wajen dawowa Nijeriya
bayan aikin Hajji.
3.1.4 Nema wa Maniyyata Sauqi a cikin Fatawa da Karantarwa
Malamai su ne magadan Annabawa, kuma yana daga manhajin Annabawa
bayar da ilmi yadda ya dace tare da tausasawa, da qanqan da kai, da yin
bayani ga mutane gwargwadon qwaqwalwarsu. Ilmi da karantar da shi
amana ce da Allah zai tambaye su a ranar qiyama. Wajibi ne su zamanto
masu faxin gaskiya ba tare da la’akari da jin daxi ko rashin jin daxin wani
ba. Kuma su tabbatar da cewa abubuwan da suke karantar da mutane ba
mujarradin ra’ayinsu ba ne. Lallai ne su tabbatar da cewa abin da suke
karantarwa ya tabbata a cikin Alqur’ani da Sunnah bisa fahimtar magabata
na qwarai.
Yana daga abin takaici, ka ga waxansu malamai na karantar da abubuwan
da ba su tabbata ba a cikin ingantacciyar Sunnah, ko ka ji suna zafafawa a
wurin da ya dace a sauqaqa, ko tsanani a muhallin sauqi. Babu shakka,
waxannan kura-kurai ne a haqqin mai karantarwa da bayar da fatawa.
Shafi na 13 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
A wajen aikin Hajji, malamai na da buqatar amfani da (qa'idodi) na
sassauci da sauqaqawa a cikin dukan al'amura, matuqar hakan bai sava wa
wani tabbataccen nassi ko wata sananniyar qa'ida ba. Hakan ya samu asali
a cikin Hadisin Jabir ibn Abdillah ( ) dangane da sauqin da
Manzon Allah ( ) ya yi wajen fatawa da karantarwa a
lokacin . Waxansu mutane sun yi tambaya game da gabatar da
waxansu ayyukan ranar goma ga wata (ranar jifar farko) maimakon jinkirta
su, amma Manzon Allah ( ) ya ce: 'Aikata wanda
ka jinkirta xin, kuma babu kome a kanka'.
Haka nan, akwai (abubuwan lura da la'akari) da (qa'idodi) da ake
buqatar malamai su yi amfani da su wajen ba da fatawa da karantarwa, ba
kawai a lokacin aikin Hajji ba, har ma da sauran lokuta. Waxannan
abubuwa sun haxa da:
1. La'akari da halin da ake ciki, da (bi'ar) da mutane suka taso a ciki, da
kuma savanin malamai in mas'ala ce da aka yi savani a kanta
2. Amfani da abin da ake cewa
3. La'akari da manufar Shari'ar Musulunci ( )
4. La'akari da matakin fahimtar waxanda ake karantarwa (
)
5. Bi sannu-sannu, kuma mataki-mataki ( ) a wajen karantarwa
6. Tabbatar da haxin kai da maslaha, ko da zai sa a bar wajibi (
)25
25
Irin wannan ya faru a zamanin halifancin Uthman ibn Affaan ( ) a lokacin da ya
cika sallar Zuhr da Asr a Mina, maimakon Qasru. Abdullah ibn Mas'ud ( ) ya yi masa
inkari a kan hakan, kasancewar Manzon Allah ( ) da Abubakar ( ) da
Umar ( ) qasaru suka yi, ba cikawa ba. Duk da haka, ya bi Uthman ( ) sallar.
Da aka tambaye shi dalili, sai ya ce: (savani sharri ne).
Shafi na 14 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Akwai buqatar malamai su yi amfani da waxannan qa'idodi a lokacin aikin
Hajji domin samar da sauqi ga Alhazai, matuqar hakan bai yi karo da
tabbataccen nassi ba. Daga cikin wuraren da ya kamata a xabbaqa wasu
daga cikin qa'idodin, akwai:
Na Xaya: Filin Arfa
Akwai malaman da ke ganin cewa barin filin Arfa kafin faxuwar rana laifi
ne babba. Waxansu ma sun kai ga cewa wanda ya bar filin Arfa kafin
faxuwar rana, ya yi laifin da dole ya yanka dabba (a matsayin fidya).
Tabbatacciyar magana dai ita ce, tsayawa a filin Arfa har faxuwar rana
mustahabbi ne ko Sunna. Idan mutum bai tsaya har wannan lokaci ba,
matuqar dai ya tsaya a filin Arfa a cikin wani yanki na yinin ko dare,
Arfarsa ta yi.26
Kenan dai kuskure ne malamai su bayyana cewa wanda duk
ya bar filin Arfa kafin faxuwar rana, ya yi laifi.
Sai dai kuma, idan hukuma ta nemi a tsaya har zuwa faxuwar rana, sabo da
wata maslaha, lallai ne kowa da kowa ya tsaya. Waxanda ba a yi wani tsari
na xaukarsu zuwa muzdalifa ba, suna da damar barin filin kafin rana ta
faxi, idan sun so.
Na Biyu: Xawaful Ifadha da Sa'ayi a tsakanin Safa da Marwa
Dangane da xawaful ifadha, akwai mas'aloli guda biyar da ke buqatar
kulawa ta musamman:
Ba dole ne mutum ya yi xawaful ifadha a ranar goma ga wata ko a
tsakanin kwanakin Mina ba. Mafi yawancin malamai na ganin halascin
jinkirta wannan xawafi har zuwa kafin qarshen watan Zul Hijjah,
musamman idan ana tsoron cinkoso ko akwai rashin lafiya, ko wata
larura dabam.
Mutumin da bai yi xawaful ifadha ba sabo da mantuwa, kuma bai tuna
ba sai bayan ya yi xawaful wada'i (xawafin ban kwana), Hajjinsa ya
inganta, kasancewar wannan xawafin ya xauke wa wancan, kamar
yadda Imam Nawawi ya tabbatar a cikin littafin sharhin Sahih
Muslim [8/193].
26
Dalili a kan haka, na qunshe cikin wani Hadisi sahihi da Abu Dawud (1950); Tirmizi (891);
Nasa'i (3041); da Ibn Majah (3016) suka ruwaito.
Shafi na 15 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Akwai savani dangane da yin xawafi ba tare da alwalla ba. Mafi
yawancin malamai sun sharxanta alwalla ga wanda zai yi xawafi.
Waxansu na ganin idan ma alwallar mutum ta karye alhali yana cikin
yin xawafi, zai yanke, ya sake alwalla, ya fara xawafin daga farko;
waxansu na ganin zai yi gini ne a kan adadin da ya yi kafin warwarewar
alwallar; waxansu kuma suka ce zai iya qarasawa ba tare da alwallar ba.
Amma, Imam Abu Hanifah na ganin halascin yin xawafi ba tare da
alwalla ba, tun daga farkonsa har qarshe. An ruwaito irin wannan
magana daga Imam Ahmad ibn Hanbal. Ibn Taimiyyah da Ibn Qayyim
da Al-Uthaymin sun qarfafi wannan fahimta, kuma sun rinjayar da ita a
kan ta jumhur. Kuma tabbas wannan fahimta ta fi inganci, musamman
idan aka yi la'akari da cewa babu wani dalili sahihi a kan wajibcin
alwalla kafin a yi xawafi.27
Bayan wannan, dagewa a kan wajibcin
alwalla a lokacin xawafi abu ne da ke zamantowa tsanani ga masu
larurori dabam-daban, kuma yana haifar da tsananin cunkoso a wajen
alwalla.
Duk da cewa wannan fahimtar ta fi kawo sauqi a cikin ayyukan Hajji,
lallai ne Alhazai su yi qoqarin yin alwalla kafin su fara xawafi, matuqar
babu wata larura babba da za ta hana su. Idan alwallarsu ta lalace kafin
su kammala xawafin, za su ci gaba, ba tare da jaddada alwalla ba.
Mai jinin al'ada (ko jinin haihuwa) za ta yi ayyukan Hajji gaba xaya, in
ban da xawafi, kamar yadda Hadisi ya tabbatar. A haqqinta, za ta
jinkirta xawafi har sai ta samu tsarki. To amma idan lokacin dawowarta
gida daga Makka ya yi kafin ta samu tsarki, kuma babu wani tanadi da
aka yi na dawowarta daga baya, tana da damar ta yi qunzugu (wato,
kamar ta sanya audugar mata), ta gabatar da xawafinta a hakan, kamar
yadda Ibn Taimiyyah da Ibn Qayyim suka haqqaqa. Sun bayyana cewa
yin hakan shi ne iyakar qoqarinta, tun da ya zama larura. Hakan ya dace
da abin da aka ruwaito daga Abu Hanifa da Ahmad ibn Hanbal. Kuma
qa'idar za ta yi aiki a nan.
Yana daga sauqaqawa a cikin ayyukan Hajji, fatawar da waxansu
malamai su ka ba da cewa idan akwai tsananin cinkoso a wajen xawafi,
za a iya gabatar da sa'ayi a tsakanin safa da marwa, sa'an nan, daga baya
a yi xawafin. Irin waxannan malamai na ganin cewa babu wani dalili
27
Babu hujjar wajibcin yin alwalla a cikin Hadisin da ya zo da hukuncin yin xawafi ga mai
jinin al'ada. Shi kuma Hadisin da ya zo da maganar wajibcin yin alwalla qarara, bai inganta
ba.
Shafi na 16 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
tabbatacce da ya sharxanta yin xawafi kafin sa'ayi. Sabo da haka, suke
xaukar gabatar da xawafi a kan sa'ayi a matsayin Sunnah, kasancewar
hakan ne Manzon Allah ( ) ya yi. Ke nan, idan akwai
larura, za a iya akkasawa, kamar yadda ya zo qarara a cikin Hadisin da
aka yi wa Manzon Allah ( ) tambaya dangane da gabatar
da sa'ayi a kan xawafi, kuma ya ce, 'je ka yi (xawafin), babu laifi'.28
Kasancewar ya halasta a jinkirta xawaful ifadha, da zarar mutum ya jefi
jamratul aqabah, ya yi aski, shi kenan, ya samu tahallulin farko (
), wato cire harami da samun damar yin amfani da duk abubuwan da
aka haramta masa a lokacin aikin Hajji, in ban da saduwa da mace.29
Ba
ya buqatar ya sake sanya haraminsa a lokacin da zai yi xawafin. Shaikh
Muhammad Nasiruddeen Al-Albani na ganin cewa za a mayar da
harami matuqar ba a yi xawaful ifadha a ranar goma ga wata ba, sabo
da wani Hadisi ingantacce. Amma Shaikh Muhammad Salih Al-
Uthaymin ya yi raddin wannan ra'ayi, kasancewar al'umma gaba
xayanta ta sava wa wannan Hadisi. Ya bayyana cewa mutum xaya ne
daga cikin tabi'ai ya tafi a kan ma'anar Hadisin. Don haka, ya kamata
malamai su yi amfani da wannan sauqi.
Na Uku: Jifar Jamratul Aqabah da Jamrori uku a ranakun Mina30
A qarqashin wannan gavar, akwai mas'aloli guda biyar: lokacin fara jifar
jamratul aqabah a ranar goma ga wata (kashegarin Arfa); lokacin jifa a
ranakun Mina; haxa jifar kwana biyu ko kwana uku a rana xaya; wakilci a
wajen jifa; da rashin kwana a Mina a ranakun jifa. 28
Shaikh Muhammad ibn Salih Al-Uthaymin ya yi magana mai kyau dangane da wannan
qa'ida ta (je ka yi babu laifi). Ya ce:
.
29
Waxansu malaman na ganin cewa Alhaji na samun tahallulin farko da zarar ya yi jefi
jamratul aqabah, ko da bai yi aski ko yanka ba. 30
Ranakun da ake gabatar da ayyukan Hajji na da sunayensu. Ranar takwas ga wata, wato
ranar da ake fita Mina, ana kiranta ; ranar tara ga wata ; ranar goma ga wata, wato
ranar jifar jamratul aqabah ; ranar sha xaya ga wata ; ranar sha biyu ;
ranar sha uku ga wata
Shafi na 17 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Wajibi ne Alhaji ya kwana a Muzdalifa, matuqar ba larura ce ta hana
hakan ba. Idan mutum bai kwana ba, zai ba da jini, ta hanyar yanka
dabbar fidyah. Idan kuwa bai samu isowa Muzdalifa ba sai bayan
fitowar alfijir, sabo da cunkoso ko gajiyar tafiya daga filin Arfa, ko wata
larura, wajibinsa shi ne ya tsaya a filin Muzdalifa na xan wani lokaci,
sa'an nan ya wuce zuwa wurin jifar jamratul aqabah. A irin wannan hali,
babu kome a kansa na fidyah. A taqaice dai, ba a jifar jamratul aqabah
sai bayan sallar alfijir. Yana daga Sunna a xan jinkirta jifar har sai
bayan fitowar rana, kamar yadda Manzon Allah ( ) ya yi.
Amma, waxanda ke da rauni, kamar mata da yara da tsofaffi da
marasa lafiya, ba su shiga cikin wannan hukunci ba. A haqqinsu, ya
halasta su bar Muzdalifa a qarshen dare, ta yadda za su isa wurin jifar
jamratul aqabah kafin fitowar alfijir, ko kuma da zarar ya fito. Manufar
ita ce su samu damar yin jifa kafin sauran mutane su iso. A magana mafi
qarfi, duk lokacin da suka isa wurin jamrar, za su gabatar da jifa, ko da
kuwa alfijir bai fito ba.
Asali dangane da lokacin yin jifa a ranakun Mina, shi ne daga bayan
zawal, wato wucewar rana daga tsakiyar sama zuwa faxuwar rana. A
wannan lokacin ne Manzon Allah ( ) da Sahabbansa (
) suka jefi jamrori. Ya tabbata a cikin Hadisi cewa Manzon Allah
( ) ya ba waxansu damar yin jifa cikin dare har zuwa
kafin fitowar alfijir.31
Hanafiyya da waxansu malaman malikiyya da
shafi'iyya duk sun bayar da fatawa da wannan. Haka nan ma,
ta tabbatar da wannan.
To sai dai kuma an ruwaito daga Ibn Abbas ( ) da Xawus, da
Muhammad Baqir, da Abu Hanifa, da Ibn Aqil, da Ibnul Jauzi32
, da Ar-
Rafi'í33
cewa za a iya yin jifa kafin zawal, tun daga lokacin walha. A
wannan zamanin kuma, an samu irin wannan fatawa daga Abdullah ibn
Mahmud, da Musxafa Zarqa, da Salih Al-Bulaihi. Haka nan, an ce
Abdur-Rahman As-Sa'adi ma yana ganin halascin haka.
31
Bukhari da Abu Dawud 32
Ibn Aqil da Ibnul Jauzi `yan hanbaliyya ne 33
Ar-Rafi'i xan shafi'iyya ne
Shafi na 18 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Bin diddigin abin da aka ruwaito daga Ibn Abbas ya tabbatar da cewa
isnadin mai rauni ne. Ban da wannan ma, abin da aka ruwaito daga Ibn
Umar ( ) na goyon baya ga maganar Ibn Abbas ( ) bai
inganta ba, ballantana ma Hadisin da Daru Qutni ya ruwaito cewa wai
Manzon Allah ( ) ya halasta yin jifa a kowane lokaci.
Dangane da ra'ayin Abu Hanifa kuwa, manyan xalibansa, Abu Ishaq da
Abul Hasan, sun bayar da fatawa savanin wannan, kuma mazhabar
hanafiyya ta yi watsi da ra'ayin Abu Hanifa a kan wannan. Al-Uthaymin
kuma ya yi wa sauran malaman raddi, ya bayyana cewa ka da Alhazai
su yi jifa sai bayan zawal.
Duk da cewa babu hujja mai qarfi dangane da gabatar da jifa kafin
zawal, idan maslaha ta hukunta yin jifar kafin zawal xin, zai shiga cikin
babin sauqaqawa. Wataqila la'akari da irin matsalolin da ake yawan
samu a ranakun jifa, sabo da yawan jama'a, yasa hukumar Saudiya ta
tsara wa kowace qasa lokacin da za ta yi jifa, ba tare da la'akari da
bayan zawal ne ko kafinsa ba. Qa'idar za ta yi amfani a
nan.
Yana daga sauqin da malamai za su yi, ba da fatawa a kan halascin haxa
jifar kwana biyu ga jami'an da ya zamanto dole su yi hakan ko masu
tsananin larura. Ko da yake qa'idar ita ce, a yi jifa a kowace rana, ya
tabbata cewar Manzon Allah ( ) ya yi rangwame ga
makiyaya da su haxa jifar kwana biyu a rana xaya.34
Wannan ne
fahimtar Imam Shafi'i da Ahmad ibn Hanbal.
Kenan, waxanda suka samu kansu a irin halin da waxancan makiyaya
suka kasance, kamar masu ayyukan kula da lafiya, ko marasa lafiya, ko
jami'an hukuma da ya zama dole su kasance a Makka ko Madina, za a
iya ba su fatawar yin haka. Shaikh Muhammad Salih Al-Uthaymin
yana ganin halascin yin jifar yini ukun gaba xaya a rana xaya, matuqar
da larurar haka.35
Ko da yake wajibi ne kwana a Mina a ranakun jifar jamrori, waxanda ke
da sahihiyar larurar da za ta hana su kwana a Mina, na da damar kwana
a Makka ko wani wuri dabam. In ya so, kowace rana, sai su tafi Mina
domin yin jifa. Dalili a kan haka na cikin Hadisin da Ibn Abbas (
34
Muwaxxa (815); Abu Dawud (1975); Tirmizi (955) 35
Duba littafin As-Sharhul Mumti' Ala Zaadil Mustaqni
Shafi na 19 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
) ya ruwaito cewa Manzon Allah ( ) ya ba Abbas
( ) damar ya kwana a Makka a ranakun Mina domin taimakawa
wajen shayar da Alhazai.36
Haka nan, Hadisi ya tabbata cewa Manzon
Allah ( ) ya ba makiyaya damar kwana a wajen Mina.37
3.2 GUDUMMUWAR JAMI'AN HUKUMAR ALHAZAI
Hukumar jin daxin Alhazai ce ke da alhakin tabbatar da cewa an gudanar
da aikin Hajji cikin sauqi, kuma yadda ya kamata. A matakin jiha da
tarayya, ana sa ran jami'an su kai su kawo wajen tabbatar da samun nasarar
ayyukan Hajji baki xaya.
Gudummuwar jami'an hukumar Alhazai na da yawan gaske, musamman da
yake rashin ba da ta su gudummuwar na iya durqusar da aikin Hajji ko ma
ya hana gudunarsa baki xaya. Yana daga vangarorin da ya kamata jami'an
su kula:
Fahimtar cewa wata dama ce Allah Ya ba su, ta su yi wa baqinSa,
Alhazai, xawainiya da hidima, don gudanar da aikin Hajji cikin
walwala. Abin da Allah Yake girmamawa, wajibi ne kowane musulmi
ya girmama, kuma ya ba shi muhimmanci. Tun da Alhazai baqin Allah
ne, kuma aikin Hajji ibada ce da Allah Yake matuqar so, lalle ne
ma'aikacin hukumar Alhazai ya ba wannan aiki muhimmanci.
Ya kamata su tuna cewa akwai mutane da yawan gaske da ke matuqar
buqatar zuwa aikin Hajji, amma ba su samu dama ba. Wasu daga
cikin jami'an hukumar Alhazai sun tafi aikin Hajji ya fi sau goma.
Gwabnati ke xaukar nauyin tafiyarsu da guzurinsu da sauransu.
Wannan ya nuna abubuwa guda biyu: wajibcin gode wa Allah a kan
ni'imar zuwa aikin Hajji shekara da shekaru, tun da lallai Allah zai
tambaye su a kan wannan ni'ima; da wajibcin gudanar da ayyukan da
hukumar Alhazai ta xora masu, ba tare da son rai ko kasala ba,
kasancewar ta hakan ne kawai za su tabbatar da cancantar kashe kuxin
da gwabnati ta yi a kansu. Ke nan, barci, ko yawon buxe idanuwa, ko
zaman hira, ko tafiyar ganin gari, bai dace da su ba, musamman a
Makka da Madina.
36
Bukhari da Muslim 37
Muwaxxa (815); Abu Dawud (1975); Tirmizi (955)
Shafi na 20 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
Wajibi ne su ji tsoron Allah wajen gudanar da ayyukan amana da aka ba
su, a madadin Alhazai. An daxe ana kuka da jami'an hukumar Alhazai
na mafi yawancin jihohi game da sama-da-faxi da suke yi da kuxin
hadaya.
Xabi'ar nuna wariya ko bambanci a tsakanin Alhazai ba ta dace ba. Lalle
ne jami'an hukumar Alhazai su guji yin haka.
Ya kamata jami'ai su taimaka wa hukumar Alhazai wajen bayar da
gamsasshen ilmi ga mahajjata tun daga nan gida Nijeriya har zuwa
qasar Saudiya a kan karantarwar Alqur’ani da Sunnar Manzon Allah
( ) bisa fahimtar magabata na qwarai. Wannan ne zai ba
kowane Alhaji ya samu damar yin akin Hajji cikin ilmi da basira.
Hakan kuwa ba zai yiwu ba, sai an samu malamai masu ilmi da tsoron
Allah, waxanda suka san yadda ake aikin Hajji.
Jami’an Alhazai su kasance masu matuqar haquri da Alhazai, domin
suna matsayin likitoci ne masu bayar da magani ga waxanda ba su da
lafiya. Su tuna cewa su ne shugabanni, kuma za su yi mu’amala ce da
mutane iri-iri, masu tarbiyya da halayya dabam-daban. Saurin fushi da
yawan faxa, ko qyale, bai dace da jami’ai ba. Kuma jami’ai su kasance
masu mutunta Alhazai, kamar yadda ake son Alhazai su yi masu xa’a.
Ka da jami’ai su nuna rashin goyon bayansu qarara ga wanda ya yi
qoqarin kiyayewa da kuma aiki da abin da ya fahimta, matuqar hakan
ba zai jawo savani na usulu ba, ko ya kawo barazana ga zaman lafiya da
kwanciyar hankali ko kuma kyakkyawan jagoranci. Misali, wanda ya
fahimci cewar ya fi dacewa a yi ihrami a cikin jirgi ko kafin ma a shiga
cikin jirgi, maimakon sai an je Jeddah (kasancewar Jeddah ba miqati ba
ne), a qyale shi, ba tare da tsangwama ko takurawa ba. Sauran Alhazai
da ke ganin sai a Jeddah za su yi harama, idan an je, sai su yi.
Ya kamata jami'ai su ba hukumar Alhazai shawarar samar da wadatattun
amsa kuwa (na’urar xaga sauti) a Mina, ta yadda za a xaura su a
qusurwoyin tantunan Alhazai na wannan jiha. Hakan zai taimaka wajen
samar da tsarin wa’azi na bai xaya da kuma isar da saqo ga dukan
mahajjata.
Ya kamata jami’an Alhazai na qananan hukumomi su tanadar wa
malamai masu wa’azi qananan lasifika na hannu domin samun sauqin
Shafi na 21 a cikin 19
Gudummuwar Jami'an Hukumar Alhazai da Malamai wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. – Ahmad Bello Dogarawa
isar da saqo a gidajen da suka sauka ko kuma wajen waxansu ayyukan
ibada a Makka ko Madina.
Ya kamata jami'an hukumar Alhazai su qarfafa gwiwar waxanda za su
buqaci yin kwana uku a Mina, ta hanyar tanadar masu dukan abubuwan
da suka dace.
4. GODIYA DA KAMMALAWA
Daga qarshe, ina son jawo hankalin mahalarta wannan taro da waxanda ma
ba su a nan, cewa aikin Hajji ibada ce babba da ke kawo alheri ga wanda
ya yi ta, ko kuma ya taimaka wajen samun nasarar gabatar da shi yadda ya
dace. Don haka, waxanda ba su samu zuwa aikin Hajji ba daga cikin
malamai masu bita, da waxanda za su riqa faxakar da maniyyata kafin su
bar Nijeriya, da jami'an hukumar jin daxin Alhazai, na bayar da
gudummuwa ce gagaruma wajen samun nasarar wannan aiki. Qoqarin da
suke yi da gudummuwar da suke bayarwa, ibada ce da za ta kawo masu
lada mai yawa matuqar sun yi don Allah kuma a kan karantarwar
Alqur’ani da Sunnah. Sabo da haka, su ci gaba da bayar da
gudummuwarsu ba tare da la’akari da cewa za a ba su kujerar Hajji ko ba
za a ba su ba.
Su kuma maniyyata, akwai buqatar su lazimci dalilai na karvar kyawawan
aiki don gudun ka da su kasa cin moriyar wannan gagarumin aiki da suke
fuskanta. Su kasance masu qanqan da kai da rashin taqama ko ruxuwa da
yawan aikin da za su yi ko kyawun aikin a idanunsu; su kasance masu
tsoron a dawo masu da ayyukansu ba tare da an karva ba, sabo da rashin
ikhlasi ko rashin dacewa da bin Sunnah; kuma su kasance masu tsananin
kwaxayin rahama da falalar Allah da yawaita istigfari da kyawawan
ayyuka.
Daga qarshe, ina godiya ga hukumar jin daxin Alhazai ta jihar Neja da ta
ba ni damar gabatar da wannan takarda a matsayin ta wa gudummuwar
wajen gudanar da aikin Hajji cikin sauqi. Ina roqon Allah Ya amsa mana.